• English
  • Business News
Sunday, July 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shekara Guda Bayan Zaben 2023: Har Yanzu Nijeriya Ba Ta Warware Ba

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Gwamnati Ta Dakatar Da Daraktocin Hukumar Sufurin Jiragen Sama 5 Sa’o’i Kadan Bayan Sauke Shugabanninsu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ranakun 25 ga watan fabrairu da 11 ga watan Maris shekarar 2024, sun zama ranakun da suke tuna wa ‘yan Nijeriya lokacin da aka gudanar da zabuka masu cike da tarihi a kasar nan.

Wadannan ranakun ne da aka gudanar da zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisun kasa da kuma zaben gwamnoni da na ‘yan majalisun jihohi.

  • Azumi Lokaci Zafi: Yadda ‘Yan Kasuwar Kankara Ke Camamarsu A Yobe Da Zamfara
  • Jimilar Kudin Da Sin Ta Samu Wajen Jigilar Kayayyaki A Farkon Watanni Biyu Na Bana Ta Kai Yuan Triliyan 55.4

Zabukan sun kasance masu muhimmancin gaske, kasancewar ana gudanar da gwamnatin farar hula na tsawon shekaru 24 ba tare da katse ba, ma’ana sojoji ba su amshi mulki ba, kuma karo na farko a tarihin Nijeriya tun bayan samun mulkin kai. An dai samu masu saka ido na cikin gida da kuma kasashen ketare da wadannan zabuka.

Mafi yawan masu sanya idanu sun bayyana cewa zaben 2023 shi ne mafi tsada a Nijeriya, inda ya lashe makudan kudade sama da naira biliyan 355 tun daga buga takardun jefa kuri’a har zuwa hidindimun da aka gudanar a lokacin zaben da kuma bayan zaben.

Duk da an sami karin rajistar masu zabe har miliyan 10 bayan a baya ana da miliyan 84, an sami karancin fitowar masu jefa kuri’a.

Labarai Masu Nasaba

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

A shekarun da suka gabata, an yi kokarin kauce wa wasu matslaolin zabe da ake samu kamar satar akwati da tarwatsa wajen zabe da wasu bata-gari ke yi da saye da sayar da kuri’a da matsalar tsaro da karya dokokin zabe da wasu jam’iyyu ke yi wajen tsayar da dan takara.

A batun gaskiya, zaben da aka gudanar a wasu yankuna a watan Nuwamba na shekarar 2023, ya sanya an gano wasu kura-kurai da jam’iyyun siyasa suke tafkawa, wanda ya zama izina ga hukuma da su kansu jam’iyyu. Hakan ta za aka dauki mataki a zaben gwamnonin da za a gudanar a jihohin Edo da Ondo a shekarar 2024.

Zaben 2023 ya zo da wasu kalubale da suka hada da fargaban rashin tsaro da matsalar tattalin arziki da talauci da ya addabi al’umma ta ko’ina, wanda ya hade da burukan ‘yan siyasa da suke neman madafun iko ta kowani hali.

Kafin lokacin zaben, wasu abubuwa sun kara bayyana kamar kabilanci da bangaranci da bambance-bambancen addini, wanda wadannan dalilai suna daga cikin abubuwan da suka sanya aka sami karancin masu fitowa zabe.

Haka kuma zaben 2023, an sayi kuri’u masu yawan gaske, inda ‘yan siyasa suka rika bai wa al’umma kudi da kyaututtuka, wadannan abubuwan sun shafi kima da darajar zaben matuka don sun yi tasiri sosai.

Baya ga wadannan kuma, wasu malaman addini da masana sun rika amfani da damarsu wajen kira da a zabi wasu bangare, wanda wannan ma ya saba wa tsarin dimokuradiyya. Amma a hannu guda kuma, wasu malaman da masana harkokin rayuwa sun taka muhimmiyar rawa wajen samun nasarar zaben 2023.

Hukumar INEC wacce a halin yanzu take shirin gudanar da zabukan gwamnoni a jihohin Edo da Ondo ba tare da an sami matsaloli ba kamar yadda aka samu a zaben gwamnonin jihohin Kogi da Imo da Bayelsa a kwanakin baya, ta ja hankalin jam’iyyun siyasa wajen ganin sun iya abun da ya dace bisa tsarin doka.

Sanin kowa ne a duk inda za a yi zabe a duniya ba wai a Njeriya ba, ba a rasa wasu matsaloli daga nan zuwa can. Amma a nan Nijeriya babban abun da ake bukata shi ne, hukumar INEC ta yi kokarin yin adalci wajen ayyukanta, yin haka ne kawai zai tabbatar da dorewar dimokuradiyya.

Sannan hakan ne zai sa al’umma su rika fitowa yin zaben, domin suna da tabbacin za a ba su abun da suka zaba, kuma za a tsare masu rayukansu.

Alamu dai na nuna cewa har yanzu dai a bangaren zabe, Nijeriya ba ta tsaya da kafafunta ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Katsewar Intanet: Samar Da Sabbin Wayoyi Zai Lakume Dala Biliyan 1

Next Post

Ya Kamata Gwamnati Ta Haramta Wa Mata Baza Jarirai A Titinan Kano – Sarkin Dillalan Kano

Related

Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Tambarin Dimokuradiyya

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

1 day ago
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

1 day ago
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

1 day ago
Yadda Taron Kungiyar Gwagwarmayar Talakawa Ta Kaya Kan Zaben 2023 A Zariya
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

1 week ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Tambarin Dimokuradiyya

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

1 week ago
Zaben Gwamnoni: Za Mu Ba Marada Kunya – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kungiyoyi 110 Ne Ke Neman Rajistan Zama Jam’iyyun Siyasa A Yanzu Haka – INEC

1 week ago
Next Post
Yaya Da Kani Sun Mutu A Cikin Ramin Masai A Kano

Ya Kamata Gwamnati Ta Haramta Wa Mata Baza Jarirai A Titinan Kano - Sarkin Dillalan Kano

LABARAI MASU NASABA

Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC

Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC

July 13, 2025
NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

July 12, 2025
Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

July 12, 2025
Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

July 12, 2025
Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

July 12, 2025
Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

July 12, 2025
Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

July 12, 2025
Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

July 12, 2025
Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

July 12, 2025
Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

July 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.