ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kafafen Yaɗa Labarai Ne Manyan Dirkokin Dimokraɗiyyarmu – Minista

by yahuzajere
3 years ago
labarai

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya sake jaddada ƙudirin wannan gwamnati wajen bai wa kafafen yaɗa labarai ‘yancin su, ba tare da takunkumi ko dabaibayi ba.

Ya ce kafafen yaɗa labarai sun taka muhimmiyar wajen tabbatar da kafuwar turakun dimokiraɗiyyar ƙasar nan, don haka abu ne da ya zama dole a a yi riƙo da kafafen yaɗa labarai saboda tasirin su.

Ministan ya bayyana haka ne a ranar Talata, lokacin da ya karɓi baƙuncin shugabannin Cibiyar Kare Haƙƙin Jaridu da ‘Yan Jarida ta Duniya (IPI), a ƙarƙashin shugaban ta, kuma Babban Editan jaridar Premium Times, Alhaji Musikilu Mojeed.

ADVERTISEMENT

IPI ta kai ziyara ne a ranar Talata, 19 ta Disamba, a ofishin ministan da ke Abuja.

IPI ƙungiya ce ta manyan editocin jaridu na duniya, masu kafafen yaɗa labarai da kuma fitattun ‘yan jarida.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ake Wainar Masara Da Miyar Yaji

Yadda Ake Miyar Margi Da Kifin Tarwad

Babban dalilin kafa ƙungiyar shi ne kare haƙƙin aikin jarida tare da tsayawa kan kare aikin jarida da ‘yan jarida daga dukkan wata barazanar da ka iya tunkarar su.

Ministan ya ƙara nanata matsayar Shugaba Tinubu dangane da ‘yancin kafafen yaɗa labarai, tare da cewa shi kan sa shugaban tsohon ɗan gwagwarmayar kare ‘yancin dimokiraɗiyya ne, don haka ya na da dukkan ruwa da tsaki wajen nuna goyon bayan ‘yancin kafafen yaɗa labarai da ‘yan jarida.

Kuma ya yi alƙawari cewa gwamnatin sa ba za ta taɓa yi wa aikin jarida ƙarfa-ƙarfa ba.

Idris ya ce dimokiraɗiyya a Nijeriya na buƙatar nagartacciyar alƙibla, wadda kuma gwamnati ke neman gudunmawar dukkan masu karsashin ƙara mata nagarta, ciki kuwa har da jaridu, kafafen yaɗa labarai da ‘yan jarida su kan su.

Ya ce yi wa wannan tsari garambawul nauyi ne da ya rataya a wuyan kowa da kowa, a dunƙule.

Daga nan ya yi yabo da jinjina ga shugaban IPI dangane da zaɓen sa da aka yi ya jagoranci cibiyar.

Ya yi kira ga Mojeed da ya yi amfani da ƙwarewar sa ta aikin jarida wajen yi wa IPI kyakkyawan jagoranci.

Tun da farko, sai da Shugaban na IPI, Musikilu Mojeed, ya shaida wa ministan cewa a yanzu ana samun cigaba a farfajiyar kafafen yaɗa labarai, don haka ana yi wa aikin jarida kyakkyawar fata nagari.

Daga nan ya yi kira ga gwamnati da ta tabbatar da kare rayuka da lafiyar ‘yan jarida a duk inda suke aiki.

 

  • Abin Da Ya Sa Nijeriya Ke Durkushewa

Ya kuma tabbatar wa da Idris cewa IPI za ta ba shi goyon baya, musamman kasancewa ya na ɗaya daga cikin membobin farko da su ka kafa cibiyar.

labarai
yahuzajere
+ postsBio
  • yahuzajere
    Da Kujerar Mulki Gara Zaman Lafiyar Kano
  • yahuzajere
    Ya Kamata Amurka Ta San Ana Barin Halal Don Kunya
  • yahuzajere
    Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
  • yahuzajere
    Sin Ta Kaddamar Da Gagarumin Bikin Ba Da Lambobin Yabo Na Kasar Sin

MASU ALAKA

Yadda Ake Wainar Masara Da Miyar Yaji
Girke-Girke

Yadda Ake Wainar Masara Da Miyar Yaji

June 14, 2026
Yadda Ake Miyar Margi Da Kifin Tarwad
Girke-Girke

Yadda Ake Miyar Margi Da Kifin Tarwad

June 6, 2026
Amfanin Man Kwakwa Guda 12
Girke-Girke

Amfanin Man Kwakwa Guda 11

May 17, 2026
Next Post
Kiran Minista Ga VON: Ku Yaɗa Kyawawan Labarun Nijeriya Ga Duniya 

Kiran Minista Ga VON: Ku Yaɗa Kyawawan Labarun Nijeriya Ga Duniya 

LABARAI MASU NASABA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.