• English
  • Business News
Tuesday, October 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kokarin Farfado Da Ilimi: Gwamnan Kano Ya Zama Gwarzo A Tsakanin Gwamnoni

by Abdullahi Muh'd Sheka
1 year ago
Ilimi

Gwamnan Jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf na ci gaba da karbar gwababan lambobin yabo wadda ke alamta nagarta da jajircewarsa wajen bunkasa harkokin ilimi da tsantsenin lalitar al’ummar Kano inda wannan ne babban dalilin da Kanawa ke kiransa da sunan “A kori jahilci”.

Gwamna Abba Kabir Yusuf na cikin gwamnoni shida da suka rabauta da babbar lambar yabo daga kungiyar Malamai ta Kasa tare da hadin guiwa da ma’aikatar ilimi ta Tarayya a lokacin bikin ranar malamai ta duniya da aka gudanar a babban filin taron Eagle Skuare da ke Abuja.

  • Hadarin Kwale-kwale A Kaiama: Gwamnan Jihar Kwara Ya Bayar Da Tallafin Naira Miliyan 100
  • Ba Mijina Ba Ne Sanadin Ƙuncin Rayuwa Da Ake Ciki A Nijeriya – Uwargidan Shugaban Ƙasa

Inda aka karrama Gwamna Abba da lamba mafi daraja bisa kyakkyawar nasarar da ya samu ta fuskar inganta harkar ilimi. Kamar yadda mai magana da yawun Gwamnan Sanusi Bature Dawakin Tofa ya bayyana wa LEADERSHIP Hausa

Jajircewa tare da sadaukar da kan Gwamna Abba ne ya ja hankalin kungiyar Malaman tare da hadin guiwar Ma’aikatar ilimi ta tarayya wajen zabo shi domin ba shi wannan lamba musamman matakinsa na Sanya wa harkar ilimi dokar ta-baci tare da kafa manyan kwamitoci domin magance matsalar da ta jima tana ci wa harkar ilimi a tuwo a kwarya a Kano. Musamman tsarin tallafa wa malamai tare da kyautata walwalarsu.

Wani abu da ke daukar hankalin duk wani mai rajin kishin ganin an farfado da harkar ilimi a Kano shi ne yadda gwamnan bai tsaya ilimin zamani ba kawai, har makarantun tsangayu da islamiyyu ya saka cikin jadawalin inganta harkar ilimin baki daya.

LABARAI MASU NASABA

An Ɗage Shari’ar Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Zuwa 19 Ga Watan Nuwamba

Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

Domin ganin aniyarsa ta sake farfado da harkar ilimi ta kai inda yake fata, Gwamna Abba a kasafin kudin wannan shekara ta 2024, ya tabbatar da gabib sashin ilimi ne ya rabauta da kaso mafi tsoka domin tabbatar da cimma nasara. Musamman shirinsa na kara gina ajujuwa, zuba kayan zama da raba kayan koyo da koyarwa ga daukacin makarantun Jihar Kano.

Irin wadannan ayyuka ne Gwamna Abba ya alkawarta wa Kanawa kuma gashi tun kafin a yi rabin wa’adi kwalliya tana biya kudin sabulu.

A halin da ake ciki, tsohon Gwamnan Jihar Kano kuma Jagoran Jam’iyyar NNPPFormer, Rabi’u Musa Kwankwaso ya taya Gwamna Abba Kabir Yusuf murnar samun lambar yabo mafi daraja daga Kungiyar Malaman Makaranta ta Kasa (NUT), bisa hobbasar da yake yi wajen bunkasa sashen ilimi.

Kwankwaso ya bayyana hakan ne a shafinsa na D (da aka fi sani da Twitter a baya), inda ya nunar da cewa hakika, Gwamna Abba ya nuna sadaukarwa ga farfado da sashen ilimi na Jihar Kano inda ya bukaci ya kara kaimi a kan hakan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Ɗage Shari’ar Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Zuwa 19 Ga Watan Nuwamba
Manyan Labarai

An Ɗage Shari’ar Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Zuwa 19 Ga Watan Nuwamba

October 21, 2025
Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa
Ra'ayi Riga

Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

October 21, 2025
Mutane 3,433 Sun Rasu a Hatsarin Mota 6,858 Cikin Wata 9 A Nijeriya – FRSC
Labarai

Mutane 3,433 Sun Rasu a Hatsarin Mota 6,858 Cikin Wata 9 A Nijeriya – FRSC

October 21, 2025
Next Post
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

LABARAI MASU NASABA

Babu Rikici A Jam’iyyar APC A Nasarawa — Shugaban Jam’iyya

Babu Rikici A Jam’iyyar APC A Nasarawa — Shugaban Jam’iyya

October 21, 2025
An Ɗage Shari’ar Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Zuwa 19 Ga Watan Nuwamba

An Ɗage Shari’ar Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Zuwa 19 Ga Watan Nuwamba

October 21, 2025
Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

October 21, 2025
Mutane 3,433 Sun Rasu a Hatsarin Mota 6,858 Cikin Wata 9 A Nijeriya – FRSC

Mutane 3,433 Sun Rasu a Hatsarin Mota 6,858 Cikin Wata 9 A Nijeriya – FRSC

October 21, 2025
NLC Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Don Biyan Buƙatun ASUU Da Sauran Ƙungiyoyi 

NLC Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Don Biyan Buƙatun ASUU Da Sauran Ƙungiyoyi 

October 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Ɗan Fashi Sanye Da Kayan NYSC A Enugu

October 21, 2025
Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

October 21, 2025
Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

October 20, 2025
An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

October 20, 2025
Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

October 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.