• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kisan Mummuken Cutar Mashako A Nijeriya Da Sassan Duniya

by Leadership Hausa
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Kisan Mummuken Cutar Mashako A Nijeriya Da Sassan Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A tsakiyar Nijeriya, ana fuskantar wata cutar mai kisa ba tare da bata lokaci ba, cutar kuwa ita ce, cutar mashako, wadda ke bazuwa kamar wutar daji a wasu jihohin Arewacin Nijeriya da suka hada da Borno, Bauchi da kuma Kano.

Tuni kungiyar nan ta Likitoci ta ‘Médecins Sans Frontières (MSF)’ ta ankarar da al’umma tare da bayar da rahoton cewa, dubban yara sun mutu daruruwa ta kuma rasa rayukansu sakamakon cutar.

  • CISA: Masana’antun Sarrafa Karfe Na Tafiya Cikin Yanayi Mai Karko Tsakanin Watan Janairu Zuwa Na Agusta
  • Babu Wata Yarjejeniya Tsakaninmu Da Gwamnatin Tarayya Kan Dakatar Da Yajin Aiki – NLC

A ra’ayinmu, wannan babbar matsala ce da ke bukatar a gaggauta daukar matakin kawo karshen cutar a matakin kasa da ma duniya baki daya.

Da farko, mun yi tunanin cewa, cutar Mashako, wata cuta ce da aka manta da ita, aka barta a kundin tarihi da ke littatafai, godiya ga shirin rigakafi da aka yi a fadin duniya a shekarun baya. Amma kuma bayyanar ta a ‘yan shekarun nan ya nuna mana bukatar a kara daukar mataki na kariya ga al’ummar mu.

Tawagar Likitocin kungiyar MSF ta bayyana cewa, sun tabbatar da yi wa mutum 6,700 maganin cutar, a yayin da aka tabbatar da barkewar cutar a Kano, an kuma samu bullar cutar har sau 110 a Jihar Borno, a Jihar Bauchi kuma an samu mutum 21 da suka kamu ana kuma ci gaba da sa ido a kan sassan Nijeriya don kare yaduwarta.

Labarai Masu Nasaba

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

Ba zamu manta da bayanin da ke nuna cewa, an samu mutun fiye da 4,000 da suka kamu da cutar a fadin duniya. Wannan kididdigar tana tayar da hankula, tana kuma nuna bukatar a gaggauta daukar mataki don kada abin ya zama annoba.

Cutar na samun karuwar yaduwa ne saboda wasu dalilai masu yawa da suka hada da karancin rigakafi abin da ya sa al’umma da dama suka zama cutar na iya kama su duk kuwa da cewa, cutar aba ce da za a iya daukar matakin kariya daga gareta. Haka kuma karancin maganin rigakafin mai suna ‘Antitodin’ yana kara sanya cutar ta zama abar fargaba ga duk wani mai kishin kasa, wannan kuma shi ne yake kara wahalar da ake fuskanta sakamakon cutar da kuma mace-macen da ake yi.

A ta bakin wani Likita daga kungiyar MSF mai suna Dakta Hashim Juma Omar, lamarin nada tayar da hankali musamman a Jihar Kano. Don kuwa fiye da mutum 700 masu dauke da cutar Mashako na neman magani yayin da ake kwantar da mutum fiye 280 a duk mako sakamakon cutar a cibiyoyi biyu na masu fama da cutar da ke Kano.

Haka kuma Gidauniyar Yara ta Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) ta bayyana cewa, Jihar Kano ne ke da kashi 80 na masu dauke da cutar Mashako a Nijeriya.

Wadanda cutar ta fi kamawa sun hada da mata da yara kanana masu shekaru kasa da biyar a duniya, sune cutar ta fi farmaka.

Da farko ya kamata kasashen duniya su hada kai da Nijeriya ta hanyar kawo mata gudummawa don yaki da cutar, ya kuma kamata a kawo karshen karancin maganin rigakafin, a kuma tabbatar da an samar da isassun magunguna a sassan Duniya.

