• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Ɗaure Hadimin Tambuwal Kan Yaɗa Bidiyon Da Ake Yi Wa Matar Gwamnan Sakkwato Liƙi Da Dala

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto and Sulaiman
9 months ago
in Labarai
0
Kotu Ta Ɗaure Hadimin Tambuwal Kan Yaɗa Bidiyon Da Ake Yi Wa Matar Gwamnan Sakkwato Liƙi Da Dala
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kotun majistare ta daya da ke Sakkwato a ranar Litinin ta tura mataimaki na musamman ga Sanata Aminu Waziri Tambuwal, mai suna Shafi’u Umar Tureta gidan gyaran hali kan yada bidiyon matar Gwamna Ahmed Aliyu a yayin da ake yi mata liki da dala.

 

Mai shari’a Fatima Hassan ce ta yanke hukuncin tsare matashin mai shekaru 36 har zuwa ranar 6 ga Satumba inda za a yanke hukunci kan yiwuwar bayar da belinsa kan laifin batancin. Sai dai kuma, an hana manema labarai halartar zaman kotun a yayin yanke hukuncin na farko.

  • Abba Ya Gabatar Da Kwarya-kwaryar Kasafin Kudi Na Naira Biliyan 99 Ga Majalisar Kano
  • A Shirye Sin Take Ta Ci Gaba Da Yin Hadin Gwiwa Tare Da Kasashen Afirka Wajen Sa Kaimi Ga Inganta Shirin Rage Talauci

Takardar shigar da karar ta bayyana cewa, matashin a ranar 18/7/2023 ya yada bidiyon matar Gwamna, Fatima Ahmed Aliyu a yayin da take bikin zagayowar ranar haihuwarta, sannan ya kara da cewa, ta na almubbazaranci da liki da kashe kudade a yayin da al’umma ke cikin yunwa.

 

Labarai Masu Nasaba

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

Bugu da kari, ana tuhumar matashin da laifin sanya tsohuwar takardar kammala makarantar sakandiren Gwamna Aliyu da sakamakon gazawa (F9) tare da kiran sa bakauye wanda bai iya magana da turanci ba, laifukan da dansanda mai shigar da kara, Abdurrahman Mansur ya ce, sun sabawa kundin dokar penal code ta jihar ta 2019 sashe na 378 da 379.

 

Sai dai jam’iyyar PDP a jihar, ta bukaci a gaggauta sakin matashin, inda ta ce, ba Shafi’u ne ya dauki bidiyon da Gwamnan ke turancin ba, saboda ba shi da wata alaka ta shiga gidan gwamnati inda aka dauki bidiyon, haka kuma, bai halarci wurin bikin zagayowar ranar haihuwar matar gwamnan ba, don haka, ba inda zai samu bidiyoyin sai ta hanyar makusantan gwamnan da iyalansa da suka yada.

 

Kakakin jam’iyyar, Hassan Sahabi Sanyinnawal ya bayyana cewar, mulkin kama-karya ne gwamnatin Sakkwato ke yi tare da kokarin cin zarafin ‘yan adawa ko ‘yan PDP, domin hakan rashin adalci ne kuma ba za su zuba ido a na cin zarafin magoya bayan su ba.

 

A nata bangaren, kungiyar kare hakkin dan’Adam ta ‘Amnesty International’ ta bi sahun wadanda suka soki lamarin, inda ta ce, kama matashin ya sabawa ‘yancin dan’Adam, don haka, ta yi Allah-wadai da kamen tare da kiran a gaggauta sakinsa.

 

Kungiyar ta ce, maimakon kama matashin, kamata ya yi, gwamnatin ta bayar da fifiko ga magance matsalolin fatara, yaran da ba su zuwa makaranta da ke gararanba kan tituna da yawaitar matsalar tsaro da ta kassara gabashin jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnatin APCKuncin rayuwaTabarbarewar tsaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wang Yi Da Jake Sullivan Sun Gudanar Da Sabon Zagaye Na Muhimmin Tattaunawa Tsakanin Sin Da Amurka

Next Post

Yawan Ribar Da Masana’Antu Masu Matsakaicin Kudin Shiga Suka Samu Ya Karu Da Kashi 3.6% A Farkon Watanni 7 Na Bana

Related

JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

14 minutes ago
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka
Ra'ayi Riga

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

1 hour ago
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata
Labarai

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

3 hours ago
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

5 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

7 hours ago
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa
Labarai

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

8 hours ago
Next Post
Yawan Ribar Da Masana’Antu Masu Matsakaicin Kudin Shiga Suka Samu Ya Karu Da Kashi 3.6% A Farkon Watanni 7 Na Bana

Yawan Ribar Da Masana’Antu Masu Matsakaicin Kudin Shiga Suka Samu Ya Karu Da Kashi 3.6% A Farkon Watanni 7 Na Bana

LABARAI MASU NASABA

JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

May 14, 2025
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

May 14, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

May 14, 2025
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

May 14, 2025
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

May 14, 2025
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.