ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Katsalandan A Harkokin Ma’adanai: Gwamnatin Tarayya Ta Gargadi Jihohi

by Bello Hamza
3 years ago
Ma'adanai

Ministan Harkokin Ma’adanai, Dakta Oladele Alake ya bayyana cewa, gwamnatocin jihohi basu da hurumi a dokokin Nijeriya na sanya hannu a kan yadda ake tafiyar da harkokin hakar ma’adanai a kasar nan, ya kuma ce, haramun ne yadda jihohi suke bayar da umanin dakatar da hakar ma’adanai a jihohinsu domin dokokin Nijeriya bai basu damar na yin haka ba.

Ministan ya bayyana matsayar gwamnatin tarayyar ne a taron manema labarai a Abuja a bikin ranar harkokin hakar ma’adanai na shekarar 2023.

  • Zaman Lafiya: MDD Ta Fara Yunkurin Samar Da Wani Sabon Tsari A Kaduna Da Katsina
  • Tinubu Ya Naɗa Sababbin Shugabannin Hukumomin Yaɗa Labarai

Ya ce, “Yadda jihohi ke haramta harkokin hakar ma’adanai a sassan Nijeriya abin takaici ne. Ina amfani da wannan damar na sanar da al’ummar Nijeriya cewa, babu wata jiha da take da hurumin katsalandan a harkokokin hakar ma’adanai, wanna abin da ya shafi tsarin mulkin Nijeriya ne kai tsaye.

ADVERTISEMENT

“Hakar ma’adai abu ne da yake a matsayin hurumi na gwamnatin tarayya, kamar yadcda tsarin mulki ya zayyana. Hakki ne na gwamnatin tarayya babu tamtama a kai.

Duk wani ma’adani da Allah ya shimfida a cikin kasa mallakin gwamnatin tarayya ne, a saboda haka gwamnatin tarayya ce kadai ke da ikon tasarufin su baki daya, kamar hakar ma’adanai da lamarin albarkatun man fetur duk a karkashin gwamnatin tarayya suke. Gwamnatin taraya ce keda ikon yin dokokin da za su tafiyar da yadda za a gudanar da su a mastayin albarkar kasa mallakin al’ummar Nijeriya gaba daya.”

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

Ministan ya kuma ce, in har gwamnatocin jihohi na son shiga harka hakar ma’adanai sai su bi tsarin da ya dace ta hanyar karbar lasisin yin haka kamar yadda doka ta tanada.
Ya ce, gwamnatin taraya ba tana shirin fada da gwamnatocin jihohi ba ne amma za ta ci gaba da ilimantar da su a kan lamarin don a samu ci gaban da ake bukata, ya kuma ce, ya samu haduwa da shugaban kungiyar gwamnonin Nijeriya inda suka samu fahimtar jun a a kan lamarin.

Bincike a halin yanzu ya nuna cewa, jihohin n da suka haramta hakar ma’adanai a yankin su sun hada da Kebbi, Zamfara, Taraba, da Osun.

Gwamnatin Jihar Kebbi ta bayyana dalilan da ya sa suka haramta hakar ma’adanai a sassan jihar. Sakataren gwamnan jihar, Ahmed Idris, ya bayyana wa manema labarai cewa, sun haramta hakar ma’adanai a jihar ne don su daidaita yadda ake tafiyar da hakar ma’adanan a jihar.

Ya ce, “Mun yi imanin yin haka zai taimaka wa gwamnati wajen taskace kudaden shiga ta yadda za a amfana da harkar yadda ya kamata”, ya kuma ce, dakatarwa abu ne na wucin gadi.

Ita kuwa Jihar Zamfara ta bayyana cewa, ta haramta hakar ma’adanai ne saboda yadda hakar ma’adanan ya ke kara ta’azara mastalar tsaron da ake fuskanta a sassan jihar.

Kwamishinan yada labarai na jihar, Munnir Haidara ya bayyana cewa, suna sane da cewa, ba hurumin su ne haramnta hakar ma’adainai ba amma sun yi haka ne saboda a samu shawo kan matsalar tsaron da ake fuskanta a sassan jihar.

A watan Satumba ne Ministan hakar ma’adanai, Dele Alake, ya ba dukkan masu hakar ma’adanai ba bsia ka’ida ba da su tabbatar sun samu lasisi nan da kwanaki 30 ko kuma su fuskanci fushin hukuma, ya kuma kafa kwamitin na musamman da suka hada da ‘sojoji da ‘yansanda don samar da tsaro a wuraren hakar ma’adanai a sassan Nijeriya.

Ma'adanai
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

MASU ALAKA

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

July 8, 2026
Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA
Labarai

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

July 8, 2026
Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi
Manyan Labarai

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

July 8, 2026
Next Post
Somaliya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Da Su Taimakawa Somaliya Wajen Tunkarar Kalubale

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

July 8, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

July 8, 2026
Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

July 8, 2026
Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

July 8, 2026
Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

July 8, 2026
Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

July 8, 2026
Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

July 8, 2026
Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

July 8, 2026
Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

July 8, 2026
NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

July 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.