• English
  • Business News
Monday, August 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kokarin Farfado Da Ilimi: Gwamnan Kano Ya Zama Gwarzo A Tsakanin Gwamnoni

by Abdullahi Muh'd Sheka
10 months ago
in Labarai
0
Ilimi: Gwamna Yusuf Ya Raba Wa Makarantun Kano Kujerun Zama 73,000
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf na ci gaba da karbar gwababan lambobin yabo wadda ke alamta nagarta da jajircewarsa wajen bunkasa harkokin ilimi da tsantsenin lalitar al’ummar Kano inda wannan ne babban dalilin da Kanawa ke kiransa da sunan “A kori jahilci”.

Gwamna Abba Kabir Yusuf na cikin gwamnoni shida da suka rabauta da babbar lambar yabo daga kungiyar Malamai ta Kasa tare da hadin guiwa da ma’aikatar ilimi ta Tarayya a lokacin bikin ranar malamai ta duniya da aka gudanar a babban filin taron Eagle Skuare da ke Abuja.

  • Hadarin Kwale-kwale A Kaiama: Gwamnan Jihar Kwara Ya Bayar Da Tallafin Naira Miliyan 100
  • Ba Mijina Ba Ne Sanadin Ƙuncin Rayuwa Da Ake Ciki A Nijeriya – Uwargidan Shugaban Ƙasa

Inda aka karrama Gwamna Abba da lamba mafi daraja bisa kyakkyawar nasarar da ya samu ta fuskar inganta harkar ilimi. Kamar yadda mai magana da yawun Gwamnan Sanusi Bature Dawakin Tofa ya bayyana wa LEADERSHIP Hausa

Jajircewa tare da sadaukar da kan Gwamna Abba ne ya ja hankalin kungiyar Malaman tare da hadin guiwar Ma’aikatar ilimi ta tarayya wajen zabo shi domin ba shi wannan lamba musamman matakinsa na Sanya wa harkar ilimi dokar ta-baci tare da kafa manyan kwamitoci domin magance matsalar da ta jima tana ci wa harkar ilimi a tuwo a kwarya a Kano. Musamman tsarin tallafa wa malamai tare da kyautata walwalarsu.

Wani abu da ke daukar hankalin duk wani mai rajin kishin ganin an farfado da harkar ilimi a Kano shi ne yadda gwamnan bai tsaya ilimin zamani ba kawai, har makarantun tsangayu da islamiyyu ya saka cikin jadawalin inganta harkar ilimin baki daya.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

Domin ganin aniyarsa ta sake farfado da harkar ilimi ta kai inda yake fata, Gwamna Abba a kasafin kudin wannan shekara ta 2024, ya tabbatar da gabib sashin ilimi ne ya rabauta da kaso mafi tsoka domin tabbatar da cimma nasara. Musamman shirinsa na kara gina ajujuwa, zuba kayan zama da raba kayan koyo da koyarwa ga daukacin makarantun Jihar Kano.

Irin wadannan ayyuka ne Gwamna Abba ya alkawarta wa Kanawa kuma gashi tun kafin a yi rabin wa’adi kwalliya tana biya kudin sabulu.

A halin da ake ciki, tsohon Gwamnan Jihar Kano kuma Jagoran Jam’iyyar NNPPFormer, Rabi’u Musa Kwankwaso ya taya Gwamna Abba Kabir Yusuf murnar samun lambar yabo mafi daraja daga Kungiyar Malaman Makaranta ta Kasa (NUT), bisa hobbasar da yake yi wajen bunkasa sashen ilimi.

Kwankwaso ya bayyana hakan ne a shafinsa na D (da aka fi sani da Twitter a baya), inda ya nunar da cewa hakika, Gwamna Abba ya nuna sadaukarwa ga farfado da sashen ilimi na Jihar Kano inda ya bukaci ya kara kaimi a kan hakan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Abba Kabir YusufGwamnaGwarzoIlimikano
ShareTweetSendShare
Previous Post

Rikicin PDP: Kotu Ta shiga Tsakani, Ta Hana Tsige Damagun

Next Post

Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

1 hour ago
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe
Ra'ayi Riga

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

2 hours ago
Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano
Manyan Labarai

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

2 hours ago
Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara
Labarai

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

4 hours ago
Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa
Labarai

Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa

4 hours ago
Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule
Labarai

Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule

5 hours ago
Next Post
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

August 4, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

August 4, 2025
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

August 4, 2025
Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

August 4, 2025
Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

August 4, 2025
Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa

Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa

August 4, 2025
Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule

Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule

August 4, 2025
Tsohon Dan Majalisar Taraba Usman Ya Fice Daga APC

Tsohon Dan Majalisar Taraba Usman Ya Fice Daga APC

August 4, 2025
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane Da Dama A Kauyukan Zamfara

August 4, 2025
Gwamnatin Kano Za Ta Mayar Da Gidan Gyaran Hali Na Kurmawa Gidan Tarihi

Gwamnatin Kano Za Ta Mayar Da Gidan Gyaran Hali Na Kurmawa Gidan Tarihi

August 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.