ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Makarantu Masu Zaman Kansu Sun Koka Kan Kudaden Tafiyar Da Ayyukansu

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
Makarantu

Masu ruwa da tsaki ta bangaren ilimi sun yi kira da a dauki tsari na gaggawa saboda  arage yawan kudaden da ake kashewa wajen tafiyar da makarantu masu zaman kansiu.

Yomi Otubela ita ce shugaban kungiyar makarantu masu zaman kansu ta kasa ya yi jawabi ne kan irin tabarbarewar tattalin arziki wanda dalilin hakan makarantu masu zaman kansu suna ji a jikinsu.

  • Kamfanin Hakar Uranium Na Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Na’urori Ga Wata Makaranta A Namibia
  • An Kama Dillalin Safarar Makamai Dan Aljeria A Zamfara 

A hirar da tayi da kamfanin dillancin labarai na Nijeriya ranar lahadi, ya ce akwai bukatar da dauki tsare- tsare ba tare da bata lokaci ba, wadanda za s taimaka wajen saukaka kudin kayan karatu.

ADVERTISEMENT

Otubela ya kara da cewar su tsare- tsaren ya dace su samar da wasu hanyoyi da za’a bar daukar haraji akan kudaden bashin da ake ba mabobin kungiyar.

Shugaban na kungiyar NAPPS yayi kira da hadin kai domin samun dama ta lamarin daya shafi fasaha.

LABARAI MASU NASABA

Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

Ya ci gaba da bayanin“Mun san cewa idan har aka samu tallafi daga gwamnatoci wadanda za’a ba makarantu masu zaman kansu,hakan zai sa su makarantu masu zaman kansu su rage fiye da yara milyan 18 wadanda basu zuwa makaranta a Nijeriya.”

Otubela ya kara jaddada cewa makarant da yawa karkashin kungiyar sun bullo da tsari na biyan kudin makaranta,inda take aiki tare da Iyayen yara, domin a tabbatar da cewa babu wani yaron da aka bari saboda Iyayen shin a fuskantar matsalolin da suka shafi kudi.

Kamar yadda yayi karin haske  kungiyar NAPPS tana yin iyakar kokarinta wajen samar da ilimi mai nagarta, da kuma sanin irin halin rayuwar da al’umma suke ciki, wajen bin lamarin hanyar data kamata.

“Muna fatan gwamnati zata kara kudaden taimakon da take badawa kan tsarie- tsaren horar da Malaman makaranta, da kuma sauran wasu nau’oin taimakon da ake badawa na kudade ga makarantu domin su inganta abubuwan more rayuwa a makarantu kamar yadda Otubela ya bayyana”.

“Hadin gwiwar ba wai abin zai tsaya bane kan taimakon matsalolin da makarantu masu zaman kansu ke fuskanta ba ne, har ma da tabbatar da kowane dalibin Nijeriya ba tare da la’akari yadda mahaifansa suke ba,ya samu ilimi mai nagarta.”

Segun Olayode wanda yana daya daga cikin Iyaye wanda shi masani ne kan kimiyyar data shafi lamarin kula da lafiya, cewa yayi ya kara kaimi ne domin ya biya karin kudin makarantar da aka yi na ‘ya’yan shi.

Wata mahaifiya ma wato, Tolani Odofin, wadda ita ma’aikaciyar gwamnati ce, tace ba zata iya biyan karin kudin makarantar ba, sai dai za ta mai da ‘ya;yanta wata makaranta.

Ta ce “Hukumar makarantar ta rubuta masu takarda lokacin huru inda aka bayyana masu  lamarin tabarbarewar tattalin arziki ne yasa aka yik arun kudin makarantar”.

Ta ce “Ni da mijina mun yanke shawarar sa su a wata  makaranta saboda ba za mu iya biyan sabon kudin makaranatar.Daga Naira 65,500  zuwa Naira 95,500, bayan haka kuma ga kudin littattafai da sauran kayan karatu sun karu”.

Makarantu
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Ilimi

Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka

July 11, 2026
ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus
Ilimi

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

July 3, 2026
Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
Ilimi

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

June 20, 2026
Next Post
Nazarin Dabarun Koyarwa Da Amfaninsu (15)

Nazarin Dabarun Koyarwa Da Amfaninsu (15)

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.