ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ribar Dala Miliyan 240: ‘Yan Kasuwa Na Zargin CBN Da NNPC Da Take Musu Hakki

by Sulaiman Bala Idris
4 years ago
CBN

‘Yan kasuwan mai daga kamfanin Canaf da BLCO da sauran wasu masu hada-hadar kasuwancin man fetur sun gudanar da zanga-zanga kan zargin kamfanin mai na kasa (NNPC) da babban bankin Nijeriya (CBN) wajen kawo tsaiko kan biyansu kudadensu.

Zanga-zangar ta gudana ce a ranar Laraba da ta gabata, inda suka yi dafifi a harabar shalkwatan kamfanin NNPC da ke Abuja, inda suke ta daga kwalaye masu dauke da rubutu daban-daban da ke nuna a biyasu ribarsa tare da cewa shugaban kasa yana sane da kasuwancin da suke gudanarwa.

  • Sabon Kamfanin Mai Na NNPC Zai Ceto Makamashin Nijeriya

Da yake zantawa da manema labarai, shugaban tawagar, Mohammed Abubakar ya ce, “Mu ne wakilan da ke sayar da danyan man Nijeriya ga kamfanoni masu matatun mai.”
A cewar Abubakar, suna gudanar da zanga-zangar ne domin NNPC ta baya su kudaden a kan dala biyu ga kowacce gangan mai.

ADVERTISEMENT

“Shugaban kasa ya amince da gudanar da kasuwancinmu tun a shekarar 2018. Muna so tsohuwar NNPC ta biya mu ba sabuwa ba.”

Ya yaba wa jami’an tsaro wajen samar musu da tsaro lokacin da suke gudanar da zanga-zangan tun lokacin da suka fara har zuwa 8 ga watan Yulin 2022, lokacin da Sufeton ‘yan sanda na kasa, IGP Usman Baba ya bukaci su dakatar da zanga-zangar.

LABARAI MASU NASABA

Wani Kamfani Ya Tallafa Wa Masu Sana’ar Shayi A Kano

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Sun bayyan akwai cikakken hujja da ke nanu cewa NNPC da CBN da gangan suka ki biyan kudaden.
“Shugaban kasa ya amince da a biya mu wadannan kudade na riba a hukumance bisa kasuwancin da kamfanonin BLCo LPFO da kuma LNG suka gudanar.

“Muna gudanar da wannan zanga-zangar ne domin sanar da duniya cewa NNPC da CBN suna amfani da sunan shugaban kasa wajen kokarin cin kudin ba tare da sanin shugaban kasa ba.”

Kamfanin ya gudanar da yarjejeniya a ranar 28 ga watan Satumbar 2021, inda ya samu amincewar karamin ministan mai, wanda ya nuna wa ‘yan jarida. Yarjejeniyar mai take, “Mu kamfanin Canaf mun saka hannun yarjejeniya da jami’anmu, Mista Anthony Awa Mba da Mista Mohammed Abubakar domin kawo mai ga tare da BLCo da dukkan sauran abubuwan da suka shafi man fetur a Nijeriya.

“Bayan kammala dukkan hada-hadar kasuwancin, mu kamfanin Canaf mun bukaci a biya mu game da wannan kasuwanci wanda muka tura asusun banki kai-tsaye ga NNPC da fadar shugaban kasa nan take.”

Shugaban kamfanin, Mista Okwii Modekwe yana kira da kamfani NNPC da ta biya ‘yan kasuwan dala miliyan 240 daga cikin dala biliyan daya na kasuwancin da suka rattaba hannu tun a ranar 19 ga watan Yulin 2018.

CBN
Sulaiman Bala Idris
+ postsBio
  • Sulaiman Bala Idris
    https://hausa.leadership.ng/author/sulaiman-bala-idris/
    Gwamna Dauda Lawal A Shekara 61:Shugaban Da Ke Gudanar Da Mulki Bisa Kyakkyawar Manufa
  • Sulaiman Bala Idris
    https://hausa.leadership.ng/author/sulaiman-bala-idris/
    ‘Symbolic Interactionism’:Sabuwar Makaranta A Kimiyyar Zamantakewa
  • Sulaiman Bala Idris
    https://hausa.leadership.ng/author/sulaiman-bala-idris/
    Hayaniya ‘Yar Facebook!
  • Sulaiman Bala Idris
    https://hausa.leadership.ng/author/sulaiman-bala-idris/
    Mummunan Zato

MASU ALAKA

Wani Kamfani Ya Tallafa Wa Masu Sana’ar Shayi A Kano
Labaran Kasuwanci

Wani Kamfani Ya Tallafa Wa Masu Sana’ar Shayi A Kano

August 23, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba
Labaran Kasuwanci

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Nijeriya Ta Yi Asarar Biliyoyin Naira Saboda Dakatar Da Shigo Da Motoci Ta Iyakokinta
Labaran Kasuwanci

Nijeriya Ta Yi Asarar Biliyoyin Naira Saboda Dakatar Da Shigo Da Motoci Ta Iyakokinta

May 29, 2026
Next Post
An Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Cinikayya Da Raya Tattalin Arziki Ta Dalar Amurka Miliyan 170 Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka

An Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Cinikayya Da Raya Tattalin Arziki Ta Dalar Amurka Miliyan 170 Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.