ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihar Gombe Ta Rusa Kamfanin Zuba Jari Da Bunƙasa Ƙadarori

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Gombe

Majalisar Zartarwar Jihar Gombe ƙarƙashin jagorancin Gwamna Mahammadu Inuwa Yahaya ta amince da rusa Kamfanin Zuba Jari da Bunƙasa ƙadarori na Jihar Gombe, GIPDC. 

Kwamishinan kuɗi da bunƙasa tattalin arziƙi, Malam Muhammadu Gambo Magaji, ne ya sanar da hakan, yana mai cewa an ɗauki matakin ne don daidaitawa da ƙarfafa hukumomin zuba jari na jihar.

“Bayan nasarar da aka samu a babban taron zuba jari na Gombe na 2022 da kuma burinmu na karɓar baƙuncin wani taron na gaba da za a yi a watan Oktobar bana, tare da ci gaba da riƙe kambunmu na jagora a fagen sauƙaƙa kasuwanci, gwamnati ta ɗauki wani tsari mai inganci na ƙarfafa hukumomin zuba jari da kuma magance kashe-kashen kuɗaɗe ba gaira ba dalili da ma kawo ƙarshen maimaita ayyuka”

ADVERTISEMENT
  • Ƴansandan Gombe Sun Yi Ram Da Ɓarayin Hanyar Jirgin Ƙasa
  • ‘Yansanda Sun Cafke Kansila Da Hakimi Kan Zargin Satar Taransifoma A Gombe

Kwamishinan ya ƙara da cewa, “Duba da yadda Kamfanin Zuba Jari da Bunƙasa Kadarorin na Jihar Gombe da Kamfanin Haɓaka Kuɗaɗen Shiga na jihar suke aiki iri ɗaya, majalisar zartarwar ta yanke shawarar rushe kamfanin zuba jari da bunƙasa kadarorin na jiha (GIPDC) da nufin daidaita ayyukansa da rage kashe-kashen kuɗi dama inganta aiki”.

Ya ce za a mayar da ayyukan kamfanin zuwa wasu hukumomin da abin ya shafa, “Kamfanin Haɓaka kuɗaɗen shiga da bunƙasa kadarorin zai koma GROCOL, sannan za a mayar da ɓangaren bunƙasa gidaje ga Ma’aikatar Gidaje ta Jihar Gombe, kuma nan ba da daɗewa ba Gwamna zai naɗa shugabannin da za su jagoranci hukumar, za a mayar da harkokin kasuwanci da zuba jarin da GIPDC ke da su ga kamfanin Gombe State Security Company Ltd da ya zama kufai”

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Hon. Gambo Magaji ya jaddada cewa matakin ba zai shafi ma’aikatan kamfanin ba ta kowace fuska, yana mai cewa za a sake fasalin hukumar gudanarwar ta yadda za a samu sauƙin gudanar da ayyuka masu inganci.

Gombe
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Nanata Bukatar Karfafa Jingar Kare Ambaliya Yayin Da Ake Kokarin Takaita Aukuwar Ambaliya A Kasar

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Nanata Bukatar Karfafa Jingar Kare Ambaliya Yayin Da Ake Kokarin Takaita Aukuwar Ambaliya A Kasar

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.