• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kashi 25% Na Makarantun Firamare A Kano Na Da Malami 1 Ga Duk Aji – LANE

by Abubakar Sulaiman
11 months ago
Makarantun

Shirin tallafin ilimi na PLANE, wanda ofishin FCDO na Burtaniya ke ɗaukar nauyi, ya bayyana cewa kusan kashi 25% na makarantun firamare a Kano na da malami ɗaya ne kawai wanda ke koyarwa a duk aji.

Wannan bayanin ya fito ne yayin wani taron gabatar da sakamakon bincike kan ingancin karatu da aka gudanar a ƙananan hukumomin da PLANE ke aiki a jihar.

  • Gwamnatin Kano Za Ta Fassara Litattafan Kimiyya Da Hausa – Mataimakin Gwamnan Kano
  • Gwamnatin Kano Ta Miƙa Yara 76 Da Aka Kama Yayin Zanga-zangar Tsadar Rayuwa

Binciken ya nuna cewa kowane malami yana koyar da yara kusan 131, wanda ya ninka sau hudu bisa ga ƙa’idar UNESCO ta 35:1. Haka kuma, an gano cewa kaso 79% na yara a ajin Kano ba su da kayan aiki kamar fensir da littattafan rubutu. Duk da haka, an samu ci gaba a ɓangaren karatun harshen Turanci da lissafi a makarantun da ake tallafawa.

Me bayar da shawarar a ɓarin FCDO, Joseph Wales, ya yaba da nasarorin da aka samu, yana mai cewa za a yi amfani da irin wannan tsarin don ƙarfafa haɗin kai a matakin al’umma, da ƙananan hukumomi, da Jiha don inganta ilimi.

Wakilin PLANE, Sam Achimugu, ya bayyana cewa suna aiki tare da gwamnati don tabbatar da cewa yara sun fi ƙwarewa a karatun harshe da lissafi a duk jihar.

LABARAI MASU NASABA

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Sakatariyar hukumar SUBEB, Amina Umar, ta tabbatar da cewa gwamnatin jihar ta fara ɗaukar matakan gyara, ciki har da tabbatar da rarraba malamai daga yankunan birni zuwa karkara don magance rashin malamai. Ta kuma yi kira ga shugabannin LGA da su naɗa shugabannin ilimi masu kwarewa domin magance matsalolin rashin halartar malamai da ɗalibai.

Taron ya haɗa wakilai daga ma’aikatar Ilimi, da SUBEB, da FCDO, da sauran masu ruwa da tsaki don tsara dabarun ci gaba.

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

gombe
Ilimi

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma
Ilimi

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
ASUU
Ilimi

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025
Next Post
Makarantu Masu Zaman Kansu Sun Koka Kan Kudaden Tafiyar Da Ayyukansu

Makarantu Masu Zaman Kansu Sun Koka Kan Kudaden Tafiyar Da Ayyukansu

LABARAI MASU NASABA

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

October 28, 2025
Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

October 28, 2025
An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

October 28, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi

October 28, 2025
Fasahohin Sin Za Su Iya Kyautata Makomar Nahiyar Afrika

Fasahohin Sin Za Su Iya Kyautata Makomar Nahiyar Afrika

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.