A ra’ayinmu, wannan ba wai maganar kamar ana taimakon Nijeriya ba ne, al’amari ne da ya shafi lafiyar duniya gaba daya. Cutar ba Ruwan ta da iyaykokin kasa da kasa, in har ba a dauki matakin da ya kamata ba, za ta iya zama wata matsala da barazana da lafiyar duniya.

Bugu da kari kuma, dole ne Nijeriya ta kara kaimi wajen gudanar da rigakafi ga al’umma, a tattabatar da kowanne yaro ya samu allurar rigakafin cutar Mashako don shi ne hanya mafi sauki ta kariya daga cutar. Ya kamata a zafafa fadakar da al’umma don kawar da camfe-camfen da ake da shi a kan karbar rigakafi, wanda daga dukkan alamu yana kawo cikas ga shirin a wasu yankuna.

Domin tabbatar da kare yaduwar cutar a kwai bukatar daukar matakan ganowa tare da kebe wanda ke dauke da cutar don kare yaduwarsa daga wuri zuwa wuri. Akwai kuma bukatar a samar da issasun magunguna tare da horars da ma’aikatan lafiya a kan hanyoyin da za su fuskanci masu cutar da kare kansu a lokaci daya.

Muna kira ga gwamnatoci da al’ummar duniya da kuma dukkan masu ruwa da tsaki da su hada hannu don kawar da cutar Mashako a Nijeriya, martaninmu mu shi ne zai tabbatar da kariya ga dubban ‘yan Nijeriya a cikin gida dama kasashen waje.

Wannan kuma ya kamata ya zama wani abin da zai farkar da Nijeriya da sauran kasashen duniya na bukatar su karfafa cibiyoyin kiwon lafiyansu, karfafa tsarin rigakafinsu da kuma kara zuba jari wajen samar da asibitoci da cibiyoyin lafiya a yankunan karkara da kuma samar da su a kusa da al’umma don inganta lafiyar al’umma gaba daya.

Camfe-camfe a kan maganin rigakafi yana daga cikin manyan matsalolin da yaki da cutar Mashako ke fuskanta, a kan haka dole a kara kaimi wajen fadakar da al’umma tare da nuna musu cewa, wannan abu ne da ya shafi lafiyarsu dana ‘ya’yansu. Ya kuma kamata a hada da ta shugabannin al’umma kamar masu unguwanni, sarakuna da sauransu.

Abin da ya kamata mu fahimta a nan shi ne, yadda aka samu barkewar cutar mashako a Nijeriya yana nuna mana cewa, wasu cututtuka masu yaduwa da aka manta da su suna iya sake bullowa idan kuma yi sakaci. Dole al’umma duniya su hada hannun don kawo dauki tare da maganin cutar Mashako a kasar nan, wannan lokaci ne na daukar mataki ba sai anjima ba musamman ganin abu ne da ya shafi rayuwar al’ummar duniya baki daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Lakadawa Jarumar TikTok Murja Ibrahim Kunya Duka A Kano

Next Post

Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Asirce: Sa-in-sa Ta Kaure Tsakanin Gwamnatin Tarayya Da Ta Zamfara

Related

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki
Manyan Labarai

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

11 hours ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

13 hours ago
Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su
Manyan Labarai

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

17 hours ago
Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

18 hours ago
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja
Manyan Labarai

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

21 hours ago
Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi
Daga Birnin Sin

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

1 day ago
Next Post
Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Asirce: Sa-in-sa Ta Kaure Tsakanin Gwamnatin Tarayya Da Ta Zamfara

Sulhu Da 'Yan Bindiga A Asirce: Sa-in-sa Ta Kaure Tsakanin Gwamnatin Tarayya Da Ta Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

June 27, 2025
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

June 27, 2025
Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

June 27, 2025
Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

June 27, 2025
Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

June 27, 2025
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

June 27, 2025
Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

June 27, 2025
JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don ÆŠaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don ÆŠaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.