• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kokarin CBN Wajen Daga Darajar Naira

by Sulaiman
3 years ago
in Labarai
0
Kokarin CBN Wajen Daga Darajar Naira
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kwanan baya ne ‘yan Nijeriya suka wayi gari suka ga darajar Naira ta sauka kasa saboda tashin farashin dala, inda hakan ya zamo babban abin damuwa ganin yadda takardar ta Naira ta sauka har zuwa 710.

Wannan kalubalen ya janyo shafar daukacin tattalin arzikin kasar nan, inda hakan ya haifar da hauhawan tashin farashin kayan masarufi, makamashi da kuma shafar fannin sufurin Jiragen sama.

  • Ribar Dala Miliyan 240: ‘Yan Kasuwa Na Zargin CBN Da NNPC Da Take Musu Hakki

Hakan ya kasance tamkar kamar na lokacin tsohon shugaban kasa na na mulkin soji Janar Badamasi Babangida da ya kirkiro da tsarin SAP wanda ake yi masa lakabi da aji a jika biyo bayan shiga cikin tsarin karbar lamunin IMF, inda masu nazari a fannin tattalin arziki suke ganin shine silar faduwar darajar Naira Da kima gazawar kula da jin dadi da walwalar ‘yan Nijeriya.

An dai takardama iri -iri, kan menene musabbabin da ke shafar kudaden musayar.

Bugu da kari, ta kasance kowa na dora wa juna laifi da kuma tunanin menene mafita don a sake dawo da darajar Naira a kasar nan wacce a shekarun baya da suka gabata, ana yin musayar ta a kan 85 dai dai takadar Pound.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

A yanzu haka dai, kowa ya zura wa Babban Bankin Nijeriya CBN ido ganin cewa, Bankin shine ke da alhakkin samar da tsare-tsare da kuma sa ido kan yadda tafiyar da ayyukan musayar kudaden a kasuwar musayar kudaden domin ya tabbatar da cewa Naira ta samu dai daito.

Hakazalika, an yi yunkuri wajen kawar da kai kan maganar da take a zahirance na cewa kudaden waje ko wadanne iri ne, ana samun su ne ta hanyar zage wa wannan takardamar ta zama wajibi a mayar da hankali wajen a tattauna kan yadda za a sake farfado da darajar Naira a Nijeriya ta hanyar samar da tsare -tsare.

Kamfanin mai na Shell a kwanan baya ya bayyna cewa, abin takaici, Nijeriya ta ci gaba da kasance wa kasa da ta dogara kachokam a kan man Fetur da iskar Gas, inda kuma bata gari ke kutsa wa a cikin fannin suna sace man da aka samar da ya kai kusan kashi 80 a cikin dari, inda kuma ake ci gaba da samun tashin farashin gangar mai a kasuwar duniya.
Bisa da wannan fahimtar, zai iya tuna wa hakan ne ya sa bayan da makuntan CBN na yanzu suka shiga ofishi ne, suka kirkiro da sabbin tsare-tsare don a farfado da tattalin arzikin kasar nan yadda za a kara fadada samar wa da Nijeriya hada-hadar kudaden musaya na ketare.

Namjin kokarin da CBN ya yi wajen wanzar da wadannan tsare-tsaren sun taimaka matuka wajen sake farfado da fannin ayyukan noma musamman a karkashin shirin aikin noma Anchor Borrowers da kuma samar da tsarin yin noma don Ribas wadanda suka kasance daya daga ciikin hanyoyin bunkasa tattalin arzikin Nijeriya.

Bugu da kari, a cikin tsarin, CBN ya haramta shigo da kayayyaki 43 daga ketare tare da rage harkallar kasuwar fage ta musayar kudade wanda duk anyi wannan ne, don a magance kalubalen samar da kudaden musaya a kasar.
CBN ya kuma mayar da hankali a kan fannin da bai shafi harkar mai ba kamar fannin hakar ma’adanai, inda bankin ya zuba kudade a fannin don habaka sarrafa kayan da ake sarrafa wa a cikin gida Nijeriya, musamman domin a rage shigo da kaya daga ketare, musamman domin a habaka samar da kudaden musaya a kasar.

