ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abba Ya Gabatar Da Kwarya-kwaryar Kasafin Kudi Na Naira Biliyan 99 Ga Majalisar Kano

by Naziru Adam Ibrahim
2 years ago
Kasafin Kudi

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya rubuta wa majalisar dokokin jihar takardar neman amincewarta da kasafin kudin shekarar 2024 na karin kudi, N99, 221,503,569.90.

Bukatar gwamnan na kunshe ne cikin wata wasiƙa da aka karanta a zauren majalisar a yayin zaman da shugaban majalisar, Ismail Falgore ya jagoranta.

  • Ambaliya Ta Yi Ajalin Mutane 49 A Arewa Maso Gabas – NEMA
  • Gwamnan Nasir Ya Kaddamar Da Rabon Tallafin Naira Biliyan 6.5 Ga Mutane 65,000 A Kebbi

Yayin da yake karanta wasikar, Falgore ya bayyana cewa gwamnan yana neman amincewarsu ne bisa bin sashe na 122 (A da B) na kundin tsarin mulkin ƙasar nan na 1999, don ƙara kaimi da aiwatar da ayyukan da suka sa gaba na inganta rayuwar al’ummar jihar.

ADVERTISEMENT

Ya kuma bayyana cewa, daga cikin kasafin kudin, an ware kimanin Naira biliyan 34 na kudin ma’aikata da wata 35 na shirin ko ta kwana da kuma na sama da biliyan 31 don gudanar da ayyuuka.

Da yake zantawa da manema labarai bayan gabatar da wasikar ga majalisar, kwamishinan tsare-tsare da kasafin kudi na jihar, Musa Shanono, ya ce, kasafin farko na jihar na 2024 ya kai Naira biliyan 438 idan an hada da wannan karin kasafin da ake neman amincewa da shi a doka, zai kawo kasafin 2024 zuwa naira biliyan 537.

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Yayin da yake nanata kudirin gwamnatin na mayar da hankali kan raya ababen more rayuwa da bunkasa walwala da ma inganta fannin lafiya da ilimi, Shanono ya jaddada cewa ƙarin kasafin kudin zai kunshi sabon mafi karancin albashi da dai sauransu.

Shi ma ɗan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Nassarawa Yusuf Aliyu, ya nemi goyon bayan sauran ‘yan majalisar don yin kira ga Gwamna Yusuf da ya gyara tare da sake gina filin wasa na Gwagwarwa da ke unguwar Gawuna a ƙaramar hukumar Nassarawa, don yakar ta’addancin da ake samu da safarar miyagun kwayoyi a filin wasan, da rashin tsaro a tsakanin al’umma.

A cewar Aliyu, mummunan halin da filin wasan ke ciki ya sanya wajen ya koma mafakar bata gari kuma abin tsoro ga mazauna yankin wanda gyara shi zai inganta tsaron al’umma.

Kasafin Kudi
Naziru Adam Ibrahim
+ postsBio
  • Naziru Adam Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/naziru-adam-ibrahim/
    Ya Kamata Farashin Siminti Ya Sauka — Umahi Ga Masana’antun Siminti
  • Naziru Adam Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/naziru-adam-ibrahim/
    Yari Ya Dace Da Rayuwar Mulki Da Kasuwanci
  • Naziru Adam Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/naziru-adam-ibrahim/
    A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara
  • Naziru Adam Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/naziru-adam-ibrahim/
    Shugaba Tinubu Ya Isa Nairobi Domin Halartar Taron Tattalin Arzikin Nahiyar Afirka

MASU ALAKA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Next Post
Inganta Raya Shawarar BRI Zai Zama Daya Daga Manyan Batutuwan Da Za A Tattauna A Gun Taron Kolin FOCAC Na Bana

Inganta Raya Shawarar BRI Zai Zama Daya Daga Manyan Batutuwan Da Za A Tattauna A Gun Taron Kolin FOCAC Na Bana

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.