• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kisan Gambo Mai Faci A Katsina: Iyalansa Sun Bar Wa Allah, Cewar Hisba

by El-Zaharadeen Umar
12 months ago
in Labarai
0
Kisan Gambo Mai Faci A Katsina: Iyalansa Sun Bar Wa Allah, Cewar Hisba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babu shakka samamayen da hukumar Hisba ta kai unguwar Kwanar Danbukari a ranar Lahadi, 5 ga Mayun 2024,  a cikin birnin Katsina da zummar tayar da masu kidan DJ da aka gayyoto a wajen wani ya haifar da zazafar mahawara, musamman a kafafen yada zumunta na zamani.

Wannan farmaki da hukumar Hisba ta kai ya yi sanadiyar rasa ran, Malam gambo Mai Faci, wanda aka yi zargin harsashi ne ya taba shi lokacin da jami’an C-Watch da suka rako hukumar Hisba domin tarwatsa DJ da kuma kamashi idan an samu sa’a.

  • Jami’ar FUBK Ta Gudanar Da Bikin Ɗaukar Sabbin Ɗalibai 2, 217 A Kebbi
  • Hajjin Bana: Saudiyya Ta Kaddamar Da Kundayen Wayar Da Kai Ga Mahajjata Cikin Harsuna 16 Har Da Hausa

Ana iya cewa, wannan dai shi ne karon farko da ita wannan hukuma da Gwammna Malam Dikko Umar Radda ya kafa bayan hawansa mulki, da ta kai farmaki irin haka kuma har aka samu asarar rai guda daya tare da jikkata wasu da dama.

Jama’a da dama dai sun yi tofin Allah wadai ga ayyukan wannan hukuma da take cewa ita aikin Allah take yi, sai gashi ta fara aikin nata da kashe dattawa da kuma raunata bayin Allah saboda masu DJ.

Wasu rahotanni sun tabbatar da cewa an shirya yin zanga-zanga a ranar Juma’ar da Malam Gambo ya rasu, don nuna fushi da kin amincewa da abin da hukumar Hisba ta yi, sai dai batun ya gamu da cikas bayan da wasu dattawan suka ce a bar wa Allah komi.

Labarai Masu Nasaba

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

Kamar yadda shaidun gani da ido suka bayyana cewa, a ranar Lahadin aka yi biki a unguwar Kwanar Danbukari, wanda ana  ciki shagalin biki sai ga jami’an hukumar Hisba sun zo domin hana wannan biki, sakamakon haka hatsaniya ta tashi, kuma jami’an C-Watch da suka rako Hisba suka yi harbi.

Baba shakka wannan harbi ya bar baya da kura, mausaman yadda ake yada labaran cewa hukumar Hisba ta yi harbi, jama’a da dama sun yi mamaki yadda za a ce hukumar irin ta Hisba ta yi amfani da bindiga wajen tarwatsa taro mai makon yin nasiha da lalama kamar yadda suke ambatawa cewa, Hisba aikin Allah take.

Bayan wannan harbi da aka yi, Malam Gambo wanda aka ce yana sana’ar faci a kusa da inda wannan lamari ya afku, an garzaya da shi zuwa asibitin koyarwa ta Jihar Katsina domin yi masa magani, kuma a iya zaman sa a can kafin Allah ya dauki ransa hukumar Hisba ce ta dauki nauyin yi masa magani.

Wani abu ya fusata jama’a shi ne, yadda kafafen sada zumunta na zamani suka ruwaito wani mutun da aka ce shi ne jami’in hulda da jama’a na hukumar Hisba na cewa ba harbin Malam Gambo aka yi ba, duwatsu ne da jama’a suka rika jefawa a lokacin yamutsin ya same.

Ko shakka babu hakan bai yi wa jama’a da dama dadi ba, musamman iyalansa da ‘yan’uwa da kuma abokan arziki, sannan lokacin da Allah ya yi masa rasuwa ba a ga shugaban hukumar Hisba ba a wajen jana’iza da kuma gaisuwa, wanda hakan tasa jama’a ke cewa ya kamata a bi kadin wannan bayan Allah domin ganin an bi masa hakkinsa na kisan da aka yi masa babu hakki.

Daga Bangaran Hukumar Hisba Ta Katsina

Bayan wadannan zarge-zarge da kuma maganganu da jama’a ke yi, wakilinmu a Jihar Katsina ya samu tattaunawa da baban Kwamadan Hukumar Hisba na Jihar Katsina, Dakta Aminu Usman (Abu Ammar) domin jin ta bakinsa da kuma matsayarsa kan wannan lamari.

