• English
  • Business News
Friday, October 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Kun San Miliyan Nawa Gombe Ke Kashewa Don Tsaftace Jihar A Duk Wata?

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
Gombe

Gwamna Inuwa Yahaya na Jihar Gombe ya bayyana cewa gwamnatin jihar tana kashe Naira miliyan ₦150m kowane wata don kula da tsaftar jihar. Da yake jawabi a yayin ƙaddamar da aikin kwashe sharar manyan magudanan ruwa a shekarar 2024 a cikin birnin Gombe, Gwamna Yahaya ya jaddada ƙudurin gwamnatin na ɗorewar tsaftar muhalli da kuma inganta rayuwar al’umma.

Ya buƙaci mazauna yankin da su tallafa wa ƙoƙarin gwamnati na amfani da sabbin cibiyoyin tattara shara da kaucewa zubar da shara barkatai cikin magudanan ruwa, wanda ke ƙara janyo matsalolin muhalli musamman ambaliyar ruwa.

  • Gwamnan Gombe Ya Gwangwaje Shugabannin Kananan Hukumomi Da Motoci
  • Jihar Gombe Ta Rusa Kamfanin Zuba Jari Da Bunƙasa Ƙadarori

Gwamnan ya bayyana muhimmancin ɗaukar nauyi tare a kula da shara don hana ambaliyar ruwa da illolinta ga rayuka da dukiyoyi. Ya kuma sanar da fara aikin tsaftace manyan magudanan ruwa don tabbatar da kwararar ruwa ba tare da matsala ba, don kaucewa ambaliyar ruwa da kuma kare rayukan jama’a, dukiyoyi da ababen more rayuwa. Ya lura cewa zubar da shara barkatai a cikin magudanan ruwa na daga cikin manyan dalilan da ke janyo ambaliyar ruwa a cikin birnin, sannan ya jaddada muhimmancin ci gaba da wayar da kan al’umma game da illolin irin wannan ɗabi’a.

Gwamna Inuwa ya sake jaddada ƙudurin gwamnatinsa na kiyaye muhalli ta hanyar sarrafa shara da kuma dasa bishiyoyi da yawa a fadin jihar. Haka kuma, ya sanar da gina ƙarin cibiyoyin tattara shara guda 21 ƙarƙashin shirin “Agro-Climatic Resilience in Semi-Arid Landscapes” (ACReSAL), a haɗin gwuiwa da Bankin Duniya.

Hukumar Kula da Muhalli ta Jihar Gombe (GOSEPA) za ta tabbatar da kwashe shara daga waɗannan cibiyoyi a kullum don samar da tsabta da ingantaccan muhalli.

LABARAI MASU NASABA

Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Nnamdi Kanu Ya Sake Bayyana A Kotu Ba Tare Da Lauya Ba, Zai Kare Kansa Da Kansa

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

October 24, 2025
Nnamdi Kanu Ya Sake Bayyana A Kotu Ba Tare Da Lauya Ba, Zai Kare Kansa Da Kansa
Manyan Labarai

Nnamdi Kanu Ya Sake Bayyana A Kotu Ba Tare Da Lauya Ba, Zai Kare Kansa Da Kansa

October 24, 2025
Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu
Labarai

Ƙungiyoyin Ma’aikatan Jihar Kaduna Sun Yabawa Gwamna Sani Kan Amincewa Da Sabon Albashin  Ma’aikata

October 24, 2025
Next Post
Gwamnan Kano Ya Kwace Filayen Makarantun Da Ganduje Ya Cefarnar

Gwamnan Kano Ya Kwace Filayen Makarantun Da Ganduje Ya Cefarnar

LABARAI MASU NASABA

Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

October 24, 2025
Nnamdi Kanu Ya Sake Bayyana A Kotu Ba Tare Da Lauya Ba, Zai Kare Kansa Da Kansa

Nnamdi Kanu Ya Sake Bayyana A Kotu Ba Tare Da Lauya Ba, Zai Kare Kansa Da Kansa

October 24, 2025
Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu

Ƙungiyoyin Ma’aikatan Jihar Kaduna Sun Yabawa Gwamna Sani Kan Amincewa Da Sabon Albashin  Ma’aikata

October 24, 2025
Ƙarfin Niyyar Manzon Allah (SAW) Da Matakinsa Na Aƙlul A’ala

Ƙarfin Niyyar Manzon Allah (SAW) Da Matakinsa Na Aƙlul A’ala

October 24, 2025
Gobara Ta Tafka Ɓarna A Kasuwar Shuwaki, Ta Ƙona Fiye da Rumfuna 500 A Kano

Gobara Ta Tafka Ɓarna A Kasuwar Shuwaki, Ta Ƙona Fiye da Rumfuna 500 A Kano

October 24, 2025
Gwarzuwar Shekarar 2025 Sanata Oluremi Tinubu

Gwarzuwar Shekarar 2025 Sanata Oluremi Tinubu

October 24, 2025
Dauda Lawal Gwarzon Gwamnan 2025: Ceto Zamfara Domin Ci Gaba

Dauda Lawal Gwarzon Gwamnan 2025: Ceto Zamfara Domin Ci Gaba

October 24, 2025
Buƙatar Daƙile Badaƙalar Amfani Da Takardun Karatun Bogi A Nijeriya

Buƙatar Daƙile Badaƙalar Amfani Da Takardun Karatun Bogi A Nijeriya

October 24, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta

Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta

October 23, 2025
Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa

October 23, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.