ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kokarin Jihohi Na Cin Gajiyar Albarkatun Ma’adanai: Dobi Ga Jihar Kaduna

by Bello Hamza
3 years ago
Kaduna

Yuwancin jihohin kasar nan da Allah ya albarkata da dimbin ma’adanai daban-daban sun kasa fito da hanyoyin cin gajiyarsu ta yadda al’umma jihohin za su amfana.

Masana nada ra’ayin cewa, in har da za a tatsi wadannan ma’adanai yadda ya kamata lallai zai taimaka wajen bunkaska tattalin al’umma ya kuma rage yadda jihohi ke dogaro da kudaden da gwamnatin tarayya kr rarraba musu daga asusu arzikin kasa, wanda da hakan ya bayar da damar gudanar da ayyukan ci gaban al’umma a cikin sauki.

  • DSS Sun Cafke Dan Jarida A Filin Jirgin Sama Akan Hanyarsa Ta Zuwa Umrah Daga Kano
  • Gwamna Uba Sani Ya Taya Kansa Murna Da Hukuncin Da Kotun Zaben Kaduna Ta Yanke

A tsawon shekaru, gwamnatocin jihohi suna kokawa a kan yadda wasu dokoki suke takura musu amfana daga albarkatun ma’adanmai da k ea jihohin nasu, musamman dokar da ta bai wa gwamnatin tarayya mallakin albarkatun kasa a duk inda suke a fadin tarayyar kasar nan.

ADVERTISEMENT

Kudin tsarin mulkin Nijeriya na shekarar 1999 (wadda aka yi wa kwaskwarima), sashi na 44 (3) banagare na 39 ta bai wa gamnatin tarayya mallakin dukkan albarkatun kasa don ta yi amfani da su wajen inganta rayuwar al’umma.

Haka kuma dokar ma’adanai da hakarsa ta Nijeriya na shekarar 2007 a sashi na 1 (1) ya kara tabbatar da mallakar dukkan ma’adanai a fadin tarayyar kasar nan a matsayin mallakin gwamnatin tarayya.

LABARAI MASU NASABA

Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

Bincike ya nuna cewa a halin yanzu harkar hakar ma’adanai ba bisa ka’dida ba ya zama ruwan dare, lallai a kwai bukatar gwamnati a dukkan matakai su hada hannu don kawo karshen harkokin ‘yan kasashen waje wadanda suke hada baki na wasu bata gari a cikin shugabannin al’umma wajen sace albarkatun kasa.

Ayyukan masu hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba na faruwa ne a daidai lokacin da al’ummar jihohi ke rayuwa cikin matsanancin talauci, an kuma tabbatar da cewaa, harkar hakar ma’adanai na ta’azzara matsalar tsaro da ake fama da shi a cikin kasa da kasashe makwabta.

A Jihar Kaduna, Kamfanin Bunkasa harkokin Ma’adanai ‘Kaduna Mining Debelopment Company Limited’ ta ba kamfanoni 30 lasisin gudanar da harkokin hakar ma’adanai a fadin jihar, wadanda suka hada da lasisi 11 na masu hakar duwatsu da lasisi 21 na masu nema tare da hakar ma’adanai da suka hada da ‘Granite, Laterite, Gold, Tin, Columbite, Tantalite, Iron, Manganese, Garnet, Beryllium, Nickel, Platinum, Cobalt da Lithium a kananan hukumomi daban-daban a fadin jihar.

Sauran ma’adanan da ke samu a jihar Kaduna sun hada da ‘Cassiterite (tin-ore) a garin Kagoro da ke karamar hukumar Kaura da Kurmin Dangana a karamar hukumar Jaba, haka kuma ana samun Tantalite a kananan hukumomin Birnin Gwari, Kagoma, Kafanchan da sauran sassan jihar.

A na samun Columbite a Jema’a, Ikara, Sanga da karamar hukumar Jaba wanda ma’adanan suna da muhimmanci a wajen hada jirgin saman da wasu na’urori masu muhimmanci. Ma’adanin Bismuth da ake amfani da shi a masana’antar hada magunguna yana samuwa ne a yankin garuruwan Gimba da Kinkiba a karamar hukumar Soba da kuma Makarfi a karamar hukumar Makarfi. Haka kuma ana samun ‘Wolframite a yankin Banki da Tsaunin Giniya; Gwal kuma na shinfide a yankin Birnin Gwari, Giwa, da karamar hukumar Chikun; ana kuma samun ma’adanin Nickel a kauyen Dangoma da ke karamar hukumar Jema’a; yayin da ma’adanin ‘Gemstones, Amethyst, Akuamarine da Tourmaline ke shinfide a kusan dukkan kananan hukumomin jihar.

A ta bakin shugaban hukumar kula da harkokin ma’adanai ta Jihar Kaduna, Dakta Nura Sani, ya bayyana cewa, jihar na da albakatun ma’adana masu dinbin yawa kuma jihar ta kasance a kan gaba a bangaren mallakar ma’adanai a cikin jihohin kasar nan.

Ya kara da cewa, an yi fiye da shekara 100 ana harkokin hakar ma’adanbin Gwal a yankin Birnin Gwari. Ya ce, ana hakar ma’adin karfe a yankin kudancin Kaduna, Kubau da Lere.

Ya ce, jihar ta hada hannu da wasu kamfanonin hakar ma’adanai na kasashen waje inda suka zuba jarin fiye da Dala miliyan 600 don kafa kamfanin hakar ma’anin karfe a karamar hukumar Kagarko.

Ya kuma kara da cewa, jihar na a kan gaba a harkar ma’adanin ‘Lithium’ inda suka hada hannun da wani kamfanin kasa Sin a don hakar ma’adanin a kauyen Kangimi da kuma wani hadin gwiwar da kasar Australian a hakar ma’adanin ‘Jubita’.

Ya kuma kara da cewa a halin yanzau Jihar Kaduna ta zama kan gaba a harkokin hakar ma’adanin “Gemstones’ da “Safayers” ana kuma shirin ganin gwamnati ta zuba jari don ganin al’ummun yankin sun amfana yadda ya kamata.

“Jihar Kaduna da shirya tsaf don samar da hanyoyin amfana daga ma’adanai masu muhimmanci da Allah ya albarkaci jiharmu da su, kamar ‘Amethyst a yankin Ikara, da “Lithium, a yankin Kurega da Manini. Haka kuma kamfanonin kasa Hong Kong sun shigo don hada hannun da mu a bangaren hakar ma’adanin “Tin mining’ a garin Gidan Waya da ke karamar hukumar Jema’a.” in ji shi.

Kaduna
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Tattalin Arziki

Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

July 11, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN
Tattalin Arziki

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

June 27, 2026
Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani
Tattalin Arziki

Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

June 26, 2026
Next Post
Yadda Bankuna Suka Ci Bashin Naira Tiriliyan 3.03 Daga CBN A Cikin Kwana 22

Yadda Bankuna Suka Ci Bashin Naira Tiriliyan 3.03 Daga CBN A Cikin Kwana 22

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.