• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Kun San Miliyan Nawa Gombe Ke Kashewa Don Tsaftace Jihar A Duk Wata?

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
Gombe

Gwamna Inuwa Yahaya na Jihar Gombe ya bayyana cewa gwamnatin jihar tana kashe Naira miliyan ₦150m kowane wata don kula da tsaftar jihar. Da yake jawabi a yayin ƙaddamar da aikin kwashe sharar manyan magudanan ruwa a shekarar 2024 a cikin birnin Gombe, Gwamna Yahaya ya jaddada ƙudurin gwamnatin na ɗorewar tsaftar muhalli da kuma inganta rayuwar al’umma.

Ya buƙaci mazauna yankin da su tallafa wa ƙoƙarin gwamnati na amfani da sabbin cibiyoyin tattara shara da kaucewa zubar da shara barkatai cikin magudanan ruwa, wanda ke ƙara janyo matsalolin muhalli musamman ambaliyar ruwa.

  • Gwamnan Gombe Ya Gwangwaje Shugabannin Kananan Hukumomi Da Motoci
  • Jihar Gombe Ta Rusa Kamfanin Zuba Jari Da Bunƙasa Ƙadarori

Gwamnan ya bayyana muhimmancin ɗaukar nauyi tare a kula da shara don hana ambaliyar ruwa da illolinta ga rayuka da dukiyoyi. Ya kuma sanar da fara aikin tsaftace manyan magudanan ruwa don tabbatar da kwararar ruwa ba tare da matsala ba, don kaucewa ambaliyar ruwa da kuma kare rayukan jama’a, dukiyoyi da ababen more rayuwa. Ya lura cewa zubar da shara barkatai a cikin magudanan ruwa na daga cikin manyan dalilan da ke janyo ambaliyar ruwa a cikin birnin, sannan ya jaddada muhimmancin ci gaba da wayar da kan al’umma game da illolin irin wannan ɗabi’a.

Gwamna Inuwa ya sake jaddada ƙudurin gwamnatinsa na kiyaye muhalli ta hanyar sarrafa shara da kuma dasa bishiyoyi da yawa a fadin jihar. Haka kuma, ya sanar da gina ƙarin cibiyoyin tattara shara guda 21 ƙarƙashin shirin “Agro-Climatic Resilience in Semi-Arid Landscapes” (ACReSAL), a haɗin gwuiwa da Bankin Duniya.

Hukumar Kula da Muhalli ta Jihar Gombe (GOSEPA) za ta tabbatar da kwashe shara daga waɗannan cibiyoyi a kullum don samar da tsabta da ingantaccan muhalli.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 
Manyan Labarai

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya
Labarai

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Next Post
Gwamnan Kano Ya Kwace Filayen Makarantun Da Ganduje Ya Cefarnar

Gwamnan Kano Ya Kwace Filayen Makarantun Da Ganduje Ya Cefarnar

LABARAI MASU NASABA

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

November 6, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

November 6, 2025
Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

November 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

November 6, 2025
Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.