• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Kyautatawa Na Iya Sa Miji Ya Mallaki Matarsa Bisa La’akari Da Halin Mata?

by Rabi'at Sidi Bala
1 year ago
in Taskira
0
Ko Kyautatawa Na Iya Sa Miji Ya Mallaki Matarsa Bisa La’akari Da Halin Mata?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wannan makon mun zo muku da sabon salo, maimakon tattaunawa da Mabiya shafin Taskira, mai karatu da kai za mu yi. Sai ka kalmashe kafa ka gyara zama, mu je zuwa…

Sau tari idan zancen game da zamantakewar da ke tsakanin ma’aurata ya tashi, babban abin da aka fi mayar da hankali a kai shi ne, wace hanya namiji zai zama namiji, har ya mallaki akalar tafiyar da harkokin gidansa a matsayin maigida. Ko kuma wadanne hanyoyi ne mace za ta tsayu da kafafunta har ta mallaki mijinta, ko kuma wadanne hanyoyi ne za ta bi domin ta rike akalar miji har ta rika juya shi son ranta? Sanin irin wadannan kudurorin da galibi suke cikin zukatan ma’auratan ne ya sanya a yayin da aka wanke yarinya domin kai ta daki a matsayin amarya a ke yi musu huduba ta musamman kan yadda za ta zauna tare da mijinta.

Sai dai akwai bambanci wajen gabatar da irin wadannan hudubar. Idan mace ta tashi a gidan gargajiya, ma’ana gidan da aka fi son ta mallaki miji ko kuma ta zama gagarabadau ta yadda ba zai taba iya gindaya mata wasu sharuda na kashin-kansa ba a matsayin maigida, ko kuma kan batun kishiya da sauransu, sai a samu wata wadda za ta yi mata huduba ta musamman cewa, ‘Namiji ba dan goyo bane, don haka kada ta yarda ta bayar da kai bori ya hau.’

Hudubar ba daya ba ce a dayan bangaren. Misali, idan mace ta tashi daga cikin gidan Malamai yayin da za a yi mata hudubar bankwana, a kan fi jaddada mata cewa aure dai ibada ne, sannan a tuna mata cewa ibada kuwa ba a yinta da son rai ko lalaci.

A kuma tabbatar mata muddin tana bukatar tsira a duniya da lahira, to fa tilas ta yi wa miji biyayya dari-bisa-dari matukar bai kauce daga kan turbar shari’ar addinin Musulunci ba.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Wasu Mata Ke Gallaza Wa ‘Ya’yansu Domin Bakanta Wa Mazajensu

Shin Ziyarar Bazata Zuwa Gidan Budurwa Daga Saurayi Na Bata Wa ‘Yanmatan Rai?

A nan, ba ina sukar ‘yan gargajiya ba ne, sai dai ina kokarin bayyana wasu daga cikin sirrukan zama tsakanin ma’aurata. Shin me ya sa namiji yake ji a ransa ba zai iya mallakar matarsa ba? Me kuma ya sa wasu matan ba sa la’akari da soyayyar farko da aka dora tafiyar a kai, suke bin wadansu hanyoyin ta bayan gida domin mallakar mazajensu?

Kenan za a yarda da ni idan na ce ma’aurata kan canza halayensu jim kadan bayan an daura musu aure. Idan har haka ne, mene ne musabbabinsu? Wasu manazarta wannan fanni sun tafi a kan cewa ba a samun isasshen lokacin da za a fahimci juna, a kuma fahimci irin tafiyar da ake fatan yi tare kafin a daura aure.

Abin da suke nufi a nan shi ne, akwai gazawa ainun a kowani bangare tsakanin iyayen miji da na matar musamman kan abin da ya shafi ilmi, ilmin kuma kan sha’anin aure.

Duk da cewa ana halartar makarantu, a kan saurari wa’azi daban-daban na zaman aure da sauransu, amma manazartan sun tabbatar cewa abu daya da aka fi yayatawa bangane da aure shi ne, ‘aure Sunnah’ ne, ko kuma a ce, Annabi (SAW) ya ce, ‘ku yi aure ku hayayyafa, domin na yi alfahari da yawanku a ranar gobe Kiyama.’

