• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Katsalandan A Harkokin Ma’adanai: Gwamnatin Tarayya Ta Gargadi Jihohi

by Bello Hamza
2 years ago
in Labarai
0
Katsalandan A Harkokin Ma’adanai: Gwamnatin Tarayya Ta Gargadi Jihohi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Harkokin Ma’adanai, Dakta Oladele Alake ya bayyana cewa, gwamnatocin jihohi basu da hurumi a dokokin Nijeriya na sanya hannu a kan yadda ake tafiyar da harkokin hakar ma’adanai a kasar nan, ya kuma ce, haramun ne yadda jihohi suke bayar da umanin dakatar da hakar ma’adanai a jihohinsu domin dokokin Nijeriya bai basu damar na yin haka ba.

Ministan ya bayyana matsayar gwamnatin tarayyar ne a taron manema labarai a Abuja a bikin ranar harkokin hakar ma’adanai na shekarar 2023.

  • Zaman Lafiya: MDD Ta Fara Yunkurin Samar Da Wani Sabon Tsari A Kaduna Da Katsina
  • Tinubu Ya Naɗa Sababbin Shugabannin Hukumomin Yaɗa Labarai

Ya ce, “Yadda jihohi ke haramta harkokin hakar ma’adanai a sassan Nijeriya abin takaici ne. Ina amfani da wannan damar na sanar da al’ummar Nijeriya cewa, babu wata jiha da take da hurumin katsalandan a harkokokin hakar ma’adanai, wanna abin da ya shafi tsarin mulkin Nijeriya ne kai tsaye.

“Hakar ma’adai abu ne da yake a matsayin hurumi na gwamnatin tarayya, kamar yadcda tsarin mulki ya zayyana. Hakki ne na gwamnatin tarayya babu tamtama a kai.

Duk wani ma’adani da Allah ya shimfida a cikin kasa mallakin gwamnatin tarayya ne, a saboda haka gwamnatin tarayya ce kadai ke da ikon tasarufin su baki daya, kamar hakar ma’adanai da lamarin albarkatun man fetur duk a karkashin gwamnatin tarayya suke. Gwamnatin taraya ce keda ikon yin dokokin da za su tafiyar da yadda za a gudanar da su a mastayin albarkar kasa mallakin al’ummar Nijeriya gaba daya.”

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Ministan ya kuma ce, in har gwamnatocin jihohi na son shiga harka hakar ma’adanai sai su bi tsarin da ya dace ta hanyar karbar lasisin yin haka kamar yadda doka ta tanada.
Ya ce, gwamnatin taraya ba tana shirin fada da gwamnatocin jihohi ba ne amma za ta ci gaba da ilimantar da su a kan lamarin don a samu ci gaban da ake bukata, ya kuma ce, ya samu haduwa da shugaban kungiyar gwamnonin Nijeriya inda suka samu fahimtar jun a a kan lamarin.

Bincike a halin yanzu ya nuna cewa, jihohin n da suka haramta hakar ma’adanai a yankin su sun hada da Kebbi, Zamfara, Taraba, da Osun.

Gwamnatin Jihar Kebbi ta bayyana dalilan da ya sa suka haramta hakar ma’adanai a sassan jihar. Sakataren gwamnan jihar, Ahmed Idris, ya bayyana wa manema labarai cewa, sun haramta hakar ma’adanai a jihar ne don su daidaita yadda ake tafiyar da hakar ma’adanan a jihar.

Ya ce, “Mun yi imanin yin haka zai taimaka wa gwamnati wajen taskace kudaden shiga ta yadda za a amfana da harkar yadda ya kamata”, ya kuma ce, dakatarwa abu ne na wucin gadi.

Ita kuwa Jihar Zamfara ta bayyana cewa, ta haramta hakar ma’adanai ne saboda yadda hakar ma’adanan ya ke kara ta’azara mastalar tsaron da ake fuskanta a sassan jihar.

Kwamishinan yada labarai na jihar, Munnir Haidara ya bayyana cewa, suna sane da cewa, ba hurumin su ne haramnta hakar ma’adainai ba amma sun yi haka ne saboda a samu shawo kan matsalar tsaron da ake fuskanta a sassan jihar.

A watan Satumba ne Ministan hakar ma’adanai, Dele Alake, ya ba dukkan masu hakar ma’adanai ba bsia ka’ida ba da su tabbatar sun samu lasisi nan da kwanaki 30 ko kuma su fuskanci fushin hukuma, ya kuma kafa kwamitin na musamman da suka hada da ‘sojoji da ‘yansanda don samar da tsaro a wuraren hakar ma’adanai a sassan Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ma'danaiNejaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Yi Amfani Da Jarin Waje Da Ya Kai Dalar Amurka Biliyan 125.74 Tsakanin Janairu Da Satumban Bana

Next Post

Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Da Su Taimakawa Somaliya Wajen Tunkarar Kalubale

Related

‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas
Labarai

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

10 minutes ago
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa
Manyan Labarai

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

48 minutes ago
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano
Labarai

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

3 hours ago
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark
Labarai

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

4 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara
Labarai

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

7 hours ago
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace
Labarai

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

8 hours ago
Next Post
Somaliya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Da Su Taimakawa Somaliya Wajen Tunkarar Kalubale

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

July 27, 2025
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

July 27, 2025
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

July 27, 2025
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.