• English
  • Business News
Friday, October 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Kyautatawa Na Iya Sa Miji Ya Mallaki Matarsa Bisa La’akari Da Halin Mata?

by Rabi'at Sidi Bala
2 years ago
Matarsa

A wannan makon mun zo muku da sabon salo, maimakon tattaunawa da Mabiya shafin Taskira, mai karatu da kai za mu yi. Sai ka kalmashe kafa ka gyara zama, mu je zuwa…

Sau tari idan zancen game da zamantakewar da ke tsakanin ma’aurata ya tashi, babban abin da aka fi mayar da hankali a kai shi ne, wace hanya namiji zai zama namiji, har ya mallaki akalar tafiyar da harkokin gidansa a matsayin maigida. Ko kuma wadanne hanyoyi ne mace za ta tsayu da kafafunta har ta mallaki mijinta, ko kuma wadanne hanyoyi ne za ta bi domin ta rike akalar miji har ta rika juya shi son ranta? Sanin irin wadannan kudurorin da galibi suke cikin zukatan ma’auratan ne ya sanya a yayin da aka wanke yarinya domin kai ta daki a matsayin amarya a ke yi musu huduba ta musamman kan yadda za ta zauna tare da mijinta.

Sai dai akwai bambanci wajen gabatar da irin wadannan hudubar. Idan mace ta tashi a gidan gargajiya, ma’ana gidan da aka fi son ta mallaki miji ko kuma ta zama gagarabadau ta yadda ba zai taba iya gindaya mata wasu sharuda na kashin-kansa ba a matsayin maigida, ko kuma kan batun kishiya da sauransu, sai a samu wata wadda za ta yi mata huduba ta musamman cewa, ‘Namiji ba dan goyo bane, don haka kada ta yarda ta bayar da kai bori ya hau.’

Hudubar ba daya ba ce a dayan bangaren. Misali, idan mace ta tashi daga cikin gidan Malamai yayin da za a yi mata hudubar bankwana, a kan fi jaddada mata cewa aure dai ibada ne, sannan a tuna mata cewa ibada kuwa ba a yinta da son rai ko lalaci.

A kuma tabbatar mata muddin tana bukatar tsira a duniya da lahira, to fa tilas ta yi wa miji biyayya dari-bisa-dari matukar bai kauce daga kan turbar shari’ar addinin Musulunci ba.

LABARAI MASU NASABA

Tsokaci A Kan Mata Masu Tsananin Kishi

Illolin Da Ke Tattare Da Mallaka Wa Kananan Yara Wayar Hannu

A nan, ba ina sukar ‘yan gargajiya ba ne, sai dai ina kokarin bayyana wasu daga cikin sirrukan zama tsakanin ma’aurata. Shin me ya sa namiji yake ji a ransa ba zai iya mallakar matarsa ba? Me kuma ya sa wasu matan ba sa la’akari da soyayyar farko da aka dora tafiyar a kai, suke bin wadansu hanyoyin ta bayan gida domin mallakar mazajensu?

Kenan za a yarda da ni idan na ce ma’aurata kan canza halayensu jim kadan bayan an daura musu aure. Idan har haka ne, mene ne musabbabinsu? Wasu manazarta wannan fanni sun tafi a kan cewa ba a samun isasshen lokacin da za a fahimci juna, a kuma fahimci irin tafiyar da ake fatan yi tare kafin a daura aure.

Abin da suke nufi a nan shi ne, akwai gazawa ainun a kowani bangare tsakanin iyayen miji da na matar musamman kan abin da ya shafi ilmi, ilmin kuma kan sha’anin aure.

Duk da cewa ana halartar makarantu, a kan saurari wa’azi daban-daban na zaman aure da sauransu, amma manazartan sun tabbatar cewa abu daya da aka fi yayatawa bangane da aure shi ne, ‘aure Sunnah’ ne, ko kuma a ce, Annabi (SAW) ya ce, ‘ku yi aure ku hayayyafa, domin na yi alfahari da yawanku a ranar gobe Kiyama.’

