Rundunar Sojin Saman Nijeriya (NAF) ta gargaɗi ‘yan bindiga da suka addabi Zamfara, Katsina da sauran jihohin Arewa maso Yamma da su fice daga maɓoyarsu ko su fuskanci mummunan luguden wuta ta sama.
Shugaban Rundunar Sojin Sama, Air Marshal Hasan Abubakar ne, ya bayyana hakan ne a ranar Laraba yayin gudanar da motsa jiki a Abuja.
- An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja
- Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa
Ya ce za su ci gaba da kai farmaki kan ‘yan ta’adda a Borno da sauran yankunan Arewa maso Gabas.
Ya ce dakarun sama ba za su zuba ido ba yayin da masu aikata laifi ke kawo ruɗani a cikin ƙasa.
“Ga maƙiyan Nijeriya, ku sani: ba za ku samu wajen ɓuya ba. Za mu same ku kuma mu kawar da ku,” in ji shi.
Abubakar ya tabbatar da cewa rundunar na da cikakken niyyar kare sararin samaniyar Nijeriya da rayuka da dukiyoyi a faɗin ƙasar nan.
Ya kuma gode wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu saboda irin goyon bayan da yake bai wa sojoji, musamman ta fannin kayan aiki da walwalar ma’aikata.
A makon da ya gabata, rundunar ta kashe aƙalla ‘yan ta’adda 20 a wani samame da aka kai Garin Mani, da ke ƙaramar hukumar Maru a Jihar Zamfara.
Wannan farmaki ya biyo bayan luguden wuta da aka riƙa yi wa ‘yan bindiga da ke cin karensu ba babbaka.
Shugaban sojin ya ce motsa jiki abu ne da ya zama dole ga dukkanin ma’aikata, kuma babu wanda zai samu ƙarin girma ba tare da cikakken lafiyar jiki da ƙwaƙwalwa ba.
Don haka, ya amince a gina sababbin wuraren motsa jiki a sansanonin rundunar Sojin Sama da kuma siyan sabbin kayan motsa jiki don raba wa sassan rundunar sama da 22.
Ya bayyana cewa aikin motsa jikin ba wai motsa jiki kawai ba ne, amma yana nuna karfi da daidaito da kuma ƙudirin rundunar wajen kare Nijeriya.
Ya buƙaci dakarun su kasance masu jajircewa da haƙuri domin cimma zaman lafiya.
Wannan aikin motsa jiki ana yin sa ne sau uku a shekara a dukkanin sassan rundunar Sojin Sama domin ƙarfafa jiki, haɗin kai da kuma nuna wa jama’a da maƙiya cewa rundunar Sojin Sama ta kasance cikin shiri, kuma za ta ci gaba da kare Nijeriya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp