ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Shirya Taro A Kan Alfanun Tattalin Arzikin Teku Ga Manyan ‘Yan Kasuwa A Ribas

by Sulaiman
3 years ago
Nis

Gwamnatin Jihar Ribas karkashin jagorancin Gwamna Siminalayi Fubara tare da hadin guiwar Hukumar Shige da Fice ta Nijeriya (NIS) sun karbi bakuncin manyan ‘yan kasuwa a kokarin gwamnatin na habbaka tattalin arziki ta bangaren saka hannun jari a bangaren alfanun albarkatun cikin ruwa.

Taron bitar na kwana daya wanda hukumar NIS da gwamnatin jihar Ribas suka shirya, ana sa ran zai samar da wata dama da za ta taimaka wa jihar Ribas da gwamnatin tarayya wajen binciko tarun albarkatun arziki da ke cikin teku.

  • Za Mu Inganta NTA Ta Fara Gogayya Da Takwarorinta Na Duniya – Ministan Yada Labarai 
  • Jami’ar Aliko Dangote Ta Karyata Jita-jitar Daukar Ma’aikata Da Ake Yadawa

Mukaddashiyar Kwanturola Janar ta Hukumar NIS, Caroline Wuraola Adepoju, wadda ta halarci taron bitar da aka yi a Kamfanin Gwamnan Jihar, wanda Sakataren Gwamnatin Jihar, Dakta Tammy Danagogo ya wakilta, ta yaba wa tsare-tsaren Gwamnatin tarayya na sake habbaka tattalin arziki wanda ya kai ga amincewa da kafa ma’aikatar tattalin arziki ta ruwa ta tarayya don fadadawa da kuma karkata tattalin arzikin Nijeriya daga man fetur da iskar gas zuwa albarkatun ruwa da tekun da ke kewayen Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Jihohin da ke zagaye da ruwa da ‘yan gabar teku sun hada da: Rivers, Bayelsa, Delta, Edo, Ondo, Lagos, Anambra, Cross Ribas, Akwa Ibom, Kebbi da Neja.

Daga cikin wadanda suka halarci taron akwai tsohon Kwanturola Janar na Hukumar NIS, Dakta David Shikfu Paraddang; Shugaban Elshcon Group, Dakta Emi Membere – Otaji; Mataimakin Shugaban Kungiyoyin Kasuwanci, Masana’antu, Ma’adinai da Aikin Noma, Majalisar Dillalan Jiragen Ruwa wanda Mista Glory Onojedo ya wakilta; Shugaban hukumar kula da tashar jiragen ruwa ta Nijeriya (NPA), Mista Michael Adamu; Kodinetan shiyyar NIMASA ta Kudu-maso-Kudu, Mista Yusuf Barde; Shugaban kamfanin Sigma Nigeria Limited, Dakta Soky Amachree da shugabannin masana’antu masu zaman kansu.

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Mahalarta taron sun yabawa Kwanturolan hukumar NIS mai kula da reshen Jihar Ribas da tawagarsa bisa shirya wannan taron karawa juna sani a lokacin da ake bukatar taron domin samun kyakkyawar fahimta akan sabuwar ma’aikatar ta yadda masu zuba jari za su nutsu da ma’aikatar da kuma tsare-tsarenta.

NIS
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
Ronaldo

Ronaldo Ya Jefa Kwallo Biyu Yayin Da Portugal Ta Lallasa Bosnia Da Ci 5-0

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.