• English
  • Business News
Monday, July 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kokarin CBN Wajen Daga Darajar Naira

by Sulaiman
3 years ago
in Labarai
0
Kokarin CBN Wajen Daga Darajar Naira
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kwanan baya ne ‘yan Nijeriya suka wayi gari suka ga darajar Naira ta sauka kasa saboda tashin farashin dala, inda hakan ya zamo babban abin damuwa ganin yadda takardar ta Naira ta sauka har zuwa 710.

Wannan kalubalen ya janyo shafar daukacin tattalin arzikin kasar nan, inda hakan ya haifar da hauhawan tashin farashin kayan masarufi, makamashi da kuma shafar fannin sufurin Jiragen sama.

  • Ribar Dala Miliyan 240: ‘Yan Kasuwa Na Zargin CBN Da NNPC Da Take Musu Hakki

Hakan ya kasance tamkar kamar na lokacin tsohon shugaban kasa na na mulkin soji Janar Badamasi Babangida da ya kirkiro da tsarin SAP wanda ake yi masa lakabi da aji a jika biyo bayan shiga cikin tsarin karbar lamunin IMF, inda masu nazari a fannin tattalin arziki suke ganin shine silar faduwar darajar Naira Da kima gazawar kula da jin dadi da walwalar ‘yan Nijeriya.

An dai takardama iri -iri, kan menene musabbabin da ke shafar kudaden musayar.

Bugu da kari, ta kasance kowa na dora wa juna laifi da kuma tunanin menene mafita don a sake dawo da darajar Naira a kasar nan wacce a shekarun baya da suka gabata, ana yin musayar ta a kan 85 dai dai takadar Pound.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Bincike Kan Belin Dillalin Kwaya

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

A yanzu haka dai, kowa ya zura wa Babban Bankin Nijeriya CBN ido ganin cewa, Bankin shine ke da alhakkin samar da tsare-tsare da kuma sa ido kan yadda tafiyar da ayyukan musayar kudaden a kasuwar musayar kudaden domin ya tabbatar da cewa Naira ta samu dai daito.

Hakazalika, an yi yunkuri wajen kawar da kai kan maganar da take a zahirance na cewa kudaden waje ko wadanne iri ne, ana samun su ne ta hanyar zage wa wannan takardamar ta zama wajibi a mayar da hankali wajen a tattauna kan yadda za a sake farfado da darajar Naira a Nijeriya ta hanyar samar da tsare -tsare.

Kamfanin mai na Shell a kwanan baya ya bayyna cewa, abin takaici, Nijeriya ta ci gaba da kasance wa kasa da ta dogara kachokam a kan man Fetur da iskar Gas, inda kuma bata gari ke kutsa wa a cikin fannin suna sace man da aka samar da ya kai kusan kashi 80 a cikin dari, inda kuma ake ci gaba da samun tashin farashin gangar mai a kasuwar duniya.
Bisa da wannan fahimtar, zai iya tuna wa hakan ne ya sa bayan da makuntan CBN na yanzu suka shiga ofishi ne, suka kirkiro da sabbin tsare-tsare don a farfado da tattalin arzikin kasar nan yadda za a kara fadada samar wa da Nijeriya hada-hadar kudaden musaya na ketare.

Namjin kokarin da CBN ya yi wajen wanzar da wadannan tsare-tsaren sun taimaka matuka wajen sake farfado da fannin ayyukan noma musamman a karkashin shirin aikin noma Anchor Borrowers da kuma samar da tsarin yin noma don Ribas wadanda suka kasance daya daga ciikin hanyoyin bunkasa tattalin arzikin Nijeriya.

Bugu da kari, a cikin tsarin, CBN ya haramta shigo da kayayyaki 43 daga ketare tare da rage harkallar kasuwar fage ta musayar kudade wanda duk anyi wannan ne, don a magance kalubalen samar da kudaden musaya a kasar.
CBN ya kuma mayar da hankali a kan fannin da bai shafi harkar mai ba kamar fannin hakar ma’adanai, inda bankin ya zuba kudade a fannin don habaka sarrafa kayan da ake sarrafa wa a cikin gida Nijeriya, musamman domin a rage shigo da kaya daga ketare, musamman domin a habaka samar da kudaden musaya a kasar.

