• English
  • Business News
Sunday, July 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kiran Minista Ga VON: Ku Yaɗa Kyawawan Labarun Nijeriya Ga Duniya 

by yahuzajere
2 years ago
in Labarai
0
Kiran Minista Ga VON: Ku Yaɗa Kyawawan Labarun Nijeriya Ga Duniya 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya umarci gidan rediyon Muryar Nijeriya (VON) da ya maida hankali wajen yaɗa kyawawan labarai da shirye-shirye game da irin gudunmawar da Nijeriya ke bayarwa ga cigaban duniya.

Mataimakin Daraktan yaɗa labarai a ma’aikatar, Malam Suleiman Haruna, ya ruwaito a cikin sanarwa ga manema labarai da ya bayar cewa ministan ya yi wannan umurnin ne a lokacin da hukumar gudanarwa ta gidan rediyon ta kai masa ziyarar aiki a ofishin sa a Abuja a ranar Talata, 19 ga Disamba, 2023.

Ministan ya yi kira ga VON da ta isar da saƙon damarmakin da ke akwai, da haɗin gwiwa, da ingantuwar ƙasar Nijeriya ta yadda Nijeriya za ta ci moriyar Zuba Jari Kai-tsaye daga Waje.

Ya ce idan an samar da kyakkyawan yanayin yin kasuwanci, to gwamnati za ta samun ƙarin ayyukan yi da kuma kuɗin shiga.

Ya ce: “Ku na da rawar da za ku taka wajen aikin sauya fasalin zamantakewa da gwamnatin Tinubu ta sanya a gaba a yanzu.

Labarai Masu Nasaba

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

“Tilas ne ku riƙa isar da saƙon mu na ƙaruwar arziki da damarmakin da ke akwai, tare da jama’a ƙwararru a fannoni daban-daban don a jawo ra’ayin masu zuba jari da kuma masu yawon shaƙatawa zuwa Nijeriya.

  • Kafafen Yaɗa Labarai Ne Manyan Dirkokin Dimokraɗiyyarmu – Minista

 

“Nijeriya ta na kan hanyar ta ta samun martaba; tilas mu ƙarfafa gwiwar masu harkokin kasuwanci su shigo ciki a dama da su domin su amfana.”

Ministan ya ce ya na sane sosai da cewa sassa da dama na Nijeriya su na buƙatar a tallafa masu domin su shigo cikin wannan tsarin na sauya fasalin zamantakewa. Ya ce duk da hakan, gwamnatin ta na yin bakin ƙoƙarin ta domin magance matsaloli.

Akwai buƙatar gidan rediyon Muryar Nijeriya (VON) ya isar da wannan saƙon ga duniya, inji shi.

Tun da farko a nasa jawabin, sai da Darakta-Janar na Muryar Nijeriya, Alhaji Jibrin Baba Ndace, ya bayyana cewa hukumar gudanarwa da ma’aikatan gidan rediyon sun kawo ziyarar ne domin su sanar da ministan irin tsarin aiki da su ka fito da shi kuma su shaida masa cewa su na bin dukkan tsare-tsaren gwamnatin Tinubu sosai da sosai.

Darakta-Janar ɗin ya ba ministan tabbacin cewa duk da yake su na watsa shirye-shirye cikin harsunan ƙasashen waje guda huɗu ne, yanzu su na da burin su faɗaɗa zuwa harsunan wasu manyan ƙasashen irin su Chaina da Indiya, waɗanda su na gudanar da harkokin kasuwanci a Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DuniyaLabaraiMinistaVON
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kafafen Yaɗa Labarai Ne Manyan Dirkokin Dimokraɗiyyarmu – Minista

Next Post

Majalisar Dokokin Sokoto Ta Amince Da Bukatar Gwamna Aliyu Na Kafa Jami’an Tsaron Jiha

Related

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya
Labarai

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

9 hours ago
Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025
Labaran Kasuwanci

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

12 hours ago
Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista
Labarai

Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

14 hours ago
Gwamnan Katsina Ya Dakatar Da Ma’aikatan Gidan Gyaran Hali Saboda Azabtar Da Wani Matashi
Labarai

Gwamnan Katsina Ya Dakatar Da Ma’aikatan Gidan Gyaran Hali Saboda Azabtar Da Wani Matashi

16 hours ago
2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu
Manyan Labarai

2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu

17 hours ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
Labarai

Shettima Ya Ziyarci Buhari A Landan Cikin Sirri Don Duba Lafiyarsa

18 hours ago
Next Post
Majalisar Dokokin Sokoto Ta Amince Da Bukatar Gwamna Aliyu Na Kafa Jami’an Tsaron Jiha

Majalisar Dokokin Sokoto Ta Amince Da Bukatar Gwamna Aliyu Na Kafa Jami’an Tsaron Jiha

LABARAI MASU NASABA

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

July 12, 2025
Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

July 12, 2025
Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

July 12, 2025
Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

July 12, 2025
Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

July 12, 2025
Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

July 12, 2025
Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

July 12, 2025
Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

July 12, 2025
Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

July 12, 2025
Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

July 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.