ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi: Raunin Jam’iyyun Adawa Da Barazana Ga Dimokuradiyyar Nijeriya

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Adawa

Daya daga cikin babbar barazana ga Dimokuradiyyar ita ce, raunin jam’iyyun adawa, wanda mutane da dama na ganin hakan zai sa kasar ta kama tsarin jam’iyya guda daya.

A cikin tsarin mulkin dimokuradiyya, ‘yan adawa na matukar taka muhimmiyar rawa wajen kalubalantar gwamnati ta yadda za a gyara tsarin da bai yi daidai da tsarin mulkin dimokuradiyya ba. Ko da gwamnati ba ta yi amfani da kiraye-kirayen ‘yan adawa wajen gyara kuskure, tana amfana da su wajen gudanar da bincike a kan korafin da suka gabatar ta yadda za a samu damar yin gyara.

  • Kano: Kotun Daukaka Kara Ta Bukace Lauyoyin Su Mayar Da Kwafin Takardun Shari’ar
  • Xi Jinping Ya Gana Da Takwaransa Na Uruguay

Tsarin mulki na shugabancin kasa ya kawo ka’idoji ta yadda jam’iyyun adawa za su iya gudanar da bincike wajen gudanar da harkokin gwamnati.

ADVERTISEMENT

A ko da yaushe, jam’iyyar adawa na sa jam’iyya mai mulki ta tashi tsaye wajen gudanar da tsare-tsare da kuma shirye-shiryenta. Haka nan kuma suna dakile wuce gona da iri da muguwar mulkin kama-karya.

A jamhuriya ta daya da ta biyu, Nijeriya tana da al’adar gudanar da siyasar adawa. Marigayi Cif Obafemi Awolowo na jam’iyyar ‘Action Group’ (AG), wanda daga ta koma jam’iyyar ‘Unity Party of Nigeria’ (UPN), a matsayinsa na dan adawa, ya tunkari gwamnatin da ke kan karagar mulki da hujjoji masu tsauri da alkaluma ta yadda za a ceto Nijeriya. Hatta Dakta Nnamdi Azikiwe da sauran su duk ’yan adawa wadanda suke kalubalantar wuce gona da iri na jam’iyya mai mulki da ke rake da gwamnati.

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Ko a lokacin mulkin soja, an sami manyan kungiyoyin fararen huda kamar irin su ‘Campaign for Democracy (CD)’, ‘Mobement for National Reformation (MNR)’, kwamitin kare hakkin Dan’adam (CDHR), kungiyar lauyoyin Nijeriya (NBA), kungiyar kwadago (NLC) da dai sauran su, sun yi tsayan daka wajen yakar mulkin kama-karya da rashin gudanar da mulki yadda ya kamata.

Irinsu Cif Gani Fawehinmi, Farfesa Wole Soyinka, Aka Bashorun, Olisa Agbakoba, Femi Falana, Beko Ransom-Kuti, Ayo Obe, Ken Saro-Wiwa da dai sauransu sun shiga gidan yari saboda sukar gwamnati.

Amma a yau a siyasar Nijeriya babu wata adawa mai karfi da yadda zai iya kawo sauyi ga manufofin gwamnati wadanda ba dace da tsarin mulki ba. Tun bayan kammala zabukan da suka gabata, jam’iyyun adawa sun yi barci, lamarin da ya sa jam’iyyar APC mai mulkin gwamnatin tarayya take jagorantar ‘yan Nijeriya yadda take so.

Yanzu haka dai a Nijeriya manyan jam’iyyun adawar sun hada da jam’iyyun PDP da LP, amma babu daya daga cikinsu da ta iya kalubalantar jam’iyyar APC mai mulki yadda ya kamata a wurin gudanar da mulkin Nijeriya.

A yanzu haka dai, ‘yan Nijeriya sun zura ido don ganin yadda PDP da LP za su iya amsar mulki a hannun jam’iyyar APC.

Adawa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
Tambarin Dimokuradiyya

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Next Post
Hujjojin Obasanjo Na Cewa “Dimokuradiyyar Turawan Yamma Ba Ta Karbi Afirka Ba”

Hujjojin Obasanjo Na Cewa “Dimokuradiyyar Turawan Yamma Ba Ta Karbi Afirka Ba”

LABARAI MASU NASABA

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.