• English
  • Business News
Saturday, October 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

by Abba Ibrahim Wada
20 seconds ago
in Wasanni
0
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kyautar lashe gasar Ballon d’Or yanzu ta zama kyautar da take auna kokarin dan wasa ko kuma wadda take fayyace dan wasan da ya fi nuna bajinta a duniyar kwallon kafa musamman a tsakanin matasa.

A karshen watan da ya gabata ne aka yi bikin karrama gwarzon ‘yankwallon kafa na duniya na shekarar 2025, inda aka karrama fitattun ‘yanwasa da suka nuna bajinta da kwarewa a kungiyoyi da kasashensu a kakar da ta wuce. Kyautar Ballon d’Or, karramawa ce da take da matukar tasiri a kwallon kafa, inda duk da cewa hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA tana karrama gwarazan da take gani su ne kan gaba a duniya, an fi kallo tare da amfani da karramawar ta Ballon d’Or a matsayin wadda ta fi daraja.

  • Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina
  • Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

A taron na, fitaccen danwasan kasar Faransa da kungiyar PSG, Ousmane Dembele ya lashe kyautar ta bana a bikin wanda aka yi a dakin taro na Theatre du Chatelet da ke birnin Paris a kasar Faransa.

Aitana Bonmati ce ta lashe Ballon d’Or ta bangaren mata, wanda shi ne karo na uku da ta lashe kyautar a jere. Wani abu da ya ja hankalin masu bibiyar karramawar daga Nijeriya shi ne yadda mai tsaron ragar kungiyar kwallon kafa ta mata wato Super Falcons, Chiamaka Ndanozie ta zo ta hudu a cikin masu tsaron raga mata a duniya.

Wadanne fitattun ‘yan kwallon kafan Nijeriya ne suka kusa lashe kambun a tarihin karramawar?

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Ƴar Wasan Gaban Nijeriya, Ifeoma Onumonu Ta Yi Ritaya

BICTOR IKPEBA – 1997

Dan wasan Nijeriya Bictor Ikpeba, ne da ake yi wa lakabi da suna “Prince of Monaco,” Ikpeba ya samu shiga ne bayan ya taimaka wa kungiyar Monaco ta samu nasarar lashe kofin Ligue 1 ta Faransa. Danwasan ya samu kuri’a 2, inda ya kare a mataki na 32 a cikin jerin wadanda suka samu karramawa a shekarar ta 1997.

ADEMOLA LOOKMAN – 2024

A kakar bara, wanda ya lashe gwarzon dan kwallon kafa na Afirka, Ademola Lukman, wanda a lokacin yake buga wasa a kungiyar Atalanta ne ya zo na 14 a bikin karramawar. Lookman ya lashe gasar Europa da Atalanta, inda ya zura kwallo uku rigis a raga, sannan ya taka rawar gani sosai a gasar cin kofin Afirka.

FINIDI GEORGE – 1995

Finidi George danwasan Nijeriya ne da ya yi tashe sosai a shekarun baya a Nijeriya da kungiyoyin Turai. Ya samu shiga cikin zaratan ‘yankwallo na duniya ne a shekarar 1995 bayan nasarar da ya samu a kungiyar Ajad ta Holland, inda ya samu shiga cikin jerin bayan an fadada karramawar zuwa kasahen da ba na turai ba.

A gasar Champions League ta shekarar 1995, Finidi ya zura kwallo tara, sannan ya bayar aka zura kwallo 11 kuma a shekarar ne Ajad ta lashe gasar Champions League da gasar Eredibisie ta kasar Holland da wasu kofuna uku. Amma a shekarar dan wasa Finidi ya kare a mataki na 21 a shekarar 1995.

BICTOR OSIMHEN – 2023

Danwasan kwallon gaba na Nijeriya wanda a yanzu haka yake buga wasa a kungiyar kwallon kafa ta Galatassary ya samu shiga ne bayan ya taimaka wa kungiyar Napoli wajen lashe gasar Serie A karon farko a shekara 33, sannan ya lashe wanda ya fi zura kwallo a shekarar ta 2023.