Dakta Usman ya fara da yin ta’aziya ga iyalan marigayi Malam Gambo da ‘yan’uwa da mutanen Jihar Katsina, inda ya yi addu’ar Allah ya jikansa ya karbi bakuncinsa ya sanya wannan al’amari ya zame masa sanadiyar shiga Aljanna.

Haka kuma ya yi tambihi kan wadanda suka rika yin rubuce-rubuce lokacin faruwar wannan al’amari. Ya ce da yawa daga cikin mutane ba su fadin gaskiyar abin da ya faru, suna fadin san zuciyarsu domin cimma wata manufa tasu.

“Hukumar Hisba ba ta rike makami, doka ba ta ba mu iznin rike bindaga ba, hatta hotan wani dan hisba da ake yadawa rike da bindiga a kafafen sadarwa na zamani, ba da izninmu ya yi hotan ba, kuma shi ma ya tabbatar, sannan yanzu haka mun dauki mataki kansa,” in ji shi.

Dakta Aminu ya fadi yadda abin ya faru, inda ya ce suna zaune a ofis wani mutun daga unguwar Kwanar Danbukari ya buga masa waya cewa gashi ana DJ kuma jama’ar unguwar ba sa so, amma yaran sun ki tashi, saboda haka ya turo ‘yan hisba su tashe su.

Ya kara da cewa umarnin da ya ba da na idan za a tafi wannan samame a tafi da jami’an C-Wacth, saboda shirin da aka ce masu DJ sun yi. Ya ce kadda a harbi kowa idan an samu turjiya a harba bindaga sama, sannan a kwaso kayan DJ idan an samu mai DJ din a kamo shi, wannan shi ne umarnin da ya ba da.

Sai dai har yanzu Dakta Aminu bai amince cewa harbin da aka yi wa Malam Gambo ne ya yi sanadiyar mutuwarsa ba, yana mai cewa binciken likita ya tabbatar da cewa ba a harbi Malam Gambo ba, jifa ce ta same shi, ba harbin bindiga ba kamar yadda ake yadawa.

A cewarsa, tun daga lokacin da wannan al’amari ya faru gwamnatin Jihar Katsina ta hannun hukumar Hisba ne suke daukar nauyin yi masa magani, kuma ko bayan Allah ya yi masa rasuwa sun kai kayan abinci gidansa tare da wasu kudade domin yin cefane.

Dakta Aminu ya ce abin da ya hana su zuwa ta’aziyya da kuma jana’iza shi ne, jama’an tsaro suka ba da shawara cewa kadda su je domin yadda jama’a suka fusata da hukumar Hisba, domin wani abu na iya faruwa idan suka je a daidai wannan lokaci.

Sai dai ya ce bayan abubuwa sun lafa, sun samu ganawa da iyalan mamacin, inda suka bayyana cewa sun yafe, sun bar wa Allah ba sa neman diyya a wajan gwamnati.

Ya ce wannan dalilin ya sa Gwamna Radda ya yi alkawarin bai wa ‘ya‘yan Malam Gambo guda biya aikin gwamnati tun da sun yi karatu, sannan akwai mace wanda za a ba ta jari domin yin sana’a.

Haka kuma ya nuna takaicinsa kan irin yadda wasu mutane suka rika amfani da wannan damar wajen ruruta wutar al’amari maimakon kamawa a kashe ta, yana mai cewa babu shakka a sanadiyar kai wannan farmaki da hukumar Hisba ta yi ne ya yi sanadiyar rasuwa Malam Gambo, saboda komai yi riga ya faru, kuma ya yi alkawarin cewa haka ba za ta sake faruwa a wannan hukuma tasu ba.

“Sai dai ina mai shaida wa al’umma cewa ba wai aikin Hisba ya zo karshe bane, maganar tsaftace al’umma a Jihar Katsina yanzu aka fara, saboda haka yana sanar da jama’a su ji tsoron Allah su bar duk abin da Allah ya hana domin ta haka ne za su samu fahimtar juna da jama’a. Ina rokon Allah ya kare faruwar haka a nan gaba”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HisbahKisaMai Faci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Sin Da Rasha Suke Mu’amala Da Juna Ya Samar Da Kwanciyar Hankali A Duniya

Next Post

Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Alƙawarin Tallafawa Gidan Rediyon EFCC

Related

Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

1 hour ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

2 hours ago
UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

10 hours ago
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista
Labarai

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

11 hours ago
gaza
Labarai

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

12 hours ago
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa
Labarai

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

14 hours ago
Next Post
Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Alƙawarin Tallafawa Gidan Rediyon EFCC

Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Alƙawarin Tallafawa Gidan Rediyon EFCC

LABARAI MASU NASABA

Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.