ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi: Raunin Jam’iyyun Adawa Da Barazana Ga Dimokuradiyyar Nijeriya

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Adawa

Daya daga cikin babbar barazana ga Dimokuradiyyar ita ce, raunin jam’iyyun adawa, wanda mutane da dama na ganin hakan zai sa kasar ta kama tsarin jam’iyya guda daya.

A cikin tsarin mulkin dimokuradiyya, ‘yan adawa na matukar taka muhimmiyar rawa wajen kalubalantar gwamnati ta yadda za a gyara tsarin da bai yi daidai da tsarin mulkin dimokuradiyya ba. Ko da gwamnati ba ta yi amfani da kiraye-kirayen ‘yan adawa wajen gyara kuskure, tana amfana da su wajen gudanar da bincike a kan korafin da suka gabatar ta yadda za a samu damar yin gyara.

  • Kano: Kotun Daukaka Kara Ta Bukace Lauyoyin Su Mayar Da Kwafin Takardun Shari’ar
  • Xi Jinping Ya Gana Da Takwaransa Na Uruguay

Tsarin mulki na shugabancin kasa ya kawo ka’idoji ta yadda jam’iyyun adawa za su iya gudanar da bincike wajen gudanar da harkokin gwamnati.

ADVERTISEMENT

A ko da yaushe, jam’iyyar adawa na sa jam’iyya mai mulki ta tashi tsaye wajen gudanar da tsare-tsare da kuma shirye-shiryenta. Haka nan kuma suna dakile wuce gona da iri da muguwar mulkin kama-karya.

A jamhuriya ta daya da ta biyu, Nijeriya tana da al’adar gudanar da siyasar adawa. Marigayi Cif Obafemi Awolowo na jam’iyyar ‘Action Group’ (AG), wanda daga ta koma jam’iyyar ‘Unity Party of Nigeria’ (UPN), a matsayinsa na dan adawa, ya tunkari gwamnatin da ke kan karagar mulki da hujjoji masu tsauri da alkaluma ta yadda za a ceto Nijeriya. Hatta Dakta Nnamdi Azikiwe da sauran su duk ’yan adawa wadanda suke kalubalantar wuce gona da iri na jam’iyya mai mulki da ke rake da gwamnati.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

Ko a lokacin mulkin soja, an sami manyan kungiyoyin fararen huda kamar irin su ‘Campaign for Democracy (CD)’, ‘Mobement for National Reformation (MNR)’, kwamitin kare hakkin Dan’adam (CDHR), kungiyar lauyoyin Nijeriya (NBA), kungiyar kwadago (NLC) da dai sauran su, sun yi tsayan daka wajen yakar mulkin kama-karya da rashin gudanar da mulki yadda ya kamata.

Irinsu Cif Gani Fawehinmi, Farfesa Wole Soyinka, Aka Bashorun, Olisa Agbakoba, Femi Falana, Beko Ransom-Kuti, Ayo Obe, Ken Saro-Wiwa da dai sauransu sun shiga gidan yari saboda sukar gwamnati.

Amma a yau a siyasar Nijeriya babu wata adawa mai karfi da yadda zai iya kawo sauyi ga manufofin gwamnati wadanda ba dace da tsarin mulki ba. Tun bayan kammala zabukan da suka gabata, jam’iyyun adawa sun yi barci, lamarin da ya sa jam’iyyar APC mai mulkin gwamnatin tarayya take jagorantar ‘yan Nijeriya yadda take so.

Yanzu haka dai a Nijeriya manyan jam’iyyun adawar sun hada da jam’iyyun PDP da LP, amma babu daya daga cikinsu da ta iya kalubalantar jam’iyyar APC mai mulki yadda ya kamata a wurin gudanar da mulkin Nijeriya.

A yanzu haka dai, ‘yan Nijeriya sun zura ido don ganin yadda PDP da LP za su iya amsar mulki a hannun jam’iyyar APC.

Adawa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
Hujjojin Obasanjo Na Cewa “Dimokuradiyyar Turawan Yamma Ba Ta Karbi Afirka Ba”

Hujjojin Obasanjo Na Cewa “Dimokuradiyyar Turawan Yamma Ba Ta Karbi Afirka Ba”

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.