• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Katsewar Intanet: Samar Da Sabbin Wayoyi Zai Lakume Dala Biliyan 1

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Kimiyya Da Fasahar Sadarwa
0
Katsewar Intanet: Samar Da Sabbin Wayoyi Zai Lakume Dala Biliyan 1
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bisa yawaitar yankewar kebul-kebul na cikin teku a ‘yan kwanakin baya da ya janyo katsewa da cikas ga ayyukan internet a Nijeriya da ma wasu sassan kasashen yammacin Afrika yanzu haka na bukatar makonni shida ko takwas kafin a iya gyarawa da cikakken karfin network zai dawo kamar yadda yake, a cewar bayanin da MainOne ta fitar.

LEADERSHIP ta labarto cewa a ranar Alhamis 14 ga watan Maris na 2024 al’umma sun fuskaci matsalolin yankewar karfin networks a kasashe 12 na Afrika ciki har da Nijeriya.

  • Kisan Okuama: Baƙin Cikin Da Ke Tattare Da Labarin
  • An Gabatar Da Rahoton Binciken Kamfanonin Sin Game Da Halinsu Na Zuba Jari a Ketare a 2023

Wadanda matsalar yankewar kebul din cikin tekun ya shafa sun hada da na West Africa Cable System (WACS), Africa Coast to Europe (ACE), MainOne, da kuma SAT3, wanda suka yi mummunar tasiri wajen kawo cikas ga lamuran data da kuma kamfanonin sadarwa a kasashe da dama na yammacin Afrika, musamman wadanda suka fi fuskantar matsalar ma su ne Nijeriya, Ghana, Senegal da kasar Kod-debuwa da lamarin ya janyo cikas da katsewar sabis din yanar gizo kuma ya shafi bangarorin tattalin arziki.

Nijeriya dai na cigaba da kirga maguden kudade na biliyoyi da take asararsu sakamakon lalacewar manyan igiyoyin kebul da ke karkashin tekuna musamman kebul din da ke Bahar Maliya da na gabar tekun yammacin Afrika. A misali, NetBlocks da ke sanya ido kan tsaron yanar gizo da yadda ake gudanar da lamuran internet, ya yi kiyasin cewa Nijeriya ta yi asarar naira biliyan 273 a cikin kwanaki hudu tsakanin ranar 14 ga watan Maris zuwa 17 ga watan Maris.
Kamfanin fasahar zamanin wanda ya bada bayanin tsare-tsaren gyaran a ranar Litinin, an kuma jero ranakun da za a bi wajen gyaran tare da cewa tunin aka fara jibge wasu kayan da suka shafi na gyara.

Kamfanin ya ce domin gyara manyan kebul-kebul dinsa guda hudu, yanzu haka na aikin hadin guiwa da abokan hulda wajen ganin an cimma nasara, “Muna da kwarin guiwar gyaranmu na igiyoyin sadarwarmu za su yi nasara kuma karfin sabis dinmu zai dawo yadda ya dace.”

Labarai Masu Nasaba

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet

Domin dakile faruwar irin wannan a nan gaba a Afrika baki daya, shugaban WIOCC, Chris Wood, ya ce gyaran zai iya lakume wa Afrika sama da dala biliyan daya wajen shimfida sabbin igiyoyin internet daga Afrika ta kudu zuwa Europe, da zai hada kasashe da dama ciki har da Nijeriya.

“Akwai tsada sosai a ina gina sabun kebul daga Afrika ta kudu zuwa Turai, da zai hada kasashe da daman gaske. A kalla zai iya cinye dala biliyan 1, wanda ya yi yawa sosai. Don haka ba abu ne mai sauki ba. Zai yi nauyi wa mutum ya biya wannan dalolin, ammai akwai bukatar ganin alfanunsa idan an cire kudi, sai dai zai dauki tsawon lokaci kafin a iya tsara wadannan igiyoyin.”

