• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kokarin Jihohi Na Cin Gajiyar Albarkatun Ma’adanai: Dobi Ga Jihar Kaduna

byBello Hamza
2 years ago
Kaduna

Yuwancin jihohin kasar nan da Allah ya albarkata da dimbin ma’adanai daban-daban sun kasa fito da hanyoyin cin gajiyarsu ta yadda al’umma jihohin za su amfana.

Masana nada ra’ayin cewa, in har da za a tatsi wadannan ma’adanai yadda ya kamata lallai zai taimaka wajen bunkaska tattalin al’umma ya kuma rage yadda jihohi ke dogaro da kudaden da gwamnatin tarayya kr rarraba musu daga asusu arzikin kasa, wanda da hakan ya bayar da damar gudanar da ayyukan ci gaban al’umma a cikin sauki.

  • DSS Sun Cafke Dan Jarida A Filin Jirgin Sama Akan Hanyarsa Ta Zuwa Umrah Daga Kano
  • Gwamna Uba Sani Ya Taya Kansa Murna Da Hukuncin Da Kotun Zaben Kaduna Ta Yanke

A tsawon shekaru, gwamnatocin jihohi suna kokawa a kan yadda wasu dokoki suke takura musu amfana daga albarkatun ma’adanmai da k ea jihohin nasu, musamman dokar da ta bai wa gwamnatin tarayya mallakin albarkatun kasa a duk inda suke a fadin tarayyar kasar nan.

Kudin tsarin mulkin Nijeriya na shekarar 1999 (wadda aka yi wa kwaskwarima), sashi na 44 (3) banagare na 39 ta bai wa gamnatin tarayya mallakin dukkan albarkatun kasa don ta yi amfani da su wajen inganta rayuwar al’umma.

Haka kuma dokar ma’adanai da hakarsa ta Nijeriya na shekarar 2007 a sashi na 1 (1) ya kara tabbatar da mallakar dukkan ma’adanai a fadin tarayyar kasar nan a matsayin mallakin gwamnatin tarayya.

LABARAI MASU NASABA

Bayan Shekara 20 Nijeriya Ta Sake Dawo Da Tsarin Bayar Da Hayar Kananan Jiragen Sama

Tashoshin Jiragen Ruwa Sun Samar Da Kashi 19.6 Na Fitar Da Kayan Da Ba Su Shafi Mai Ba—Dantsoho

Bincike ya nuna cewa a halin yanzu harkar hakar ma’adanai ba bisa ka’dida ba ya zama ruwan dare, lallai a kwai bukatar gwamnati a dukkan matakai su hada hannu don kawo karshen harkokin ‘yan kasashen waje wadanda suke hada baki na wasu bata gari a cikin shugabannin al’umma wajen sace albarkatun kasa.

Ayyukan masu hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba na faruwa ne a daidai lokacin da al’ummar jihohi ke rayuwa cikin matsanancin talauci, an kuma tabbatar da cewaa, harkar hakar ma’adanai na ta’azzara matsalar tsaro da ake fama da shi a cikin kasa da kasashe makwabta.

A Jihar Kaduna, Kamfanin Bunkasa harkokin Ma’adanai ‘Kaduna Mining Debelopment Company Limited’ ta ba kamfanoni 30 lasisin gudanar da harkokin hakar ma’adanai a fadin jihar, wadanda suka hada da lasisi 11 na masu hakar duwatsu da lasisi 21 na masu nema tare da hakar ma’adanai da suka hada da ‘Granite, Laterite, Gold, Tin, Columbite, Tantalite, Iron, Manganese, Garnet, Beryllium, Nickel, Platinum, Cobalt da Lithium a kananan hukumomi daban-daban a fadin jihar.

Sauran ma’adanan da ke samu a jihar Kaduna sun hada da ‘Cassiterite (tin-ore) a garin Kagoro da ke karamar hukumar Kaura da Kurmin Dangana a karamar hukumar Jaba, haka kuma ana samun Tantalite a kananan hukumomin Birnin Gwari, Kagoma, Kafanchan da sauran sassan jihar.

