ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Katsalandan A Harkokin Ma’adanai: Gwamnatin Tarayya Ta Gargadi Jihohi

by Bello Hamza
3 years ago
Ma'adanai

Ministan Harkokin Ma’adanai, Dakta Oladele Alake ya bayyana cewa, gwamnatocin jihohi basu da hurumi a dokokin Nijeriya na sanya hannu a kan yadda ake tafiyar da harkokin hakar ma’adanai a kasar nan, ya kuma ce, haramun ne yadda jihohi suke bayar da umanin dakatar da hakar ma’adanai a jihohinsu domin dokokin Nijeriya bai basu damar na yin haka ba.

Ministan ya bayyana matsayar gwamnatin tarayyar ne a taron manema labarai a Abuja a bikin ranar harkokin hakar ma’adanai na shekarar 2023.

  • Zaman Lafiya: MDD Ta Fara Yunkurin Samar Da Wani Sabon Tsari A Kaduna Da Katsina
  • Tinubu Ya Naɗa Sababbin Shugabannin Hukumomin Yaɗa Labarai

Ya ce, “Yadda jihohi ke haramta harkokin hakar ma’adanai a sassan Nijeriya abin takaici ne. Ina amfani da wannan damar na sanar da al’ummar Nijeriya cewa, babu wata jiha da take da hurumin katsalandan a harkokokin hakar ma’adanai, wanna abin da ya shafi tsarin mulkin Nijeriya ne kai tsaye.

ADVERTISEMENT

“Hakar ma’adai abu ne da yake a matsayin hurumi na gwamnatin tarayya, kamar yadcda tsarin mulki ya zayyana. Hakki ne na gwamnatin tarayya babu tamtama a kai.

Duk wani ma’adani da Allah ya shimfida a cikin kasa mallakin gwamnatin tarayya ne, a saboda haka gwamnatin tarayya ce kadai ke da ikon tasarufin su baki daya, kamar hakar ma’adanai da lamarin albarkatun man fetur duk a karkashin gwamnatin tarayya suke. Gwamnatin taraya ce keda ikon yin dokokin da za su tafiyar da yadda za a gudanar da su a mastayin albarkar kasa mallakin al’ummar Nijeriya gaba daya.”

LABARAI MASU NASABA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

Ministan ya kuma ce, in har gwamnatocin jihohi na son shiga harka hakar ma’adanai sai su bi tsarin da ya dace ta hanyar karbar lasisin yin haka kamar yadda doka ta tanada.
Ya ce, gwamnatin taraya ba tana shirin fada da gwamnatocin jihohi ba ne amma za ta ci gaba da ilimantar da su a kan lamarin don a samu ci gaban da ake bukata, ya kuma ce, ya samu haduwa da shugaban kungiyar gwamnonin Nijeriya inda suka samu fahimtar jun a a kan lamarin.

Bincike a halin yanzu ya nuna cewa, jihohin n da suka haramta hakar ma’adanai a yankin su sun hada da Kebbi, Zamfara, Taraba, da Osun.

Gwamnatin Jihar Kebbi ta bayyana dalilan da ya sa suka haramta hakar ma’adanai a sassan jihar. Sakataren gwamnan jihar, Ahmed Idris, ya bayyana wa manema labarai cewa, sun haramta hakar ma’adanai a jihar ne don su daidaita yadda ake tafiyar da hakar ma’adanan a jihar.

Ya ce, “Mun yi imanin yin haka zai taimaka wa gwamnati wajen taskace kudaden shiga ta yadda za a amfana da harkar yadda ya kamata”, ya kuma ce, dakatarwa abu ne na wucin gadi.

Ita kuwa Jihar Zamfara ta bayyana cewa, ta haramta hakar ma’adanai ne saboda yadda hakar ma’adanan ya ke kara ta’azara mastalar tsaron da ake fuskanta a sassan jihar.

Kwamishinan yada labarai na jihar, Munnir Haidara ya bayyana cewa, suna sane da cewa, ba hurumin su ne haramnta hakar ma’adainai ba amma sun yi haka ne saboda a samu shawo kan matsalar tsaron da ake fuskanta a sassan jihar.

A watan Satumba ne Ministan hakar ma’adanai, Dele Alake, ya ba dukkan masu hakar ma’adanai ba bsia ka’ida ba da su tabbatar sun samu lasisi nan da kwanaki 30 ko kuma su fuskanci fushin hukuma, ya kuma kafa kwamitin na musamman da suka hada da ‘sojoji da ‘yansanda don samar da tsaro a wuraren hakar ma’adanai a sassan Nijeriya.

Ma'adanai
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shekara 3 Da Shirin Ceto Jihar Zamfara: Jinjina Ta Musamman Ga Gwamna Dauda Lawal
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    An Yi Tir Da ‘Yan Takarar Da Suka Fice Daga APC Saboda Faduwa Zabe
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kotu Ta Yi Gwanjon Kaddarorin Sani Sha’aban Bisa Taurin Bashi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

MASU ALAKA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci
Ra'ayi Riga

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
Manyan Labarai

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
Next Post
Somaliya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Da Su Taimakawa Somaliya Wajen Tunkarar Kalubale

LABARAI MASU NASABA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

June 13, 2026
Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

June 13, 2026
Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

June 13, 2026
Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.