ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kashi 67 Cikin 100 Na Ɗaliban Kaduna Sun Samu Nasara A WAEC – Kwamishinan Ilimi

by Sulaiman
2 years ago
Kwamishinan Ilimi

Gwamnatin jihar Kaduna ta sanar da samun gagarumar nasara a fannin ilimi, inda sama da kashi 67 cikin 100 na dalibanta suka samu sakamako mai daraja ta biyar (C5) zuwa sama a jarrabawar kammala sakandare ta yammacin Afirka (WASSCE).

 

Kwamishinan Ilimi na Jihar, Farfesa Muhammad Sani Bello ne ya bayyana haka a taron kwana daya da hukumar tabbatar da ingancin makarantu ta jihar (KSSQA) ta shirya mai taken “Quality Assurance in Education: Summit for Best Practices”.

ADVERTISEMENT
  • Gidauniyar Buratai Ta Taya Giwa-Daramola Murnar Zama Shugaban Kungiyar Tseren Kwale-kwale Na Ondo
  • Karin Farashin Man Fetur: Ko Tinubu Zai Saurari Muryar Talaka?

Da yake zantawa da manema labarai, Farfesa Bello ya ce, wannan gagarumar nasara da aka samu, ta nuna irin hoɓɓasa da gwamnatin Gwamna Uba Sani ke yi a ɓangaren ilimi, da nufin daukaka darajar ilimi a jihar.

 

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

Farfesa Bello ya yi nuni da cewa, “Kaduna ta himmatu wajen ganin cewa, ba wai kawai samun ilimi ba, har ma da tabbatar da dalibai sun kammala karatunsu da sakamako mai kyau. Mun riga mun ga gagarumar nasara, kuma muna fata wannan nasarar za ta ci gaba”

 

Ya bayyana kwarin gwiwar cewa, tsarin ilimin jihar nan ba da jimawa ba zai zama na daya a Nijeriya wajen bayar da ilimi. Kwamishinan ya bukaci sauran hukumomi da su yi koyi da hukumar tabbatar da ingancin ilimi wajen aiwatar da dabarun kula da ingancin ilimi.

 

Da yake amsa tambayoyin manema labarai, Farfesa Usman Abubakar Zaria, babban darakta a hukumar KSSQA, ya bayyana matakai daban-daban da aka dauka na karfafa matakan ilimi a makarantun gwamnati da masu zaman kansu. Ya jaddada cewa, dole ne makarantu masu zaman kansu su bi ka’idojin tabbatar da ingancin ilimi a jihar.

 

“Daya daga cikin manyan nasarorin da muka samu a karkashin Gwamna Uba Sani shi ne, daukakar darajarmu a wurin samun sakamakon jarabawar kammala sakandire ta WAEC daga kashi 54 zuwa kashi 67 cikin 100, kuma darajarmu ta tashi daga na 10 zuwa na 7 a fadin kasar nan. Mun kuma bullo da ingantattun tsarin tantance jabun sakamako ta hanyar amfani da na’urar (QR code) da kuma fitar da sabbin fasahohi, kamar na’urorin kwamfuta, don inganta koyo,” in ji Farfesa Zaria.

 

Da yake jawabi a kan matsalar rashin tsaro da ta addabi wasu sassan jihar, Farfesa Zaria, ya ce, duk da cewa a baya rashin tsaro ya yi tasiri wajen hana yara shiga makarantu, amma a baya-bayan nan an samu ci gaba a fannin tsaro a fadin jihar, wanda a halin yanzu kananan yara da suka shiga makarantun firamare sun kai kusan miliyan 1.8, wanda a shekarar baya aka samu kimanin yara miliyan 1.7

Kwamishinan Ilimi
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje
  • Sulaiman
    Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa
  • Sulaiman
    Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci
  • Sulaiman
    Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Xi Zai Halarci Taron Kolin BRICS Karo Na 16 A Rasha

Xi Zai Halarci Taron Kolin BRICS Karo Na 16 A Rasha

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.