Shin ana samun lokaci isasshe wajen bayyana ainihin ‘Sunnar’ da ake zance a nan? Ko kuma wace hikima ta sa Manzo (SAW) ya ce ‘Ku hayayyafa domin na yi alfahari da yawanku ranar gobe Kiyama?’ Shin irin haihuwar da ake yi babu tsari, kuma tarbiyya ce Annabi (S) yake nufi? Ko wace iri? Wadannan su ne kadan daga cikin kalubalen da manazartan ke kallo a matsayin gazawar iyaye wajen ilmantar da ‘ya’yansu kafin su kulla auratayya a tsakaninsu.

Wasu kuma suna kallon matsalolin da ke aukuwa jim kadan bayan an yi aure a matsayin son duniya, wanda shi ne jigon wanzuwa cikin garari da bala’i daban-daban. Galibin ma’aurata kan dora akalar tafiyar da zaman aurensu ne kan son duniya musamman a wannan zamani. An wayi gari, hatta a zagayen wadanda ake gani Malamai ne a yau, ba a fi mayar da hankali kan aure domin Allah ba, sai abin da ake kira auren jari.

Shin mene ne auren jari? Me ya sa wasu ke hankoron auran mace domin a dan lasa musu dukiya ko wani abin duniya? A fili yake cewa duk wanda ya hau motar kwadayi, za ta sauke shi ne a tsakiyar tashar wulakanci. Amma duk da haka, abin alfahari ga wasu a ce yau sun auri ‘yar gidan wane ko kuma a ce ‘yarka na auren wani attajiri ko mai akalar mulki a hannu.

Baki dayan nazarin suna yin ishara ne kan abu guda, wato yadda ma’aurata da galibin al’umma ke jahiltar fasalin auren a farkon lokaci. Ko kuma idan aka tashi yin zance bangane da batun aure, sai a yi wa jama’a dabaibayi da cewa aure Sunnah ne. Kuma ba a zurfafa tunani kan mece ce Sunnar? Ba a yin bincike kan dalilan da suka sabbaba har fiyayyen halittun Annabinmu Muhammad (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da tsarkakan iyalan gidansa da Sahabbansa managarta) ya bayyana aure a daya daga cikin manyan dabi’u. Har ya fada cewa, “Aure Sunnata ce duk wanda ya tozarta sunnata, ba ya tare da ni.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kishi
Taskira

Tsokaci A Kan Mata Masu Tsananin Kishi

October 12, 2025
Illolin Da Ke Tattare Da Mallaka Wa Kananan Yara Wayar Hannu
Taskira

Illolin Da Ke Tattare Da Mallaka Wa Kananan Yara Wayar Hannu

October 4, 2025
Bukatar Mutane Su Kula Da Warin Jikinsu
Taskira

Bukatar Mutane Su Kula Da Warin Jikinsu

September 27, 2025
Next Post
Sharhi: Raunin Jam’iyyun Adawa Da Barazana Ga Dimokuradiyyar Nijeriya

Sharhi: Raunin Jam’iyyun Adawa Da Barazana Ga Dimokuradiyyar Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

October 17, 2025
Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

October 17, 2025
Abduljabbar

Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja

October 17, 2025
An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

October 17, 2025
Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

October 17, 2025
Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki

Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki

October 17, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Gwamnatin Kano Ta Kai Ƙarar Ganduje Da Wasu Kotu Kan Zargin Almundahanar N4.4bn

October 17, 2025
Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
Ma’aikatar Kasuwanci Ta Kasar Sin: Sin Za Ta Kyautata Matakan Takaita Fitar Da Ma’adanan Farin Karfe Na Rare Earth

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Kasar Sin: Sin Za Ta Kyautata Matakan Takaita Fitar Da Ma’adanan Farin Karfe Na Rare Earth

October 17, 2025
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Zan Tabbatar Ana Tafiyar Da Ayyuka A Tashoshin Jiragen Ruwa A Afrika Ta Yamma —Dantsoho

October 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.