• English
  • Business News
Saturday, October 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Katsalandan A Harkokin Ma’adanai: Gwamnatin Tarayya Ta Gargadi Jihohi

by Bello Hamza
2 years ago
Ma'adanai

Ministan Harkokin Ma’adanai, Dakta Oladele Alake ya bayyana cewa, gwamnatocin jihohi basu da hurumi a dokokin Nijeriya na sanya hannu a kan yadda ake tafiyar da harkokin hakar ma’adanai a kasar nan, ya kuma ce, haramun ne yadda jihohi suke bayar da umanin dakatar da hakar ma’adanai a jihohinsu domin dokokin Nijeriya bai basu damar na yin haka ba.

Ministan ya bayyana matsayar gwamnatin tarayyar ne a taron manema labarai a Abuja a bikin ranar harkokin hakar ma’adanai na shekarar 2023.

  • Zaman Lafiya: MDD Ta Fara Yunkurin Samar Da Wani Sabon Tsari A Kaduna Da Katsina
  • Tinubu Ya Naɗa Sababbin Shugabannin Hukumomin Yaɗa Labarai

Ya ce, “Yadda jihohi ke haramta harkokin hakar ma’adanai a sassan Nijeriya abin takaici ne. Ina amfani da wannan damar na sanar da al’ummar Nijeriya cewa, babu wata jiha da take da hurumin katsalandan a harkokokin hakar ma’adanai, wanna abin da ya shafi tsarin mulkin Nijeriya ne kai tsaye.

“Hakar ma’adai abu ne da yake a matsayin hurumi na gwamnatin tarayya, kamar yadcda tsarin mulki ya zayyana. Hakki ne na gwamnatin tarayya babu tamtama a kai.

Duk wani ma’adani da Allah ya shimfida a cikin kasa mallakin gwamnatin tarayya ne, a saboda haka gwamnatin tarayya ce kadai ke da ikon tasarufin su baki daya, kamar hakar ma’adanai da lamarin albarkatun man fetur duk a karkashin gwamnatin tarayya suke. Gwamnatin taraya ce keda ikon yin dokokin da za su tafiyar da yadda za a gudanar da su a mastayin albarkar kasa mallakin al’ummar Nijeriya gaba daya.”

LABARAI MASU NASABA

Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

Ministan ya kuma ce, in har gwamnatocin jihohi na son shiga harka hakar ma’adanai sai su bi tsarin da ya dace ta hanyar karbar lasisin yin haka kamar yadda doka ta tanada.
Ya ce, gwamnatin taraya ba tana shirin fada da gwamnatocin jihohi ba ne amma za ta ci gaba da ilimantar da su a kan lamarin don a samu ci gaban da ake bukata, ya kuma ce, ya samu haduwa da shugaban kungiyar gwamnonin Nijeriya inda suka samu fahimtar jun a a kan lamarin.

Bincike a halin yanzu ya nuna cewa, jihohin n da suka haramta hakar ma’adanai a yankin su sun hada da Kebbi, Zamfara, Taraba, da Osun.

Gwamnatin Jihar Kebbi ta bayyana dalilan da ya sa suka haramta hakar ma’adanai a sassan jihar. Sakataren gwamnan jihar, Ahmed Idris, ya bayyana wa manema labarai cewa, sun haramta hakar ma’adanai a jihar ne don su daidaita yadda ake tafiyar da hakar ma’adanan a jihar.

Ya ce, “Mun yi imanin yin haka zai taimaka wa gwamnati wajen taskace kudaden shiga ta yadda za a amfana da harkar yadda ya kamata”, ya kuma ce, dakatarwa abu ne na wucin gadi.

Ita kuwa Jihar Zamfara ta bayyana cewa, ta haramta hakar ma’adanai ne saboda yadda hakar ma’adanan ya ke kara ta’azara mastalar tsaron da ake fuskanta a sassan jihar.

Kwamishinan yada labarai na jihar, Munnir Haidara ya bayyana cewa, suna sane da cewa, ba hurumin su ne haramnta hakar ma’adainai ba amma sun yi haka ne saboda a samu shawo kan matsalar tsaron da ake fuskanta a sassan jihar.

A watan Satumba ne Ministan hakar ma’adanai, Dele Alake, ya ba dukkan masu hakar ma’adanai ba bsia ka’ida ba da su tabbatar sun samu lasisi nan da kwanaki 30 ko kuma su fuskanci fushin hukuma, ya kuma kafa kwamitin na musamman da suka hada da ‘sojoji da ‘yansanda don samar da tsaro a wuraren hakar ma’adanai a sassan Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri
Labarai

Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar
Manyan Labarai

Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

October 24, 2025
Labarai

Gwamnatin Katsina Ta Ƙara Samar Da Dakarun Tsaro 200 Domin Maganace Ta’addanci

October 24, 2025
Next Post
Somaliya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Da Su Taimakawa Somaliya Wajen Tunkarar Kalubale

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

October 24, 2025
Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

October 24, 2025
An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 24, 2025

Gwamnatin Katsina Ta Ƙara Samar Da Dakarun Tsaro 200 Domin Maganace Ta’addanci

October 24, 2025
Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

October 24, 2025
Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

October 24, 2025
An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

October 24, 2025
Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15 

Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15 

October 24, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Wa Sarakuna Ba Zai Rage Musu Iko Ba A Shirinsa Na Ƙirƙirar Sabbin Masarautu

Gwamnan Bauchi Ya Naɗa Yayansa A Matsayin Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.