• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Hana Fina-finan Daba Zai Rage Aikata Laifukan Daba A Kano?

by Rabilu Sanusi Bena
1 year ago
in Nishadi
0
Ko Hana Fina-finan Daba Zai Rage Aikata Laifukan Daba A Kano?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar tace fina finai da dab’i ta jahar Kano ta bayyana cewa biyo bayan korafe-korafen da al’umma ke yi a kan shirya fina-finan da ke nuna fadan Daba da harkar Daudu a jihar Kano, shugaban Hukumar tace fina-finai da dab’i ta jihar Kano Abba El-mustapha ya ba da umarnin dakatarwa tare da hana dukkan fina-finan da ke nuna fadan Daba da harkar Daudu a fadin jihar Kano.

Abba El-mustapha ya bayar da wannan umarni jim kadan bayan wata ganawa da ya yi da manyan ma’aikatan Hukumar tace fina-finan na Kano tare da wasu daga cikin wakilan ‘yan masana’antar shirya fina-finan ta Kannywood wanda suka hada da kungiyoyin MOPPAN, AREWA FILMS MAKERS DIRECTORS da kuma PRODUCERS.

  • ‘Yan Ta’adda Sun Yi Yunƙurin Ƙwace Iko Da Sakatariyar Jihar Oyo
  • Cinikayyar Shige Da Fice Ta Sin Ta Daga Da Kaso 5% A Rubu’in Farko Na Bana

Abba ya kara da cewa doka ce ta bawa Hukumar damar dakatarwa ko hana duk wani film da take ganin ya ci karo da tarbiya tare da al’adar al’ummar da ke jihar, a saboda haka tuni lokaci ya shige da za a saka ido irin wannan gurbatattun fina-finai su ci gaba da yaduwa a cikin al’umma.

Abba El-mustapha ya gode wa yan masana’antar shirya fina-finan ta kannywood dangane da hadin Kai da kuma goyan bayan da suke baiwa Hukumar a koda yaushe, daga karshe ya kara  gode wa al’ummar jjhar Kano kan irin hadin kan da suke bawa Hukumar musamman na sanar da ita duk wani abu da suke ganin ya saba da al’ada tare da tarbiyar addinin musulunci.

Abba El-mustapha ya kuma yi alkawarin ci gaba da barin kofar sa a bude domin karbar shawarwari ga duk wadanda suke da bukatar hakan.

Labarai Masu Nasaba

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

A ‘yan kwanakin nan wasu unguwanni da ke Kano suna fama da matsalar karuwar masu aikin daba da sauran miyagun ayyuka,wadanda wasu suka alakanta hakan da yawan kale-kallen fina finan Hausa da ake nuna yadda ake yin daba da fashi da makami da matasa keyi a halin yanzu.

Hakan yasa hukumar tace fina finai da dab’i ta jahar Kano karkashin jagorancin shugabanta Abba El Mustapha ta bayyana matakin dakatar da nuna duk wani shiri dake nuna aikin daba a fadin jahar ta Kano mai tarin al’umma fiye da mutum miliyan 15.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Abubuwan Da Za A Rika Tuna Saratu Gidado Da Su A Fagen Fim

Next Post

HOTUNA: Yadda Sojoji Suka Kama Mutum 9 Da Suka Kai Hari Sakatariyar Oyo

Related

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango
Nishadi

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

14 hours ago
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)
Nishadi

Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

6 days ago
Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba
Nishadi

Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba

2 weeks ago
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah
Nishadi

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

3 weeks ago
Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya
Nishadi

Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya

4 weeks ago
Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu
Nishadi

Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

1 month ago
Next Post
HOTUNA: Yadda Sojoji Suka Kama Mutum 9 Da Suka Kai Hari Sakatariyar Oyo

HOTUNA: Yadda Sojoji Suka Kama Mutum 9 Da Suka Kai Hari Sakatariyar Oyo

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.