Har ila yau, bisa wasu alkaluman da CBN ya fitar sun nuna cewa, fannin ilimin boko na kasar nan ya fuskanci barazana sama da shekaru goma da suka wuce inda kuma a wata kididdigar ta CBN ta nuna cewa, Nijeriya ta kashe makudan kudade har dala biliyan 28.65 a cikin shekaru goma wajen zuwa neman ilimin boko a kasar waje wato daga 2010 zuwa 2020 duk wadannan dimbin kudaden ana samar da su ne ta hanyar kudaden musaya na kasar waje.

Har ila yau, abinda ke kara ciwa CBN da tattalin arzikin Nijeriya Tuwo a Kwarya shine, akasarin wadannan kudaden na musayar da ake yin amfani da su, na jabu ne domin an samo su ne a kasuwar bayan fage.

Bugu da kari, an kiyasta cewa, Nijeriya na tabka asarar da ta kai ta kimanin dala biliyan 1.3 a duk shekara wajen fitar da ake yi daga kasar zuwa ketare domin neman lafiya, inda hakan ya zamo wani babban nauyi a kan tattalin arzikin kasar.

Karin wani abin tkkaci shine, yadda kasuwar bayan fage a kasar ta koma tamkar ita ce ke jan Akalar kasuwar musayar kudaden musaya na kasar waje.
Yanzu Nijeriya na tunkarar kakar zaben 2023, inda kuma ‘yan siyasa a kasar ke ta kai Gwaro da Mari wajen samo kudaden musaya na kasar waje don fara gabatar da yakin neman zabe.

Anga irin wannan yar manuniyar a yayin da wasu jamiyyun siyasa a kasar suka yi ta ruwan dala a lokacin gudanar da zaben fidda gwani a kwanan baya, inda hakan ya kara shafar tattalin arzikin Nijeriya.

Wasu masu fashin baki na da ra’ayi wanda nima shine nawa irin ra’ayin cewar, mafita ita ce Gwamnatin Tarayya ta hanyar yin amfani da CBN ba tare da bata wani lokaci ba, ta daina samar da rangwame a fannonin kiwon lafiya da ilimin boko kuma Gwamnatin ta kara sanya wadannan fanonin biyu, a cikin kayayyaki 43 da aka haramta shigo wa da su cikin kasar nan.

Ya kamata CBN ya kara matsa lamba a Kan masu samar da kudaden musaya na kasar waje a kasar nan da kuma magance masu janyo kalubale a fannin
Ina da yakinin cewa, matukar aka rungumi tare da kuma wanzar da wadannan matakan, za su bai wa kudaden musaya na kasar waje damar kara daga darajar Naira.

Akwai kuma bukatar Gwamnatin ta kara jajirce wa wajen kara bai wa CBN kwarin gwiwar don gudanar da ayyukan da ya sa a gaba.

Adegoke, mai fashin baki ne a kan alamuran yau da kullum kuma ya na da zama a garin Akure a jihar Ondo.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ruwan-wuta: ‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Ta’adda, Sun Kubutar Da Dabbobi 110 A Katsina

Next Post

Son Zuciyar Wasu Tsiraru Ya Haddasa Rashin Tsaro A NIjeriya – Alhaji Ibrahim

Related

Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Bincike Kan Belin Dillalin Kwaya
Labarai

Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Bincike Kan Belin Dillalin Kwaya

12 minutes ago
Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar
Labarai

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

11 hours ago
Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo
Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

12 hours ago
‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas
Labarai

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

16 hours ago
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa
Manyan Labarai

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

16 hours ago
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano
Labarai

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

18 hours ago
Next Post
Son Zuciyar Wasu Tsiraru Ya Haddasa Rashin Tsaro A NIjeriya – Alhaji Ibrahim

Son Zuciyar Wasu Tsiraru Ya Haddasa Rashin Tsaro A NIjeriya - Alhaji Ibrahim

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Bincike Kan Belin Dillalin Kwaya

Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Bincike Kan Belin Dillalin Kwaya

July 28, 2025
Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

July 27, 2025
Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

July 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

July 27, 2025
Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

July 27, 2025
Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

July 27, 2025
Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

July 27, 2025
Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

July 27, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

July 27, 2025
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

July 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.