ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shekara Guda Bayan Zaben 2023: Har Yanzu Nijeriya Ba Ta Warware Ba

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Zabe

Ranakun 25 ga watan fabrairu da 11 ga watan Maris shekarar 2024, sun zama ranakun da suke tuna wa ‘yan Nijeriya lokacin da aka gudanar da zabuka masu cike da tarihi a kasar nan.

Wadannan ranakun ne da aka gudanar da zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisun kasa da kuma zaben gwamnoni da na ‘yan majalisun jihohi.

  • Azumi Lokaci Zafi: Yadda ‘Yan Kasuwar Kankara Ke Camamarsu A Yobe Da Zamfara
  • Jimilar Kudin Da Sin Ta Samu Wajen Jigilar Kayayyaki A Farkon Watanni Biyu Na Bana Ta Kai Yuan Triliyan 55.4

Zabukan sun kasance masu muhimmancin gaske, kasancewar ana gudanar da gwamnatin farar hula na tsawon shekaru 24 ba tare da katse ba, ma’ana sojoji ba su amshi mulki ba, kuma karo na farko a tarihin Nijeriya tun bayan samun mulkin kai. An dai samu masu saka ido na cikin gida da kuma kasashen ketare da wadannan zabuka.

ADVERTISEMENT

Mafi yawan masu sanya idanu sun bayyana cewa zaben 2023 shi ne mafi tsada a Nijeriya, inda ya lashe makudan kudade sama da naira biliyan 355 tun daga buga takardun jefa kuri’a har zuwa hidindimun da aka gudanar a lokacin zaben da kuma bayan zaben.

Duk da an sami karin rajistar masu zabe har miliyan 10 bayan a baya ana da miliyan 84, an sami karancin fitowar masu jefa kuri’a.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

A shekarun da suka gabata, an yi kokarin kauce wa wasu matslaolin zabe da ake samu kamar satar akwati da tarwatsa wajen zabe da wasu bata-gari ke yi da saye da sayar da kuri’a da matsalar tsaro da karya dokokin zabe da wasu jam’iyyu ke yi wajen tsayar da dan takara.

A batun gaskiya, zaben da aka gudanar a wasu yankuna a watan Nuwamba na shekarar 2023, ya sanya an gano wasu kura-kurai da jam’iyyun siyasa suke tafkawa, wanda ya zama izina ga hukuma da su kansu jam’iyyu. Hakan ta za aka dauki mataki a zaben gwamnonin da za a gudanar a jihohin Edo da Ondo a shekarar 2024.

Zaben 2023 ya zo da wasu kalubale da suka hada da fargaban rashin tsaro da matsalar tattalin arziki da talauci da ya addabi al’umma ta ko’ina, wanda ya hade da burukan ‘yan siyasa da suke neman madafun iko ta kowani hali.

Kafin lokacin zaben, wasu abubuwa sun kara bayyana kamar kabilanci da bangaranci da bambance-bambancen addini, wanda wadannan dalilai suna daga cikin abubuwan da suka sanya aka sami karancin masu fitowa zabe.

Haka kuma zaben 2023, an sayi kuri’u masu yawan gaske, inda ‘yan siyasa suka rika bai wa al’umma kudi da kyaututtuka, wadannan abubuwan sun shafi kima da darajar zaben matuka don sun yi tasiri sosai.

Baya ga wadannan kuma, wasu malaman addini da masana sun rika amfani da damarsu wajen kira da a zabi wasu bangare, wanda wannan ma ya saba wa tsarin dimokuradiyya. Amma a hannu guda kuma, wasu malaman da masana harkokin rayuwa sun taka muhimmiyar rawa wajen samun nasarar zaben 2023.

Hukumar INEC wacce a halin yanzu take shirin gudanar da zabukan gwamnoni a jihohin Edo da Ondo ba tare da an sami matsaloli ba kamar yadda aka samu a zaben gwamnonin jihohin Kogi da Imo da Bayelsa a kwanakin baya, ta ja hankalin jam’iyyun siyasa wajen ganin sun iya abun da ya dace bisa tsarin doka.

Sanin kowa ne a duk inda za a yi zabe a duniya ba wai a Njeriya ba, ba a rasa wasu matsaloli daga nan zuwa can. Amma a nan Nijeriya babban abun da ake bukata shi ne, hukumar INEC ta yi kokarin yin adalci wajen ayyukanta, yin haka ne kawai zai tabbatar da dorewar dimokuradiyya.

Sannan hakan ne zai sa al’umma su rika fitowa yin zaben, domin suna da tabbacin za a ba su abun da suka zaba, kuma za a tsare masu rayukansu.

Alamu dai na nuna cewa har yanzu dai a bangaren zabe, Nijeriya ba ta tsaya da kafafunta ba.

Zabe
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
Yaya Da Kani Sun Mutu A Cikin Ramin Masai A Kano

Ya Kamata Gwamnati Ta Haramta Wa Mata Baza Jarirai A Titinan Kano - Sarkin Dillalan Kano

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.