ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Shirya Taro A Kan Alfanun Tattalin Arzikin Teku Ga Manyan ‘Yan Kasuwa A Ribas

by Sulaiman
3 years ago
Nis

Gwamnatin Jihar Ribas karkashin jagorancin Gwamna Siminalayi Fubara tare da hadin guiwar Hukumar Shige da Fice ta Nijeriya (NIS) sun karbi bakuncin manyan ‘yan kasuwa a kokarin gwamnatin na habbaka tattalin arziki ta bangaren saka hannun jari a bangaren alfanun albarkatun cikin ruwa.

Taron bitar na kwana daya wanda hukumar NIS da gwamnatin jihar Ribas suka shirya, ana sa ran zai samar da wata dama da za ta taimaka wa jihar Ribas da gwamnatin tarayya wajen binciko tarun albarkatun arziki da ke cikin teku.

  • Za Mu Inganta NTA Ta Fara Gogayya Da Takwarorinta Na Duniya – Ministan Yada Labarai 
  • Jami’ar Aliko Dangote Ta Karyata Jita-jitar Daukar Ma’aikata Da Ake Yadawa

Mukaddashiyar Kwanturola Janar ta Hukumar NIS, Caroline Wuraola Adepoju, wadda ta halarci taron bitar da aka yi a Kamfanin Gwamnan Jihar, wanda Sakataren Gwamnatin Jihar, Dakta Tammy Danagogo ya wakilta, ta yaba wa tsare-tsaren Gwamnatin tarayya na sake habbaka tattalin arziki wanda ya kai ga amincewa da kafa ma’aikatar tattalin arziki ta ruwa ta tarayya don fadadawa da kuma karkata tattalin arzikin Nijeriya daga man fetur da iskar gas zuwa albarkatun ruwa da tekun da ke kewayen Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Jihohin da ke zagaye da ruwa da ‘yan gabar teku sun hada da: Rivers, Bayelsa, Delta, Edo, Ondo, Lagos, Anambra, Cross Ribas, Akwa Ibom, Kebbi da Neja.

Daga cikin wadanda suka halarci taron akwai tsohon Kwanturola Janar na Hukumar NIS, Dakta David Shikfu Paraddang; Shugaban Elshcon Group, Dakta Emi Membere – Otaji; Mataimakin Shugaban Kungiyoyin Kasuwanci, Masana’antu, Ma’adinai da Aikin Noma, Majalisar Dillalan Jiragen Ruwa wanda Mista Glory Onojedo ya wakilta; Shugaban hukumar kula da tashar jiragen ruwa ta Nijeriya (NPA), Mista Michael Adamu; Kodinetan shiyyar NIMASA ta Kudu-maso-Kudu, Mista Yusuf Barde; Shugaban kamfanin Sigma Nigeria Limited, Dakta Soky Amachree da shugabannin masana’antu masu zaman kansu.

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Mahalarta taron sun yabawa Kwanturolan hukumar NIS mai kula da reshen Jihar Ribas da tawagarsa bisa shirya wannan taron karawa juna sani a lokacin da ake bukatar taron domin samun kyakkyawar fahimta akan sabuwar ma’aikatar ta yadda masu zuba jari za su nutsu da ma’aikatar da kuma tsare-tsarenta.

NIS
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Ronaldo

Ronaldo Ya Jefa Kwallo Biyu Yayin Da Portugal Ta Lallasa Bosnia Da Ci 5-0

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.