ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Katsewar Intanet: Samar Da Sabbin Wayoyi Zai Lakume Dala Biliyan 1

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Intanet

Bisa yawaitar yankewar kebul-kebul na cikin teku a ‘yan kwanakin baya da ya janyo katsewa da cikas ga ayyukan internet a Nijeriya da ma wasu sassan kasashen yammacin Afrika yanzu haka na bukatar makonni shida ko takwas kafin a iya gyarawa da cikakken karfin network zai dawo kamar yadda yake, a cewar bayanin da MainOne ta fitar.

LEADERSHIP ta labarto cewa a ranar Alhamis 14 ga watan Maris na 2024 al’umma sun fuskaci matsalolin yankewar karfin networks a kasashe 12 na Afrika ciki har da Nijeriya.

  • Kisan Okuama: Baƙin Cikin Da Ke Tattare Da Labarin
  • An Gabatar Da Rahoton Binciken Kamfanonin Sin Game Da Halinsu Na Zuba Jari a Ketare a 2023

Wadanda matsalar yankewar kebul din cikin tekun ya shafa sun hada da na West Africa Cable System (WACS), Africa Coast to Europe (ACE), MainOne, da kuma SAT3, wanda suka yi mummunar tasiri wajen kawo cikas ga lamuran data da kuma kamfanonin sadarwa a kasashe da dama na yammacin Afrika, musamman wadanda suka fi fuskantar matsalar ma su ne Nijeriya, Ghana, Senegal da kasar Kod-debuwa da lamarin ya janyo cikas da katsewar sabis din yanar gizo kuma ya shafi bangarorin tattalin arziki.

ADVERTISEMENT

Nijeriya dai na cigaba da kirga maguden kudade na biliyoyi da take asararsu sakamakon lalacewar manyan igiyoyin kebul da ke karkashin tekuna musamman kebul din da ke Bahar Maliya da na gabar tekun yammacin Afrika. A misali, NetBlocks da ke sanya ido kan tsaron yanar gizo da yadda ake gudanar da lamuran internet, ya yi kiyasin cewa Nijeriya ta yi asarar naira biliyan 273 a cikin kwanaki hudu tsakanin ranar 14 ga watan Maris zuwa 17 ga watan Maris.
Kamfanin fasahar zamanin wanda ya bada bayanin tsare-tsaren gyaran a ranar Litinin, an kuma jero ranakun da za a bi wajen gyaran tare da cewa tunin aka fara jibge wasu kayan da suka shafi na gyara.

Kamfanin ya ce domin gyara manyan kebul-kebul dinsa guda hudu, yanzu haka na aikin hadin guiwa da abokan hulda wajen ganin an cimma nasara, “Muna da kwarin guiwar gyaranmu na igiyoyin sadarwarmu za su yi nasara kuma karfin sabis dinmu zai dawo yadda ya dace.”

LABARAI MASU NASABA

Zarewa Ta Ƙirƙiro Na’urar Gano Tsatsa Bayan Lashe Kyautar ‘Carbon Neutrality’ Ta Duniya

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

Domin dakile faruwar irin wannan a nan gaba a Afrika baki daya, shugaban WIOCC, Chris Wood, ya ce gyaran zai iya lakume wa Afrika sama da dala biliyan daya wajen shimfida sabbin igiyoyin internet daga Afrika ta kudu zuwa Europe, da zai hada kasashe da dama ciki har da Nijeriya.

“Akwai tsada sosai a ina gina sabun kebul daga Afrika ta kudu zuwa Turai, da zai hada kasashe da daman gaske. A kalla zai iya cinye dala biliyan 1, wanda ya yi yawa sosai. Don haka ba abu ne mai sauki ba. Zai yi nauyi wa mutum ya biya wannan dalolin, ammai akwai bukatar ganin alfanunsa idan an cire kudi, sai dai zai dauki tsawon lokaci kafin a iya tsara wadannan igiyoyin.”

Ma’aikata Ta Samar Da Shafin Yanar Gizo Domin Zamanantar Da Ayyukanta
A yunkurin ma’aikatar gwamnatin tarayya na zamantar da ayyuka da tafiya daidai da zamani, ma’aikatar gidaje da tsara birane ta gwamnatin tarayya ta samar da wani shafin yanar gizo da ya kasance turaka da zai ke saukaka tafiyar da ayyukanta.

A wata sanarwa da daraktan yada labarai na ma’aikatar Badamasi Salisu Haiba ya fitar, ya ce turakar yanar gizon shine irinsa na farko da ma’aikatar ta yi tun lokacin da tsame ma’aikatar daga ma’aikatar ayyuka da gidaje yanzu shafin shi ne www.fmhud.gob.ng.

Da ya ke kaddamar da shafin, babban sakatare a ma’aikatar, Dakta Marcus Ogunbiyi, ya jinjina wa kokarin sashin fasahar zamani na ma’aikatar (ICT) bisa inganta matakin samar da internet mai karfi, a cewarsa, lamarin wani mataki ne mai kyau na tafiya daidai da zamani a lamuran da suka shafi hidimar aiki, wanda a cewarsa na daga daga cikin muhimman ginshiki da tsare-tsaren da dabarbarun ma’aikatar kula da ma’aikata ta gwamnatin tarayya ta sanya a gaba (FCSSIP 25).

“Fasahar zamani wani mataki ne da ake kokarin dauka na inganta ayyukan gwamnati da shi, don haka wannan kaddamarwar da ma’aikatar ta yi na sashin yanar gizo babban cigaba ne kuma abun murna ne,” ya shaida.
Da yake umartar dukkanin rassa da sashi-sashi da suke tura aikace-aikacensu ga sashin fasahar zamani (ICT) na ma’aikatar domin kwaskwarima da daurawa a shafin yanar gizon kai tsaye, babban sakataren ya kuma sanar da karin cigaba na cewa an kirkiri turakar email a hukumance ga kowani ma’aikacin ma’aikatar, ya ce, hakan zai taimaka wajen kyautata aiki da saukaka aiki hadi da wanzar da komai cikin gaskiya.

Tun da farko, daraktan sashin fasahar zamani, Marcus Amiolemen, ya ce, “Yanzu zamani ne na yanar gizo, kowace kungiya ko ma’aikaar da ta kasa mallakar shafin yanar gizo ba za ta samu nasarar cimma muhimman nasarori ba.

“Wannan shafin da muka samar zai kasance dandamali na baje ayyuka da shirye-shiryen ma’aikatar ga duniya baki daya, shafin na da saukin shiga,” ya shaida.

Intanet
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Zarewa Ta Ƙirƙiro Na’urar Gano Tsatsa Bayan Lashe Kyautar ‘Carbon Neutrality’ Ta Duniya
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Zarewa Ta Ƙirƙiro Na’urar Gano Tsatsa Bayan Lashe Kyautar ‘Carbon Neutrality’ Ta Duniya

February 21, 2026
Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

September 5, 2025
Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

April 19, 2025
Next Post
Gwamnati Ta Dakatar Da Daraktocin Hukumar Sufurin Jiragen Sama 5 Sa’o’i Kadan Bayan Sauke Shugabanninsu

Shekara Guda Bayan Zaben 2023: Har Yanzu Nijeriya Ba Ta Warware Ba

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.