Kimanin ‘ya’yan jam’iyyar APC su 1,000 ne suka fice daga jam’iyyar zuwa jam’iyyar NNPP a jihar Kano.
Mai magana da yawun gwamnan jihar Kano, Sanusi Bature Dawakin Tofa, a wata sanarwa da ya fitar a shafinsa na Facebook, ya ce, ‘ya’yan jam’iyyar APC sun sauya shekar ne a kananan hukumomin Tofa da Ghari inda shugaban jam’iyyar na jihar, Dr. Hashimu Dungurawa ya karbe su.
- Gobara Ta Ƙone Gidan Kakakin Majalisar Zamfara
- Amurka Ta Kitsa Shirin “Volt Typhoon” Ne Da Nufin Bata Sunan Wasu Kasashe
Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da jam’iyyar NNPP ta kara zage damtse domin samun nasara a zabukan kananan hukumomi da aka shirya gudanarwa a ranar 26 ga watan Oktoba mai zuwa a jihar Kano.
Jam’iyyar ta yi amfani da wannan dama wajen kaddamar da yakin neman zaben shugaban karamar hukumar gabanin zaben.
Dan takarar kujerar shugaban karamar hukumar Tofa a jam’iyyar NNPP, Yakubu Adis, da takwaransa na Ghari, Hashimu Mai Sabulu, a yayin bikin sun nuna kwarin gwiwa game da samun nasara a zaben da ke tafe.
Dukkan ‘yan takarar biyu sun bayyana jin dadinsu da samun sabbin magoya inda suka ce, wannan babbar nasara ce ga jam’iyyar NNPP.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp