ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kafafen Yaɗa Labarai Ne Manyan Dirkokin Dimokraɗiyyarmu – Minista

by yahuzajere
2 years ago
labarai

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya sake jaddada ƙudirin wannan gwamnati wajen bai wa kafafen yaɗa labarai ‘yancin su, ba tare da takunkumi ko dabaibayi ba.

Ya ce kafafen yaɗa labarai sun taka muhimmiyar wajen tabbatar da kafuwar turakun dimokiraɗiyyar ƙasar nan, don haka abu ne da ya zama dole a a yi riƙo da kafafen yaɗa labarai saboda tasirin su.

Ministan ya bayyana haka ne a ranar Talata, lokacin da ya karɓi baƙuncin shugabannin Cibiyar Kare Haƙƙin Jaridu da ‘Yan Jarida ta Duniya (IPI), a ƙarƙashin shugaban ta, kuma Babban Editan jaridar Premium Times, Alhaji Musikilu Mojeed.

ADVERTISEMENT

IPI ta kai ziyara ne a ranar Talata, 19 ta Disamba, a ofishin ministan da ke Abuja.

IPI ƙungiya ce ta manyan editocin jaridu na duniya, masu kafafen yaɗa labarai da kuma fitattun ‘yan jarida.

LABARAI MASU NASABA

Amfanin Man Kwakwa Guda 11

Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada

Babban dalilin kafa ƙungiyar shi ne kare haƙƙin aikin jarida tare da tsayawa kan kare aikin jarida da ‘yan jarida daga dukkan wata barazanar da ka iya tunkarar su.

Ministan ya ƙara nanata matsayar Shugaba Tinubu dangane da ‘yancin kafafen yaɗa labarai, tare da cewa shi kan sa shugaban tsohon ɗan gwagwarmayar kare ‘yancin dimokiraɗiyya ne, don haka ya na da dukkan ruwa da tsaki wajen nuna goyon bayan ‘yancin kafafen yaɗa labarai da ‘yan jarida.

Kuma ya yi alƙawari cewa gwamnatin sa ba za ta taɓa yi wa aikin jarida ƙarfa-ƙarfa ba.

Idris ya ce dimokiraɗiyya a Nijeriya na buƙatar nagartacciyar alƙibla, wadda kuma gwamnati ke neman gudunmawar dukkan masu karsashin ƙara mata nagarta, ciki kuwa har da jaridu, kafafen yaɗa labarai da ‘yan jarida su kan su.

Ya ce yi wa wannan tsari garambawul nauyi ne da ya rataya a wuyan kowa da kowa, a dunƙule.

Daga nan ya yi yabo da jinjina ga shugaban IPI dangane da zaɓen sa da aka yi ya jagoranci cibiyar.

Ya yi kira ga Mojeed da ya yi amfani da ƙwarewar sa ta aikin jarida wajen yi wa IPI kyakkyawan jagoranci.

Tun da farko, sai da Shugaban na IPI, Musikilu Mojeed, ya shaida wa ministan cewa a yanzu ana samun cigaba a farfajiyar kafafen yaɗa labarai, don haka ana yi wa aikin jarida kyakkyawar fata nagari.

Daga nan ya yi kira ga gwamnati da ta tabbatar da kare rayuka da lafiyar ‘yan jarida a duk inda suke aiki.

 

  • Abin Da Ya Sa Nijeriya Ke Durkushewa

Ya kuma tabbatar wa da Idris cewa IPI za ta ba shi goyon baya, musamman kasancewa ya na ɗaya daga cikin membobin farko da su ka kafa cibiyar.

labarai
yahuzajere
+ postsBio
  • yahuzajere
    Da Kujerar Mulki Gara Zaman Lafiyar Kano
  • yahuzajere
    Ya Kamata Amurka Ta San Ana Barin Halal Don Kunya
  • yahuzajere
    Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
  • yahuzajere
    Sin Ta Kaddamar Da Gagarumin Bikin Ba Da Lambobin Yabo Na Kasar Sin

MASU ALAKA

Amfanin Man Kwakwa Guda 12
Girke-Girke

Amfanin Man Kwakwa Guda 11

May 17, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Girke-Girke

Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada

May 10, 2026
Yadda Ake Hada Dafadikan Taliya (Jollof Spaghetti)
Girke-Girke

Yadda Ake Hada Dafadikan Taliya (Jollof Spaghetti)

April 25, 2026
Next Post
Kiran Minista Ga VON: Ku Yaɗa Kyawawan Labarun Nijeriya Ga Duniya 

Kiran Minista Ga VON: Ku Yaɗa Kyawawan Labarun Nijeriya Ga Duniya 

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.