• Leadership Hausa
Monday, October 2, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ribar Dala Miliyan 240: ‘Yan Kasuwa Na Zargin CBN Da NNPC Da Take Musu Hakki

by Sulaiman Bala Idris
1 year ago
in Labaran Kasuwanci
0
Ribar Dala Miliyan 240: ‘Yan Kasuwa Na Zargin CBN Da NNPC Da Take Musu Hakki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

‘Yan kasuwan mai daga kamfanin Canaf da BLCO da sauran wasu masu hada-hadar kasuwancin man fetur sun gudanar da zanga-zanga kan zargin kamfanin mai na kasa (NNPC) da babban bankin Nijeriya (CBN) wajen kawo tsaiko kan biyansu kudadensu.

Zanga-zangar ta gudana ce a ranar Laraba da ta gabata, inda suka yi dafifi a harabar shalkwatan kamfanin NNPC da ke Abuja, inda suke ta daga kwalaye masu dauke da rubutu daban-daban da ke nuna a biyasu ribarsa tare da cewa shugaban kasa yana sane da kasuwancin da suke gudanarwa.

  • Sabon Kamfanin Mai Na NNPC Zai Ceto Makamashin Nijeriya

Da yake zantawa da manema labarai, shugaban tawagar, Mohammed Abubakar ya ce, “Mu ne wakilan da ke sayar da danyan man Nijeriya ga kamfanoni masu matatun mai.”
A cewar Abubakar, suna gudanar da zanga-zangar ne domin NNPC ta baya su kudaden a kan dala biyu ga kowacce gangan mai.

“Shugaban kasa ya amince da gudanar da kasuwancinmu tun a shekarar 2018. Muna so tsohuwar NNPC ta biya mu ba sabuwa ba.”

Ya yaba wa jami’an tsaro wajen samar musu da tsaro lokacin da suke gudanar da zanga-zangan tun lokacin da suka fara har zuwa 8 ga watan Yulin 2022, lokacin da Sufeton ‘yan sanda na kasa, IGP Usman Baba ya bukaci su dakatar da zanga-zangar.

Labarai Masu Nasaba

Man Girki Mara Asali: Kamfanin Power Oil Ya Kulla Alaka Da Ali Nuhu Kan Wayar Da Kai

Kamfanonin Da Suka Durkushe A Arewa Cikin Shekara 44

Sun bayyan akwai cikakken hujja da ke nanu cewa NNPC da CBN da gangan suka ki biyan kudaden.
“Shugaban kasa ya amince da a biya mu wadannan kudade na riba a hukumance bisa kasuwancin da kamfanonin BLCo LPFO da kuma LNG suka gudanar.

“Muna gudanar da wannan zanga-zangar ne domin sanar da duniya cewa NNPC da CBN suna amfani da sunan shugaban kasa wajen kokarin cin kudin ba tare da sanin shugaban kasa ba.”

Kamfanin ya gudanar da yarjejeniya a ranar 28 ga watan Satumbar 2021, inda ya samu amincewar karamin ministan mai, wanda ya nuna wa ‘yan jarida. Yarjejeniyar mai take, “Mu kamfanin Canaf mun saka hannun yarjejeniya da jami’anmu, Mista Anthony Awa Mba da Mista Mohammed Abubakar domin kawo mai ga tare da BLCo da dukkan sauran abubuwan da suka shafi man fetur a Nijeriya.

“Bayan kammala dukkan hada-hadar kasuwancin, mu kamfanin Canaf mun bukaci a biya mu game da wannan kasuwanci wanda muka tura asusun banki kai-tsaye ga NNPC da fadar shugaban kasa nan take.”

Shugaban kamfanin, Mista Okwii Modekwe yana kira da kamfani NNPC da ta biya ‘yan kasuwan dala miliyan 240 daga cikin dala biliyan daya na kasuwancin da suka rattaba hannu tun a ranar 19 ga watan Yulin 2018.

