ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Kun San Miliyan Nawa Gombe Ke Kashewa Don Tsaftace Jihar A Duk Wata?

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
Gombe

Gwamna Inuwa Yahaya na Jihar Gombe ya bayyana cewa gwamnatin jihar tana kashe Naira miliyan ₦150m kowane wata don kula da tsaftar jihar. Da yake jawabi a yayin ƙaddamar da aikin kwashe sharar manyan magudanan ruwa a shekarar 2024 a cikin birnin Gombe, Gwamna Yahaya ya jaddada ƙudurin gwamnatin na ɗorewar tsaftar muhalli da kuma inganta rayuwar al’umma.

Ya buƙaci mazauna yankin da su tallafa wa ƙoƙarin gwamnati na amfani da sabbin cibiyoyin tattara shara da kaucewa zubar da shara barkatai cikin magudanan ruwa, wanda ke ƙara janyo matsalolin muhalli musamman ambaliyar ruwa.

  • Gwamnan Gombe Ya Gwangwaje Shugabannin Kananan Hukumomi Da Motoci
  • Jihar Gombe Ta Rusa Kamfanin Zuba Jari Da Bunƙasa Ƙadarori

Gwamnan ya bayyana muhimmancin ɗaukar nauyi tare a kula da shara don hana ambaliyar ruwa da illolinta ga rayuka da dukiyoyi. Ya kuma sanar da fara aikin tsaftace manyan magudanan ruwa don tabbatar da kwararar ruwa ba tare da matsala ba, don kaucewa ambaliyar ruwa da kuma kare rayukan jama’a, dukiyoyi da ababen more rayuwa. Ya lura cewa zubar da shara barkatai a cikin magudanan ruwa na daga cikin manyan dalilan da ke janyo ambaliyar ruwa a cikin birnin, sannan ya jaddada muhimmancin ci gaba da wayar da kan al’umma game da illolin irin wannan ɗabi’a.

ADVERTISEMENT

Gwamna Inuwa ya sake jaddada ƙudurin gwamnatinsa na kiyaye muhalli ta hanyar sarrafa shara da kuma dasa bishiyoyi da yawa a fadin jihar. Haka kuma, ya sanar da gina ƙarin cibiyoyin tattara shara guda 21 ƙarƙashin shirin “Agro-Climatic Resilience in Semi-Arid Landscapes” (ACReSAL), a haɗin gwuiwa da Bankin Duniya.

Hukumar Kula da Muhalli ta Jihar Gombe (GOSEPA) za ta tabbatar da kwashe shara daga waɗannan cibiyoyi a kullum don samar da tsabta da ingantaccan muhalli.

LABARAI MASU NASABA

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4
Manyan Labarai

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna
Labarai

NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

November 13, 2025
Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2
Manyan Labarai

Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2

November 13, 2025
Next Post
Gwamnan Kano Ya Kwace Filayen Makarantun Da Ganduje Ya Cefarnar

Gwamnan Kano Ya Kwace Filayen Makarantun Da Ganduje Ya Cefarnar

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

November 13, 2025
Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

November 13, 2025
Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

November 13, 2025
Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

November 13, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

November 13, 2025
Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

November 13, 2025
Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

November 13, 2025
Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

November 13, 2025
NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

November 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.