• English
  • Business News
Wednesday, September 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Kyautatawa Na Iya Sa Miji Ya Mallaki Matarsa Bisa La’akari Da Halin Mata?

by Rabi'at Sidi Bala
2 years ago
in Taskira
0
Ko Kyautatawa Na Iya Sa Miji Ya Mallaki Matarsa Bisa La’akari Da Halin Mata?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wannan makon mun zo muku da sabon salo, maimakon tattaunawa da Mabiya shafin Taskira, mai karatu da kai za mu yi. Sai ka kalmashe kafa ka gyara zama, mu je zuwa…

Sau tari idan zancen game da zamantakewar da ke tsakanin ma’aurata ya tashi, babban abin da aka fi mayar da hankali a kai shi ne, wace hanya namiji zai zama namiji, har ya mallaki akalar tafiyar da harkokin gidansa a matsayin maigida. Ko kuma wadanne hanyoyi ne mace za ta tsayu da kafafunta har ta mallaki mijinta, ko kuma wadanne hanyoyi ne za ta bi domin ta rike akalar miji har ta rika juya shi son ranta? Sanin irin wadannan kudurorin da galibi suke cikin zukatan ma’auratan ne ya sanya a yayin da aka wanke yarinya domin kai ta daki a matsayin amarya a ke yi musu huduba ta musamman kan yadda za ta zauna tare da mijinta.

Sai dai akwai bambanci wajen gabatar da irin wadannan hudubar. Idan mace ta tashi a gidan gargajiya, ma’ana gidan da aka fi son ta mallaki miji ko kuma ta zama gagarabadau ta yadda ba zai taba iya gindaya mata wasu sharuda na kashin-kansa ba a matsayin maigida, ko kuma kan batun kishiya da sauransu, sai a samu wata wadda za ta yi mata huduba ta musamman cewa, ‘Namiji ba dan goyo bane, don haka kada ta yarda ta bayar da kai bori ya hau.’

Hudubar ba daya ba ce a dayan bangaren. Misali, idan mace ta tashi daga cikin gidan Malamai yayin da za a yi mata hudubar bankwana, a kan fi jaddada mata cewa aure dai ibada ne, sannan a tuna mata cewa ibada kuwa ba a yinta da son rai ko lalaci.

A kuma tabbatar mata muddin tana bukatar tsira a duniya da lahira, to fa tilas ta yi wa miji biyayya dari-bisa-dari matukar bai kauce daga kan turbar shari’ar addinin Musulunci ba.

Labarai Masu Nasaba

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

A nan, ba ina sukar ‘yan gargajiya ba ne, sai dai ina kokarin bayyana wasu daga cikin sirrukan zama tsakanin ma’aurata. Shin me ya sa namiji yake ji a ransa ba zai iya mallakar matarsa ba? Me kuma ya sa wasu matan ba sa la’akari da soyayyar farko da aka dora tafiyar a kai, suke bin wadansu hanyoyin ta bayan gida domin mallakar mazajensu?

Kenan za a yarda da ni idan na ce ma’aurata kan canza halayensu jim kadan bayan an daura musu aure. Idan har haka ne, mene ne musabbabinsu? Wasu manazarta wannan fanni sun tafi a kan cewa ba a samun isasshen lokacin da za a fahimci juna, a kuma fahimci irin tafiyar da ake fatan yi tare kafin a daura aure.

Abin da suke nufi a nan shi ne, akwai gazawa ainun a kowani bangare tsakanin iyayen miji da na matar musamman kan abin da ya shafi ilmi, ilmin kuma kan sha’anin aure.

Duk da cewa ana halartar makarantu, a kan saurari wa’azi daban-daban na zaman aure da sauransu, amma manazartan sun tabbatar cewa abu daya da aka fi yayatawa bangane da aure shi ne, ‘aure Sunnah’ ne, ko kuma a ce, Annabi (SAW) ya ce, ‘ku yi aure ku hayayyafa, domin na yi alfahari da yawanku a ranar gobe Kiyama.’

Shin ana samun lokaci isasshe wajen bayyana ainihin ‘Sunnar’ da ake zance a nan? Ko kuma wace hikima ta sa Manzo (SAW) ya ce ‘Ku hayayyafa domin na yi alfahari da yawanku ranar gobe Kiyama?’ Shin irin haihuwar da ake yi babu tsari, kuma tarbiyya ce Annabi (S) yake nufi? Ko wace iri? Wadannan su ne kadan daga cikin kalubalen da manazartan ke kallo a matsayin gazawar iyaye wajen ilmantar da ‘ya’yansu kafin su kulla auratayya a tsakaninsu.

