ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ribar Dala Miliyan 240: ‘Yan Kasuwa Na Zargin CBN Da NNPC Da Take Musu Hakki

by Sulaiman Bala Idris
4 years ago
CBN

‘Yan kasuwan mai daga kamfanin Canaf da BLCO da sauran wasu masu hada-hadar kasuwancin man fetur sun gudanar da zanga-zanga kan zargin kamfanin mai na kasa (NNPC) da babban bankin Nijeriya (CBN) wajen kawo tsaiko kan biyansu kudadensu.

Zanga-zangar ta gudana ce a ranar Laraba da ta gabata, inda suka yi dafifi a harabar shalkwatan kamfanin NNPC da ke Abuja, inda suke ta daga kwalaye masu dauke da rubutu daban-daban da ke nuna a biyasu ribarsa tare da cewa shugaban kasa yana sane da kasuwancin da suke gudanarwa.

  • Sabon Kamfanin Mai Na NNPC Zai Ceto Makamashin Nijeriya

Da yake zantawa da manema labarai, shugaban tawagar, Mohammed Abubakar ya ce, “Mu ne wakilan da ke sayar da danyan man Nijeriya ga kamfanoni masu matatun mai.”
A cewar Abubakar, suna gudanar da zanga-zangar ne domin NNPC ta baya su kudaden a kan dala biyu ga kowacce gangan mai.

ADVERTISEMENT

“Shugaban kasa ya amince da gudanar da kasuwancinmu tun a shekarar 2018. Muna so tsohuwar NNPC ta biya mu ba sabuwa ba.”

Ya yaba wa jami’an tsaro wajen samar musu da tsaro lokacin da suke gudanar da zanga-zangan tun lokacin da suka fara har zuwa 8 ga watan Yulin 2022, lokacin da Sufeton ‘yan sanda na kasa, IGP Usman Baba ya bukaci su dakatar da zanga-zangar.

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Ta Yi Asarar Biliyoyin Naira Saboda Dakatar Da Shigo Da Motoci Ta Iyakokinta

Farashin Siminti Zai Ragu Idan Farashin Kayan Aiki Ya Sauka – BUA

Sun bayyan akwai cikakken hujja da ke nanu cewa NNPC da CBN da gangan suka ki biyan kudaden.
“Shugaban kasa ya amince da a biya mu wadannan kudade na riba a hukumance bisa kasuwancin da kamfanonin BLCo LPFO da kuma LNG suka gudanar.

“Muna gudanar da wannan zanga-zangar ne domin sanar da duniya cewa NNPC da CBN suna amfani da sunan shugaban kasa wajen kokarin cin kudin ba tare da sanin shugaban kasa ba.”

Kamfanin ya gudanar da yarjejeniya a ranar 28 ga watan Satumbar 2021, inda ya samu amincewar karamin ministan mai, wanda ya nuna wa ‘yan jarida. Yarjejeniyar mai take, “Mu kamfanin Canaf mun saka hannun yarjejeniya da jami’anmu, Mista Anthony Awa Mba da Mista Mohammed Abubakar domin kawo mai ga tare da BLCo da dukkan sauran abubuwan da suka shafi man fetur a Nijeriya.

“Bayan kammala dukkan hada-hadar kasuwancin, mu kamfanin Canaf mun bukaci a biya mu game da wannan kasuwanci wanda muka tura asusun banki kai-tsaye ga NNPC da fadar shugaban kasa nan take.”

Shugaban kamfanin, Mista Okwii Modekwe yana kira da kamfani NNPC da ta biya ‘yan kasuwan dala miliyan 240 daga cikin dala biliyan daya na kasuwancin da suka rattaba hannu tun a ranar 19 ga watan Yulin 2018.

CBN
Sulaiman Bala Idris
+ postsBio
  • Sulaiman Bala Idris
    https://hausa.leadership.ng/author/sulaiman-bala-idris/
    Hayaniya ‘Yar Facebook!
  • Sulaiman Bala Idris
    https://hausa.leadership.ng/author/sulaiman-bala-idris/
    Mummunan Zato
  • Sulaiman Bala Idris
    https://hausa.leadership.ng/author/sulaiman-bala-idris/
    Me Ake Nufi Da Ado? 
  • Sulaiman Bala Idris
    https://hausa.leadership.ng/author/sulaiman-bala-idris/
    Gwamna Dauda Lawal A Shekara 60: Inda Akwai Fata, Akwai Mafita

MASU ALAKA

Nijeriya Ta Yi Asarar Biliyoyin Naira Saboda Dakatar Da Shigo Da Motoci Ta Iyakokinta
Labaran Kasuwanci

Nijeriya Ta Yi Asarar Biliyoyin Naira Saboda Dakatar Da Shigo Da Motoci Ta Iyakokinta

May 29, 2026
Farashin Siminti Zai Ragu Idan Farashin Kayan Aiki Ya Sauka – BUA
Labaran Kasuwanci

Farashin Siminti Zai Ragu Idan Farashin Kayan Aiki Ya Sauka – BUA

May 21, 2026
Indomie Ta Sake Karrama Kwastominta A Gasar “Garabasar Samun Nasara” A Jihohin Arewacin Nijeriya
Labaran Kasuwanci

Indomie Ta Sake Karrama Kwastominta A Gasar “Garabasar Samun Nasara” A Jihohin Arewacin Nijeriya

April 21, 2026
Next Post
An Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Cinikayya Da Raya Tattalin Arziki Ta Dalar Amurka Miliyan 170 Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka

An Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Cinikayya Da Raya Tattalin Arziki Ta Dalar Amurka Miliyan 170 Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.