• English
  • Business News
Friday, October 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

by Rabilu Sanusi Bena
2 months ago
Ummi Nuhu

A ƴan kwanakin nan ne, jarumai daga masana’antar Kannywood, waɗanda a baya suka samu ɗaukaka tare da samun ɗimbin dukiya a masana’antar ta shirya fina-finan Hausa, suka koka a kan yadda duniya ta juya musu baya.

Ko shakka babu, waɗannan jarumai sun yi matuƙar samun alhairai da masoyan daban-daban a wancan lokaci. Ɗaya daga cikin jaruman ita ce, Ummi Nuhu, wadda a shekarar 2000 zuwa 2015, tana ɗaya daga cikin manyan-manyan waɗanda ludayinsu yake kan dawo a masana’antar.

  • Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ
  • Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Ummi Nuhu, wadda iyayenta ‘yan asalin garin Bunkure ne da ke Jihar Kano, amma aka haife ta; ta kuma tashi a Jihar Kaduna, a shekara ta 2000; tauraruwarta ta fara haskakawa a Kannywood, a ƙarƙashin jagorancin Ali Nuhu, ta yi fice a fina-finai da dama da suka haɗa da; Al’amari, Fil’azal, Zo Mu Zauna da kuma Rabin Jiki, inda ta zama ɗaya daga cikin fitattun jarumai na Kamfanin FKD.

Amma daga baya, ta ɓace ɓat; an daina ganin fuskarta a shirin fina-finan Hausa na Kannywood, wannan ne dalilin ma da ya sanya masu sha’awar kallon fina-finan na Hausa a yanzu, ba su san ta ba. Kwanakin baya, jarumar Kannywood, Hadiza Gabon, ta yi hira da ita a cikin shirinta na ‘Gobon’s Room Talk Show’, a wannan shiri ne, Ummi ta bayyana batutuwa da dama dangane da rayuwarta a lokacin da take kan sharafinta da kuma lokacin da aka daina yayinta.

Haka zalika, Ummi a wata hira da ta yi da BBC Hausa, ta bayyana yadda ta yi da-na-sanin wasu abubuwa da dama da ta aikata a lokacin da kan ɗaukaka da tarin masoya, “Na yi lokacin da babu wani Furodusa da zai yi fim, ba tare da ya nemi na fito a cikinsa ba, a wancan lokacin; na samu damammaki masu ɗimbin yawa da suka haɗa da kuɗaɗe, daukaka ta masoya, har ta kai ga duk inda na shiga sai na haɗu da masoya maza da mata, suna ɗokin zuwana wannan waje”, in ji Ummi.

LABARAI MASU NASABA

Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 

Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?

“Na taɓa zama abar kwatance, musamman a ɓangaren da shafi kuɗi, suna, girmamawa, amma kuskuren da na yi ya zama dalilin da yasa masana’antar ta juya min baya, sakamakon babu abin da na iya ko na sani face; harkar ta fim. Halin da ake ciki yanzu, babu wani tallafi, babu aikin yi, akwai lokacin da ina da ɗimbin masoya da suke son aurena da kuma nuna min soyayya, amma sai na kasa zaɓen wanda zan ci gaba da rayuwata da shi a wancan lokaci.

Babban dalilin da ya jawo min koma-baya a harkar fim shi ne, hatsarin da na samu na mota, wanda Allah ya jarrabce ni da shi, na yi hatsarin mota da har sai da na samu karaya huɗu a ƙafata, sannan kuma na samu buguwa a kaina da har sai da na manta da komai na rayuwa da na sani a wancan lokaci, bugu da gari; fuskata ta samu raunuka masu yawa da suka canza mani fasalin fuskar tawa, hakan ya sa na ɗauki tsawon lokaci ina jinya.

Da ta ke amsa tambaya a kan ko ‘yan’uwan sana’arta na Kannywood sun taimaka mata a lokacin da take cikin wannan mawuyacin hali? Ummi ta ce, duk da babu wani wanda ya ɗauki nauyin jinyarta a wancan lokaci, amma dai ba za ta taɓa mantawa da yadda suka riƙa zuwa har gida suna gaishe ta ba, “Ni na ɗauki nauyin jinyar kaina, saboda bakin gwargwado ina da abin da zan iya ɗaukar nauyin jinyata”, in ji Ummi.

Dangane da da-na-sanin da ta ke yi a rayuwa kuma, Ummi ta ce; babu wani abu da take da-na-sanin rashin yi da ya wuce aure, domin da a ce ta yi aure, zuwa yanzu wataƙila da Allah ya azurta ta da samun zuri’a, waɗanda za su riƙa kula da ita yanzu da kuma bayan ta tsufa. “Don haka, ina fatan yin aure kafin rayuwata ta zo ƙarshe”.

Daga ƙarshe, tsohuwar jarumar ta buƙaci matasa masu tasowa a masana’antar Kannywood, da kada su maimaita irin kuskuren da da yawa daga cikin tsoffin jarumai mata suka yi, “Ina shawartar duka wata mace mai lokaci a masana’antar Kannywood yanzu, da ta tabbatar da cewa; ta saka hannun jari a wasu wuraren kasuwanci da za su riƙa samar mata da wani abu ta yadda ko da lokacin ɗaukakarta ya wuce, za ta ci gaba da yi; domin kula da rayuwarta.

Dalili kuwa shi ne, duk irin ɗaukakar da kika samu a yanzu, lokaci na nan zuwa da dole zai gushe, ki zama kamar ba ki taɓa samun wannan ɗaukaka ba, kamar yadda yanzu ake yi babu mu, duk kuwa da irin shaharar da muka samu a lokutan baya.

 

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 
Nishadi

Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 

October 11, 2025
Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?
Nishadi

Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?

October 11, 2025
Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano
Nishadi

Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano

October 6, 2025
Next Post
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

LABARAI MASU NASABA

Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta

Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta

October 23, 2025
Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa

October 23, 2025
Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 50, Sun Daƙile Hare-Hare A Borno

October 23, 2025
Me Ake Fatan Gani A Shirin Sin Na Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar Na Gaba

Me Ake Fatan Gani A Shirin Sin Na Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar Na Gaba

October 23, 2025
Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

October 23, 2025
Uwargidan Tinubu Ta Ƙaddamar Da Ɗakin Karatu Na E-learning A Zamfara

Uwargidan Tinubu Ta Ƙaddamar Da Ɗakin Karatu Na E-learning A Zamfara

October 23, 2025
Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Kasar Sin Ta Karyata Rahoto Na Zuki-ta-malle Da Wata Cibiyar Binciken Amurka Ta Fitar Game Da Hadin Gwiwar Sin Da Yammacin Afirka

October 23, 2025
An Kammala Taron JKS Inda Aka Amince Da Shawarwari Kan Shirin Ci Gaban Kasar Sin Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 15

An Kammala Taron JKS Inda Aka Amince Da Shawarwari Kan Shirin Ci Gaban Kasar Sin Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 15

October 23, 2025
Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 23, 2025
Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

October 23, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.