Har ila yau, bisa wasu alkaluman da CBN ya fitar sun nuna cewa, fannin ilimin boko na kasar nan ya fuskanci barazana sama da shekaru goma da suka wuce inda kuma a wata kididdigar ta CBN ta nuna cewa, Nijeriya ta kashe makudan kudade har dala biliyan 28.65 a cikin shekaru goma wajen zuwa neman ilimin boko a kasar waje wato daga 2010 zuwa 2020 duk wadannan dimbin kudaden ana samar da su ne ta hanyar kudaden musaya na kasar waje.

Har ila yau, abinda ke kara ciwa CBN da tattalin arzikin Nijeriya Tuwo a Kwarya shine, akasarin wadannan kudaden na musayar da ake yin amfani da su, na jabu ne domin an samo su ne a kasuwar bayan fage.

Bugu da kari, an kiyasta cewa, Nijeriya na tabka asarar da ta kai ta kimanin dala biliyan 1.3 a duk shekara wajen fitar da ake yi daga kasar zuwa ketare domin neman lafiya, inda hakan ya zamo wani babban nauyi a kan tattalin arzikin kasar.

Karin wani abin tkkaci shine, yadda kasuwar bayan fage a kasar ta koma tamkar ita ce ke jan Akalar kasuwar musayar kudaden musaya na kasar waje.
Yanzu Nijeriya na tunkarar kakar zaben 2023, inda kuma ‘yan siyasa a kasar ke ta kai Gwaro da Mari wajen samo kudaden musaya na kasar waje don fara gabatar da yakin neman zabe.

Anga irin wannan yar manuniyar a yayin da wasu jamiyyun siyasa a kasar suka yi ta ruwan dala a lokacin gudanar da zaben fidda gwani a kwanan baya, inda hakan ya kara shafar tattalin arzikin Nijeriya.

Wasu masu fashin baki na da ra’ayi wanda nima shine nawa irin ra’ayin cewar, mafita ita ce Gwamnatin Tarayya ta hanyar yin amfani da CBN ba tare da bata wani lokaci ba, ta daina samar da rangwame a fannonin kiwon lafiya da ilimin boko kuma Gwamnatin ta kara sanya wadannan fanonin biyu, a cikin kayayyaki 43 da aka haramta shigo wa da su cikin kasar nan.

Ya kamata CBN ya kara matsa lamba a Kan masu samar da kudaden musaya na kasar waje a kasar nan da kuma magance masu janyo kalubale a fannin
Ina da yakinin cewa, matukar aka rungumi tare da kuma wanzar da wadannan matakan, za su bai wa kudaden musaya na kasar waje damar kara daga darajar Naira.

Akwai kuma bukatar Gwamnatin ta kara jajirce wa wajen kara bai wa CBN kwarin gwiwar don gudanar da ayyukan da ya sa a gaba.

Adegoke, mai fashin baki ne a kan alamuran yau da kullum kuma ya na da zama a garin Akure a jihar Ondo.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ruwan-wuta: ‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Ta’adda, Sun Kubutar Da Dabbobi 110 A Katsina

Next Post

Son Zuciyar Wasu Tsiraru Ya Haddasa Rashin Tsaro A NIjeriya – Alhaji Ibrahim

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

5 hours ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna
Labarai

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

6 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

7 hours ago
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya
Labarai

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

8 hours ago
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF
Manyan Labarai

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

10 hours ago
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike
Manyan Labarai

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

12 hours ago
Next Post
Son Zuciyar Wasu Tsiraru Ya Haddasa Rashin Tsaro A NIjeriya – Alhaji Ibrahim

Son Zuciyar Wasu Tsiraru Ya Haddasa Rashin Tsaro A NIjeriya - Alhaji Ibrahim

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.