• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kisan Gillar Basaraken Daular Gobir A Hannun Masu Garkuwa Ta Girgiza Al’umma

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto, Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
10 months ago
in Labarai
0
Ɗan Sarkin Gobir Da Aka Kashe Ya Kuɓuta Daga Hannun ‘Yan Bindiga
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kisan gillar babban basarake Daular Gobir, Sarkin Kudun Gatawa, Alhaji Muhammad Bawa a hannun ‘yan bindiga, ta yi matukar girgiza al’ummar jihar Sakkwato wadanda rasuwarsa a hannun ‘yan bindigar ta zo masu a- ba- zata a yayin da suke tsammamin dawowarsa a cikin iyali lafiya.

 

A yayin da al’ummar Sakkwato suke jimami da jajantawa kan faruwar mummunan al’amarin tare da dora alhakin hakan ga gwamnati haka ma bayanai daga masarautar Gobir da Gabashin Sakkwato ya nuna al’amurra sun tsaya cik!

  • Yadda Ambaliya Ta Lalata Gidaje 255 A Garin Natsinta Da Ke Katsina
  • Gwamnatin Kano Za Ta Tsara Zamantar Da Magungunan Gargajiya

Al’umma sun shiga cikin kunci da takaicin yadda basaraken wanda aka shaida da gudanar da mulkin gaskiya da adalci ya rasa ransa a hannun ‘yan bindigar duk kuwa da ikirarin da Gwamna Ahmed Aliyu ya yi a yayin yekuwar neman zabe cewa, idan duka kudin jihar Sakkwato za su kare sai gwamnatinsa ta samar da ingantaccen tsaro a Gabashin Sakkwato.

 

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

A cikin bidiyon da aka saki a karshen mako, an ga basaraken cikin yanayi na tashin hankali, sanye da tufafin da suka jike da jini kuma daure da sarkoki, yana rokon gwamnatin da ya ce ya hidimta mata tsawon shekara 45 ta taimaka masa a wannan mawuyacin hali.

 

Dangane da lamarin, wani dan Majalisar Dokoki ta Jihar Sakkwato, Honarabul Aminu Boza, ya tabbatar da cewa mutumin da ke cikin bidiyon shi ne basaraken da aka sace.
Iyalin Sarkin sun nuna damuwa da takaici kan yadda suka sanar da hukuma, amma ba a sami cikakkiyar kulawa ba. Sun bayyana cewa duk da kokarin tattaunawa da masu garkuwar da suka yi, wadanda suka sace shi sun nace sai gwamnati ta shiga lamarin kafin a sako shi.

 

A hirarsa da BBC, Shuaibu Gwanda Gobir, wanda shi ne magajin garin na Gobir kuma daya daga cikin masu nadin sarki, ya ce labari ya ishe su cewa masu garkuwar sun kashe sarkin ne a ranar Talata.

 

“Labarin da na samu shi ne ‘yan bindigar sun harbe shi ne tun a jiya Talata bayan la’asar, kuma wadanda suka je tattauna biyan kudin fansa ne suka ga gawar sarkin a kwance,” in ji shi.

 

Ya kara da cewa zuwa lokacin da aka yi magana da shi ba su karbi gawar mai martaban ba tukunna.

 

Kazalika, ya ce akwai dan sarkin mai suna Kabiru da aka yi garkuwa da su tare, kuma abin da suka saka a gaba kenan yanzu.
Magajin garin ya ce: “A ranar Talata da safe an kira shugaban masu garkuwar har ma yana tambaya game da kudin fansa. Da aka nemi a yi magana da sarkin sai ya ce yana can yana jin dumi a gefen wuta.

 

“Da aka yi magana da Kabiru ya tabbatar da cewa sarki na can yana jin dumi, amma ya yi ta rokon a biya kudin fansa domin kubutar da su.”

 

Wani dan sarkin na Gobir ya ce an yi wa mahaifin nasa kwanton-bauna ne a yankin Kwanar Maharba yayin da yake komawa gida.

 

“‘Yan bindigar sun fara harbi kan mai uwa da wabi lokacin da suka hangi motar mahaifin namu, abin da kuma ya janyo fashewar tayoyin motar da karkatar da hankalin direbansa har ta kai ya tsaya,” in ji dan sarkin.

 

Majiyoyi daga Sabon Birni sun ce an yi garkuwa da karin mutum biyar a yankin a ranar da aka sace sarkin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsaro: Gwamnatin Tinubu Ta Kashe Naira Tiriliyan 3.2 A Shekara Daya

Next Post

Dalilai 5 Da Suka Sa ASUU Barazanar Sake Tsunduma Yajin Aiki

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

2 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

5 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

6 hours ago
Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

15 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

17 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

18 hours ago
Next Post
ASUU

Dalilai 5 Da Suka Sa ASUU Barazanar Sake Tsunduma Yajin Aiki

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.