ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Shirya Taro A Kan Alfanun Tattalin Arzikin Teku Ga Manyan ‘Yan Kasuwa A Ribas

by Sulaiman
3 years ago
Nis

Gwamnatin Jihar Ribas karkashin jagorancin Gwamna Siminalayi Fubara tare da hadin guiwar Hukumar Shige da Fice ta Nijeriya (NIS) sun karbi bakuncin manyan ‘yan kasuwa a kokarin gwamnatin na habbaka tattalin arziki ta bangaren saka hannun jari a bangaren alfanun albarkatun cikin ruwa.

Taron bitar na kwana daya wanda hukumar NIS da gwamnatin jihar Ribas suka shirya, ana sa ran zai samar da wata dama da za ta taimaka wa jihar Ribas da gwamnatin tarayya wajen binciko tarun albarkatun arziki da ke cikin teku.

  • Za Mu Inganta NTA Ta Fara Gogayya Da Takwarorinta Na Duniya – Ministan Yada Labarai 
  • Jami’ar Aliko Dangote Ta Karyata Jita-jitar Daukar Ma’aikata Da Ake Yadawa

Mukaddashiyar Kwanturola Janar ta Hukumar NIS, Caroline Wuraola Adepoju, wadda ta halarci taron bitar da aka yi a Kamfanin Gwamnan Jihar, wanda Sakataren Gwamnatin Jihar, Dakta Tammy Danagogo ya wakilta, ta yaba wa tsare-tsaren Gwamnatin tarayya na sake habbaka tattalin arziki wanda ya kai ga amincewa da kafa ma’aikatar tattalin arziki ta ruwa ta tarayya don fadadawa da kuma karkata tattalin arzikin Nijeriya daga man fetur da iskar gas zuwa albarkatun ruwa da tekun da ke kewayen Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Jihohin da ke zagaye da ruwa da ‘yan gabar teku sun hada da: Rivers, Bayelsa, Delta, Edo, Ondo, Lagos, Anambra, Cross Ribas, Akwa Ibom, Kebbi da Neja.

Daga cikin wadanda suka halarci taron akwai tsohon Kwanturola Janar na Hukumar NIS, Dakta David Shikfu Paraddang; Shugaban Elshcon Group, Dakta Emi Membere – Otaji; Mataimakin Shugaban Kungiyoyin Kasuwanci, Masana’antu, Ma’adinai da Aikin Noma, Majalisar Dillalan Jiragen Ruwa wanda Mista Glory Onojedo ya wakilta; Shugaban hukumar kula da tashar jiragen ruwa ta Nijeriya (NPA), Mista Michael Adamu; Kodinetan shiyyar NIMASA ta Kudu-maso-Kudu, Mista Yusuf Barde; Shugaban kamfanin Sigma Nigeria Limited, Dakta Soky Amachree da shugabannin masana’antu masu zaman kansu.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Sabon Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Mahalarta taron sun yabawa Kwanturolan hukumar NIS mai kula da reshen Jihar Ribas da tawagarsa bisa shirya wannan taron karawa juna sani a lokacin da ake bukatar taron domin samun kyakkyawar fahimta akan sabuwar ma’aikatar ta yadda masu zuba jari za su nutsu da ma’aikatar da kuma tsare-tsarenta.

NIS
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Sabon Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano
  • Sulaiman
    Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu
  • Sulaiman
    Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz
  • Sulaiman
    Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

MASU ALAKA

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Sabon Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Sabon Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
Tsaro

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
Next Post
Ronaldo

Ronaldo Ya Jefa Kwallo Biyu Yayin Da Portugal Ta Lallasa Bosnia Da Ci 5-0

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Sabon Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Sabon Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

June 25, 2026
Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

June 25, 2026
Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

June 25, 2026
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

June 25, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.