• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kashi 67 Cikin 100 Na Ɗaliban Kaduna Sun Samu Nasara A WAEC – Kwamishinan Ilimi

by Sulaiman
10 months ago
in Labarai
0
Kashi 67 Cikin 100 Na Ɗaliban Kaduna Sun Samu Nasara A WAEC – Kwamishinan Ilimi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin jihar Kaduna ta sanar da samun gagarumar nasara a fannin ilimi, inda sama da kashi 67 cikin 100 na dalibanta suka samu sakamako mai daraja ta biyar (C5) zuwa sama a jarrabawar kammala sakandare ta yammacin Afirka (WASSCE).

 

Kwamishinan Ilimi na Jihar, Farfesa Muhammad Sani Bello ne ya bayyana haka a taron kwana daya da hukumar tabbatar da ingancin makarantu ta jihar (KSSQA) ta shirya mai taken “Quality Assurance in Education: Summit for Best Practices”.

  • Gidauniyar Buratai Ta Taya Giwa-Daramola Murnar Zama Shugaban Kungiyar Tseren Kwale-kwale Na Ondo
  • Karin Farashin Man Fetur: Ko Tinubu Zai Saurari Muryar Talaka?

Da yake zantawa da manema labarai, Farfesa Bello ya ce, wannan gagarumar nasara da aka samu, ta nuna irin hoɓɓasa da gwamnatin Gwamna Uba Sani ke yi a ɓangaren ilimi, da nufin daukaka darajar ilimi a jihar.

 

Labarai Masu Nasaba

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Farfesa Bello ya yi nuni da cewa, “Kaduna ta himmatu wajen ganin cewa, ba wai kawai samun ilimi ba, har ma da tabbatar da dalibai sun kammala karatunsu da sakamako mai kyau. Mun riga mun ga gagarumar nasara, kuma muna fata wannan nasarar za ta ci gaba”

 

Ya bayyana kwarin gwiwar cewa, tsarin ilimin jihar nan ba da jimawa ba zai zama na daya a Nijeriya wajen bayar da ilimi. Kwamishinan ya bukaci sauran hukumomi da su yi koyi da hukumar tabbatar da ingancin ilimi wajen aiwatar da dabarun kula da ingancin ilimi.

 

Da yake amsa tambayoyin manema labarai, Farfesa Usman Abubakar Zaria, babban darakta a hukumar KSSQA, ya bayyana matakai daban-daban da aka dauka na karfafa matakan ilimi a makarantun gwamnati da masu zaman kansu. Ya jaddada cewa, dole ne makarantu masu zaman kansu su bi ka’idojin tabbatar da ingancin ilimi a jihar.

 

“Daya daga cikin manyan nasarorin da muka samu a karkashin Gwamna Uba Sani shi ne, daukakar darajarmu a wurin samun sakamakon jarabawar kammala sakandire ta WAEC daga kashi 54 zuwa kashi 67 cikin 100, kuma darajarmu ta tashi daga na 10 zuwa na 7 a fadin kasar nan. Mun kuma bullo da ingantattun tsarin tantance jabun sakamako ta hanyar amfani da na’urar (QR code) da kuma fitar da sabbin fasahohi, kamar na’urorin kwamfuta, don inganta koyo,” in ji Farfesa Zaria.

 

Da yake jawabi a kan matsalar rashin tsaro da ta addabi wasu sassan jihar, Farfesa Zaria, ya ce, duk da cewa a baya rashin tsaro ya yi tasiri wajen hana yara shiga makarantu, amma a baya-bayan nan an samu ci gaba a fannin tsaro a fadin jihar, wanda a halin yanzu kananan yara da suka shiga makarantun firamare sun kai kusan miliyan 1.8, wanda a shekarar baya aka samu kimanin yara miliyan 1.7


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gidauniyar Buratai Ta Taya Giwa-Daramola Murnar Zama Shugaban Kungiyar Tseren Kwale-kwale Na Ondo

Next Post

Xi Zai Halarci Taron Kolin BRICS Karo Na 16 A Rasha

Related

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya
Labarai

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

8 hours ago
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi
Labarai

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

9 hours ago
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa
Labarai

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

9 hours ago
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba
Labarai

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

10 hours ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

12 hours ago
Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 
Labarai

Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 

13 hours ago
Next Post
Xi Zai Halarci Taron Kolin BRICS Karo Na 16 A Rasha

Xi Zai Halarci Taron Kolin BRICS Karo Na 16 A Rasha

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.