ShareTweetSendShare
Previous Post

Atiku Da Tinubu Sun Fara Cacar Baki Kan Zaben 2023

Next Post

An Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Cinikayya Da Raya Tattalin Arziki Ta Dalar Amurka Miliyan 170 Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka

Related

Man Girki Mara Asali: Kamfanin Power Oil Ya Kulla Alaka Da Ali Nuhu Kan Wayar Da Kai
Labaran Kasuwanci

Man Girki Mara Asali: Kamfanin Power Oil Ya Kulla Alaka Da Ali Nuhu Kan Wayar Da Kai

1 month ago
‘Yan Takaran Gwamna 8 Sun Mara Wa Gwamnan Gombe Baya
Labaran Kasuwanci

Kamfanonin Da Suka Durkushe A Arewa Cikin Shekara 44

2 months ago
PDP Ta Yi Satar Amsa Daga Manufofin Buhari – Tinubu
Labaran Kasuwanci

Amurka Ta Bukaci Aiki Tare Da Sabuwar Gwamnatin Tinubu

4 months ago
Dakatar Da Shigo Da Manja: Kwararru A Nijeriya Sun Bukaci A Zuba Jari Mai Yawa A Fannin
Labaran Kasuwanci

Dakatar Da Shigo Da Manja: Kwararru A Nijeriya Sun Bukaci A Zuba Jari Mai Yawa A Fannin

5 months ago
Yadda Dawo Da Tsaffin Takardun Kudi Ya Kara Bunkasa Kasuwar Hatsi A Jihar Katsina
Labaran Kasuwanci

Yadda Dawo Da Tsaffin Takardun Kudi Ya Kara Bunkasa Kasuwar Hatsi A Jihar Katsina

5 months ago
Karancin Kudi: Mun Yi Asarar Kwai Na Biliyan 30 -Masu Kiwo
Labaran Kasuwanci

Karancin Kudi: Mun Yi Asarar Kwai Na Biliyan 30 -Masu Kiwo

7 months ago
Next Post
An Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Cinikayya Da Raya Tattalin Arziki Ta Dalar Amurka Miliyan 170 Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka

An Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Cinikayya Da Raya Tattalin Arziki Ta Dalar Amurka Miliyan 170 Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka

LABARAI MASU NASABA

Kotu A Amurka Ta Umarci Jami’ar Chicago Ta Bai Wa Atiku Bayanan Karatun Tinubu

Kotu A Amurka Ta Umarci Jami’ar Chicago Ta Bai Wa Atiku Bayanan Karatun Tinubu

October 1, 2023
Tinubu

Ranar ‘Yanci: Tinubu Ya Kara Wa Kananan Ma’aikata N25,000 Kan Albashinsu

October 1, 2023
Hangzhou

Birnin Hangzhou Ya Samu Karuwar Masu Yawon Bude Ido Albarkacin Gasar Wasanni Ta Asiya Dake Gudana

October 1, 2023
Syria

Shugaban Syria: Manyan Tsare-tsare Uku Na duniya Su Ne Jagororin Sabuwar Duniya

October 1, 2023
BUA

Daga Gobe 2 Ga Oktoba Farashin Buhun Simintin BUA Ya Koma N3,500 – Kamfanin

October 1, 2023
Kasar Sin

Ofishin Jakadancin Kasar Sin Dake Najeriya Ya Shirya Bikin Murnar Cikar Sin Shekaru 74 Da Kafuwa

October 1, 2023
Yadda ‘Arewa Peace Ambassador Forum’ Ta Nada Sheikh Muhajjadina Jakadan Zaman Lafiya

Yadda ‘Arewa Peace Ambassador Forum’ Ta Nada Sheikh Muhajjadina Jakadan Zaman Lafiya

October 1, 2023
Amurka

Amurka Ita Ce “Daular Karya”Ta Ko Wace Fuska

October 1, 2023
Gwamnatin Tarayya Ta Yaba Da Ayyukan Bello Koko Na Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Amince Da Kafa Sashi Na Musamman A NPA Don Inganta Ayyukanta

October 1, 2023
Dambe: An Fafata Tsakanin Dan Aliyu Da Rabe Shagon Ebola

Dambe: An Fafata Tsakanin Dan Aliyu Da Rabe Shagon Ebola

October 1, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.