ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi: Raunin Jam’iyyun Adawa Da Barazana Ga Dimokuradiyyar Nijeriya

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Adawa

Daya daga cikin babbar barazana ga Dimokuradiyyar ita ce, raunin jam’iyyun adawa, wanda mutane da dama na ganin hakan zai sa kasar ta kama tsarin jam’iyya guda daya.

A cikin tsarin mulkin dimokuradiyya, ‘yan adawa na matukar taka muhimmiyar rawa wajen kalubalantar gwamnati ta yadda za a gyara tsarin da bai yi daidai da tsarin mulkin dimokuradiyya ba. Ko da gwamnati ba ta yi amfani da kiraye-kirayen ‘yan adawa wajen gyara kuskure, tana amfana da su wajen gudanar da bincike a kan korafin da suka gabatar ta yadda za a samu damar yin gyara.

  • Kano: Kotun Daukaka Kara Ta Bukace Lauyoyin Su Mayar Da Kwafin Takardun Shari’ar
  • Xi Jinping Ya Gana Da Takwaransa Na Uruguay

Tsarin mulki na shugabancin kasa ya kawo ka’idoji ta yadda jam’iyyun adawa za su iya gudanar da bincike wajen gudanar da harkokin gwamnati.

ADVERTISEMENT

A ko da yaushe, jam’iyyar adawa na sa jam’iyya mai mulki ta tashi tsaye wajen gudanar da tsare-tsare da kuma shirye-shiryenta. Haka nan kuma suna dakile wuce gona da iri da muguwar mulkin kama-karya.

A jamhuriya ta daya da ta biyu, Nijeriya tana da al’adar gudanar da siyasar adawa. Marigayi Cif Obafemi Awolowo na jam’iyyar ‘Action Group’ (AG), wanda daga ta koma jam’iyyar ‘Unity Party of Nigeria’ (UPN), a matsayinsa na dan adawa, ya tunkari gwamnatin da ke kan karagar mulki da hujjoji masu tsauri da alkaluma ta yadda za a ceto Nijeriya. Hatta Dakta Nnamdi Azikiwe da sauran su duk ’yan adawa wadanda suke kalubalantar wuce gona da iri na jam’iyya mai mulki da ke rake da gwamnati.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Ko a lokacin mulkin soja, an sami manyan kungiyoyin fararen huda kamar irin su ‘Campaign for Democracy (CD)’, ‘Mobement for National Reformation (MNR)’, kwamitin kare hakkin Dan’adam (CDHR), kungiyar lauyoyin Nijeriya (NBA), kungiyar kwadago (NLC) da dai sauran su, sun yi tsayan daka wajen yakar mulkin kama-karya da rashin gudanar da mulki yadda ya kamata.

Irinsu Cif Gani Fawehinmi, Farfesa Wole Soyinka, Aka Bashorun, Olisa Agbakoba, Femi Falana, Beko Ransom-Kuti, Ayo Obe, Ken Saro-Wiwa da dai sauransu sun shiga gidan yari saboda sukar gwamnati.

Amma a yau a siyasar Nijeriya babu wata adawa mai karfi da yadda zai iya kawo sauyi ga manufofin gwamnati wadanda ba dace da tsarin mulki ba. Tun bayan kammala zabukan da suka gabata, jam’iyyun adawa sun yi barci, lamarin da ya sa jam’iyyar APC mai mulkin gwamnatin tarayya take jagorantar ‘yan Nijeriya yadda take so.

Yanzu haka dai a Nijeriya manyan jam’iyyun adawar sun hada da jam’iyyun PDP da LP, amma babu daya daga cikinsu da ta iya kalubalantar jam’iyyar APC mai mulki yadda ya kamata a wurin gudanar da mulkin Nijeriya.

A yanzu haka dai, ‘yan Nijeriya sun zura ido don ganin yadda PDP da LP za su iya amsar mulki a hannun jam’iyyar APC.

Adawa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
Hujjojin Obasanjo Na Cewa “Dimokuradiyyar Turawan Yamma Ba Ta Karbi Afirka Ba”

Hujjojin Obasanjo Na Cewa “Dimokuradiyyar Turawan Yamma Ba Ta Karbi Afirka Ba”

LABARAI MASU NASABA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.