Wasu kuma suna kallon matsalolin da ke aukuwa jim kadan bayan an yi aure a matsayin son duniya, wanda shi ne jigon wanzuwa cikin garari da bala’i daban-daban. Galibin ma’aurata kan dora akalar tafiyar da zaman aurensu ne kan son duniya musamman a wannan zamani. An wayi gari, hatta a zagayen wadanda ake gani Malamai ne a yau, ba a fi mayar da hankali kan aure domin Allah ba, sai abin da ake kira auren jari.

Shin mene ne auren jari? Me ya sa wasu ke hankoron auran mace domin a dan lasa musu dukiya ko wani abin duniya? A fili yake cewa duk wanda ya hau motar kwadayi, za ta sauke shi ne a tsakiyar tashar wulakanci. Amma duk da haka, abin alfahari ga wasu a ce yau sun auri ‘yar gidan wane ko kuma a ce ‘yarka na auren wani attajiri ko mai akalar mulki a hannu.

Baki dayan nazarin suna yin ishara ne kan abu guda, wato yadda ma’aurata da galibin al’umma ke jahiltar fasalin auren a farkon lokaci. Ko kuma idan aka tashi yin zance bangane da batun aure, sai a yi wa jama’a dabaibayi da cewa aure Sunnah ne. Kuma ba a zurfafa tunani kan mece ce Sunnar? Ba a yin bincike kan dalilan da suka sabbaba har fiyayyen halittun Annabinmu Muhammad (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da tsarkakan iyalan gidansa da Sahabbansa managarta) ya bayyana aure a daya daga cikin manyan dabi’u. Har ya fada cewa, “Aure Sunnata ce duk wanda ya tozarta sunnata, ba ya tare da ni.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba Na Kewar Fadar Shugaban Kasa – Buhari

Next Post

Sharhi: Raunin Jam’iyyun Adawa Da Barazana Ga Dimokuradiyyar Nijeriya

Related

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari
Taskira

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

2 weeks ago
Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi
Taskira

Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

2 months ago
Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu
Taskira

Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

2 months ago
Alfanu Da Rashin Alfanun Tallata Shirin Aure Tun Kafin Lokacin Ya Zo
Taskira

Alfanu Da Rashin Alfanun Tallata Shirin Aure Tun Kafin Lokacin Ya Zo

3 months ago
Taskira

Tsokaci Kan Yadda Wasu Matasa Ke Yin Aure Ba Tare Da Sana’a Ba

4 months ago
Tsokaci Kan Yadda Wasu Matasa Ke Yin Aure Ba Tare Da Sana’a Ba
Taskira

Tsokaci Kan Yadda Wasu Matasa Ke Yin Aure Ba Tare Da Sana’a Ba

4 months ago
Next Post
Sharhi: Raunin Jam’iyyun Adawa Da Barazana Ga Dimokuradiyyar Nijeriya

Sharhi: Raunin Jam’iyyun Adawa Da Barazana Ga Dimokuradiyyar Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

majalisar kasa

Majalisa Ta Bai Wa Minista Sa’o’i 48 Ya Bayyana A Gabanta Kan Hatsarin Jirgin Abuja Zuwa Kaduna

September 10, 2025
Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa

Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa

September 9, 2025
IATF 2025: Zamfara A Shirye Ta Ke Wajen Maraba Da Masu Zuba Jari – Gwamna Lawal 

IATF 2025: Zamfara A Shirye Ta Ke Wajen Maraba Da Masu Zuba Jari – Gwamna Lawal 

September 9, 2025
An Kai Jirgin Ceto Na Farko Na Kasar Sin Yankin Tsakiyar Kasar

An Kai Jirgin Ceto Na Farko Na Kasar Sin Yankin Tsakiyar Kasar

September 9, 2025
Sin Ta Samu Karuwar Kaso 9.9 Na Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje A Bara

Sin Ta Samu Karuwar Kaso 9.9 Na Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje A Bara

September 9, 2025
Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

September 9, 2025
Nazarin CGTN: Cin Gajiyar Damarmaki Tare Da Samun Sakamakon Moriyar Juna Ta Hanyar Yin Komai A Bude

Nazarin CGTN: Cin Gajiyar Damarmaki Tare Da Samun Sakamakon Moriyar Juna Ta Hanyar Yin Komai A Bude

September 9, 2025
Kasar Sin Ta Samar Da Kaso 30 Na Jimillar Kason Ci Gaban Masana’antun Duniya A Tsakanin 2021 Zuwa 2025

Kasar Sin Ta Samar Da Kaso 30 Na Jimillar Kason Ci Gaban Masana’antun Duniya A Tsakanin 2021 Zuwa 2025

September 9, 2025
Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Mutum 9 Da Harsasai 4,264 Da Muggan Makamai A Nasarawa 

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Mutum 9 Da Harsasai 4,264 Da Muggan Makamai A Nasarawa 

September 9, 2025
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Babu Shirin Gaggawa Wajen Fara Aiwatar Da Harajin Kashi 5 Na Man Fetur – Minista

September 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.