Ma’aikata Ta Samar Da Shafin Yanar Gizo Domin Zamanantar Da Ayyukanta
A yunkurin ma’aikatar gwamnatin tarayya na zamantar da ayyuka da tafiya daidai da zamani, ma’aikatar gidaje da tsara birane ta gwamnatin tarayya ta samar da wani shafin yanar gizo da ya kasance turaka da zai ke saukaka tafiyar da ayyukanta.

A wata sanarwa da daraktan yada labarai na ma’aikatar Badamasi Salisu Haiba ya fitar, ya ce turakar yanar gizon shine irinsa na farko da ma’aikatar ta yi tun lokacin da tsame ma’aikatar daga ma’aikatar ayyuka da gidaje yanzu shafin shi ne www.fmhud.gob.ng.

Da ya ke kaddamar da shafin, babban sakatare a ma’aikatar, Dakta Marcus Ogunbiyi, ya jinjina wa kokarin sashin fasahar zamani na ma’aikatar (ICT) bisa inganta matakin samar da internet mai karfi, a cewarsa, lamarin wani mataki ne mai kyau na tafiya daidai da zamani a lamuran da suka shafi hidimar aiki, wanda a cewarsa na daga daga cikin muhimman ginshiki da tsare-tsaren da dabarbarun ma’aikatar kula da ma’aikata ta gwamnatin tarayya ta sanya a gaba (FCSSIP 25).

“Fasahar zamani wani mataki ne da ake kokarin dauka na inganta ayyukan gwamnati da shi, don haka wannan kaddamarwar da ma’aikatar ta yi na sashin yanar gizo babban cigaba ne kuma abun murna ne,” ya shaida.
Da yake umartar dukkanin rassa da sashi-sashi da suke tura aikace-aikacensu ga sashin fasahar zamani (ICT) na ma’aikatar domin kwaskwarima da daurawa a shafin yanar gizon kai tsaye, babban sakataren ya kuma sanar da karin cigaba na cewa an kirkiri turakar email a hukumance ga kowani ma’aikacin ma’aikatar, ya ce, hakan zai taimaka wajen kyautata aiki da saukaka aiki hadi da wanzar da komai cikin gaskiya.

Tun da farko, daraktan sashin fasahar zamani, Marcus Amiolemen, ya ce, “Yanzu zamani ne na yanar gizo, kowace kungiya ko ma’aikaar da ta kasa mallakar shafin yanar gizo ba za ta samu nasarar cimma muhimman nasarori ba.

“Wannan shafin da muka samar zai kasance dandamali na baje ayyuka da shirye-shiryen ma’aikatar ga duniya baki daya, shafin na da saukin shiga,” ya shaida.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Rundunar ‘Yansandan Bauchi Ta Fara Cafko Masu Garkuwa Ta Amfani Da Fasahar Zamani

Next Post

Shekara Guda Bayan Zaben 2023: Har Yanzu Nijeriya Ba Ta Warware Ba

Related

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

3 weeks ago
Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet

2 months ago
Hanyoyin Kare Kanka Daga Damfara Ta Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Hanyoyin Kare Kanka Daga Damfara Ta Intanet

2 months ago
Yadda Za A Kare Yara Daga Barazanar Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Yadda Za A Kare Yara Daga Barazanar Intanet

3 months ago
Mantuwa Na Matukar Taimakon Rayuwar Mutane – Masani
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Mantuwa Na Matukar Taimakon Rayuwar Mutane – Masani

7 months ago
Yadda Na Kirkiro ‘Brain-chip’ Da Ke Dawo Wa Wadanda Aka Haifa Da Makanta Ganinsu – Elon Musk
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Yadda Na Kirkiro ‘Brain-chip’ Da Ke Dawo Wa Wadanda Aka Haifa Da Makanta Ganinsu – Elon Musk

7 months ago
Next Post
Gwamnati Ta Dakatar Da Daraktocin Hukumar Sufurin Jiragen Sama 5 Sa’o’i Kadan Bayan Sauke Shugabanninsu

Shekara Guda Bayan Zaben 2023: Har Yanzu Nijeriya Ba Ta Warware Ba

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.