A shekarar ce Osimhen ya zo na takwas a duniya sannan kuma duka a shekarar dan wasa Bictor Osimhen shi ne ya lashe gwarzon dankwallon Afirka mafi kwarewa a shekarar 2023.

NWANKWO KANU – 1996 DA 1999

Shahararren dan wasa Nwankwo Kanu na cikin zaratan ‘yankwallo kafa ‘yan Nijeriya suka dade suna jan zarensu a harkar tamaula. A shekarar 1996, Kanu ya samu kuri’a 14, inda ya zo na 11 bayan ya lashe kofin Olympic da aka buga a Atlanta, da kuma rawar da ya taka a kungiyar Inter Milan ta Italiya.

Haka kuma a lokacin da ya koma Arsenal, tsohon kyaftin din na Nijeriya ya sake samun shiga, inda a shekarar 1999 ya zo na 23 a duniya. Sanan tsohon danwasan na Arsenal ya lashe karramawar gwarzon dankwallon Afirka sau biyu a shekarun 1996 da 1999.

ASISAT OSHOALA – 2022 DA 2023

Mace mai kamar maza, Asisat Oshoala ita ce ‘yarkwallon Nijeriya mace da ta fi lashe kambun gwarzuwar kwallon kafa ta Afirka. Sannan ita ce mace ta farko daga Nijeriya da ta fara shiga jerin wadanda aka karrama a Ballon d’Or ta mata. Bayan lashe gasar Champions League ne ta zama gwarzuwa ta 16 a duniya a shekarar 2022, sannan ta sake zuwa ta 20 a shekarar 2023.

CHIAMAKA NNADOZIE – 2025

A bikin karramawar ta bana kuma, mai tsaron ragar kungiyar Brighton & Hobe Albion ta Ingila, Chiamaka Nnadozie ce ta samu tagomashi, inda ta zo ta hudu a cikin masu tsaron raga mata a duniya, wanda shi ne matsayi mafi girma da Nijeriya ta taba samu a karramawar. Chiamaka Nnadozie ta lashe kofin gasar cin kofin Afirka na mata sau biyu a 2018 da 2024.

A Afirka dai an samu dan wasa George Weah, dan kasar Liberiya wanda ya taba lashe kyautar Ballon d’Or a duniya, kuma tun daga wancan lokacin har yanzu ba a sake samun wani dan wasa daga nahiyar Afirka ba da ya sake lashe kyautar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ballon D'Or
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Related

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya
Wasanni

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

3 hours ago
Ƴar Wasan Gaban Nijeriya, Ifeoma Onumonu Ta Yi Ritaya
Wasanni

Ƴar Wasan Gaban Nijeriya, Ifeoma Onumonu Ta Yi Ritaya

6 hours ago
Lamine Yamal Zai Shafe Mako 3 Yana Jinya
Wasanni

Lamine Yamal Zai Shafe Mako 3 Yana Jinya

1 day ago
PSG Ta Doke Barcelona Har Gida A Gasar Zakarun Turai
Wasanni

PSG Ta Doke Barcelona Har Gida A Gasar Zakarun Turai

3 days ago
Mbappe Ya Jefa Kwallonsa Ta 60 A Gasar Zakarun Turai A Wasan Da Real Madrid Ta Doke Kairat 
Wasanni

Mbappe Ya Jefa Kwallonsa Ta 60 A Gasar Zakarun Turai A Wasan Da Real Madrid Ta Doke Kairat 

3 days ago
Kofin Duniya: FIFA Ta Zabtarewa Afirka Ta Kudu Maki Uku
Wasanni

Kofin Duniya: FIFA Ta Zabtarewa Afirka Ta Kudu Maki Uku

5 days ago

LABARAI MASU NASABA

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

October 4, 2025
An Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana

An Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.