A na samun Columbite a Jema’a, Ikara, Sanga da karamar hukumar Jaba wanda ma’adanan suna da muhimmanci a wajen hada jirgin saman da wasu na’urori masu muhimmanci. Ma’adanin Bismuth da ake amfani da shi a masana’antar hada magunguna yana samuwa ne a yankin garuruwan Gimba da Kinkiba a karamar hukumar Soba da kuma Makarfi a karamar hukumar Makarfi. Haka kuma ana samun ‘Wolframite a yankin Banki da Tsaunin Giniya; Gwal kuma na shinfide a yankin Birnin Gwari, Giwa, da karamar hukumar Chikun; ana kuma samun ma’adanin Nickel a kauyen Dangoma da ke karamar hukumar Jema’a; yayin da ma’adanin ‘Gemstones, Amethyst, Akuamarine da Tourmaline ke shinfide a kusan dukkan kananan hukumomin jihar.

A ta bakin shugaban hukumar kula da harkokin ma’adanai ta Jihar Kaduna, Dakta Nura Sani, ya bayyana cewa, jihar na da albakatun ma’adana masu dinbin yawa kuma jihar ta kasance a kan gaba a bangaren mallakar ma’adanai a cikin jihohin kasar nan.

Ya kara da cewa, an yi fiye da shekara 100 ana harkokin hakar ma’adanbin Gwal a yankin Birnin Gwari. Ya ce, ana hakar ma’adin karfe a yankin kudancin Kaduna, Kubau da Lere.

Ya ce, jihar ta hada hannu da wasu kamfanonin hakar ma’adanai na kasashen waje inda suka zuba jarin fiye da Dala miliyan 600 don kafa kamfanin hakar ma’anin karfe a karamar hukumar Kagarko.

Ya kuma kara da cewa, jihar na a kan gaba a harkar ma’adanin ‘Lithium’ inda suka hada hannun da wani kamfanin kasa Sin a don hakar ma’adanin a kauyen Kangimi da kuma wani hadin gwiwar da kasar Australian a hakar ma’adanin ‘Jubita’.

Ya kuma kara da cewa a halin yanzau Jihar Kaduna ta zama kan gaba a harkokin hakar ma’adanin “Gemstones’ da “Safayers” ana kuma shirin ganin gwamnati ta zuba jari don ganin al’ummun yankin sun amfana yadda ya kamata.

“Jihar Kaduna da shirya tsaf don samar da hanyoyin amfana daga ma’adanai masu muhimmanci da Allah ya albarkaci jiharmu da su, kamar ‘Amethyst a yankin Ikara, da “Lithium, a yankin Kurega da Manini. Haka kuma kamfanonin kasa Hong Kong sun shigo don hada hannun da mu a bangaren hakar ma’adanin “Tin mining’ a garin Gidan Waya da ke karamar hukumar Jema’a.” in ji shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bayan Shekara 20 Nijeriya Ta Sake Dawo Da Tsarin Bayar Da Hayar Kananan Jiragen Sama
Tattalin Arziki

Bayan Shekara 20 Nijeriya Ta Sake Dawo Da Tsarin Bayar Da Hayar Kananan Jiragen Sama

October 3, 2025
Tashoshin Jiragen Ruwa Sun Samar Da Kashi 19.6 Na Fitar Da Kayan Da Ba Su Shafi Mai Ba—Dantsoho
Tattalin Arziki

Tashoshin Jiragen Ruwa Sun Samar Da Kashi 19.6 Na Fitar Da Kayan Da Ba Su Shafi Mai Ba—Dantsoho

October 3, 2025
Majalisar Wakilai Za Ta Sasanta Dangote Da NUPENG
Tattalin Arziki

Majalisar Wakilai Za Ta Sasanta Dangote Da NUPENG

September 27, 2025
Next Post
Yadda Bankuna Suka Ci Bashin Naira Tiriliyan 3.03 Daga CBN A Cikin Kwana 22

Yadda Bankuna Suka Ci Bashin Naira Tiriliyan 3.03 Daga CBN A Cikin Kwana 22

LABARAI MASU NASABA

An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version