Shin ana samun lokaci isasshe wajen bayyana ainihin ‘Sunnar’ da ake zance a nan? Ko kuma wace hikima ta sa Manzo (SAW) ya ce ‘Ku hayayyafa domin na yi alfahari da yawanku ranar gobe Kiyama?’ Shin irin haihuwar da ake yi babu tsari, kuma tarbiyya ce Annabi (S) yake nufi? Ko wace iri? Wadannan su ne kadan daga cikin kalubalen da manazartan ke kallo a matsayin gazawar iyaye wajen ilmantar da ‘ya’yansu kafin su kulla auratayya a tsakaninsu.

Wasu kuma suna kallon matsalolin da ke aukuwa jim kadan bayan an yi aure a matsayin son duniya, wanda shi ne jigon wanzuwa cikin garari da bala’i daban-daban. Galibin ma’aurata kan dora akalar tafiyar da zaman aurensu ne kan son duniya musamman a wannan zamani. An wayi gari, hatta a zagayen wadanda ake gani Malamai ne a yau, ba a fi mayar da hankali kan aure domin Allah ba, sai abin da ake kira auren jari.

Shin mene ne auren jari? Me ya sa wasu ke hankoron auran mace domin a dan lasa musu dukiya ko wani abin duniya? A fili yake cewa duk wanda ya hau motar kwadayi, za ta sauke shi ne a tsakiyar tashar wulakanci. Amma duk da haka, abin alfahari ga wasu a ce yau sun auri ‘yar gidan wane ko kuma a ce ‘yarka na auren wani attajiri ko mai akalar mulki a hannu.

Baki dayan nazarin suna yin ishara ne kan abu guda, wato yadda ma’aurata da galibin al’umma ke jahiltar fasalin auren a farkon lokaci. Ko kuma idan aka tashi yin zance bangane da batun aure, sai a yi wa jama’a dabaibayi da cewa aure Sunnah ne. Kuma ba a zurfafa tunani kan mece ce Sunnar? Ba a yin bincike kan dalilan da suka sabbaba har fiyayyen halittun Annabinmu Muhammad (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da tsarkakan iyalan gidansa da Sahabbansa managarta) ya bayyana aure a daya daga cikin manyan dabi’u. Har ya fada cewa, “Aure Sunnata ce duk wanda ya tozarta sunnata, ba ya tare da ni.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba Na Kewar Fadar Shugaban Kasa – Buhari

Next Post

Sharhi: Raunin Jam’iyyun Adawa Da Barazana Ga Dimokuradiyyar Nijeriya

Related

Yadda Wasu Mata Ke Gallaza Wa ‘Ya’yansu Domin Bakanta Wa Mazajensu
Taskira

Yadda Wasu Mata Ke Gallaza Wa ‘Ya’yansu Domin Bakanta Wa Mazajensu

2 weeks ago
Shin Ziyarar Bazata Zuwa Gidan Budurwa Daga Saurayi Na Bata Wa ‘Yanmatan Rai?
Taskira

Shin Ziyarar Bazata Zuwa Gidan Budurwa Daga Saurayi Na Bata Wa ‘Yanmatan Rai?

4 weeks ago
Yadda Rashin Ilimi Ke Cutar Da Rayuwar Al’umma
Taskira

Yadda Rashin Ilimi Ke Cutar Da Rayuwar Al’umma

1 month ago
Mece Ce Makomar ‘Ramadan Basket’ A Wannan Lokaci Na Matsin Tattalin Arziki?
Taskira

Mece Ce Makomar ‘Ramadan Basket’ A Wannan Lokaci Na Matsin Tattalin Arziki?

3 months ago
Me Ya Sa Wasu Yaran Ba Sa Jin Maganar Iyayensu?
Taskira

Me Ya Sa Wasu Yaran Ba Sa Jin Maganar Iyayensu?

4 months ago
Me Ke Sa Mata Gallaza Wa Yaran Da Aka Bar Musu Amana?
Taskira

Me Ke Sa Mata Gallaza Wa Yaran Da Aka Bar Musu Amana?

4 months ago
Next Post
Sharhi: Raunin Jam’iyyun Adawa Da Barazana Ga Dimokuradiyyar Nijeriya

Sharhi: Raunin Jam’iyyun Adawa Da Barazana Ga Dimokuradiyyar Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

May 15, 2025
Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

May 15, 2025
Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

May 15, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisar Wakilai Za Ta Binciki Yadda Aka Samu Mummunan Sakamakon Jarabawar UTME 2025

May 15, 2025
Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

May 15, 2025
An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

May 15, 2025
HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

May 15, 2025
Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

May 15, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

May 15, 2025
Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.