• English
  • Business News
Saturday, August 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Ci Tarar ‘Yansanda Naira Miliyan 300 Kan Kisan ‘Yan Shi’a A Zariya

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
'yansanda
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata Babbar Kotun Tarayya da ke zamanta a Kaduna ta umurci hukumomin ‘yansanda da su biya zunzurutun kudi Naira miliyan 300 ga iyayen ‘yan Shi’a uku da ake zargin jami’anta sun kashe a lokacin da suke gudanar da muzahara a shekarar 2022 a Zariya.

Mai shari’a Hawa Buhari, a cikin hukuncin da ta yanke, ta ce “masu neman hakkokinsu kamar yadda doka ta yi umarnin a ba su a cikin sashe na 33, 38, 39, 40, 42 da 46 na kundin tsarin mulkin 1999 (da aka gyara); Umarni na 2, Dokoki na 1, 2, 3, 4, 11 da 12 na Dokokin Kare Hakki da nuna Mahimmanci (Tasirin Tilastawa) da tsarin Dokokin 2009; ya yi nuni da cewa; Ana aiwatar da doka ta 4, 8, 10, 11 da 12 na Yarjejeniya Ta Afirka ta 2004 game da ‘yancin dan’Adam da jama’a.”
Alkalin kotun ta ce adadin Naira miliyan 100 da ya zama dole a biya ga kowane iyayen mamacin, inda za a biya jimillar Naira miliyan 300, a matsayin diyya, sannan kuma gamayyar diyyar, za a rika samar da riba ta kashi 10 cikin 100 a duk shekara har sai an biya kudaden.

  • Wani Dansanda Mai Rakiyar Jirgin Kasan Kaduna Zuwa Abuja Ya Rasu Acikin Jirgin
  • Kotu Ta Hana ‘Yansanda Kama Shugabannin Jam’iyyar APC Da Suka Dakatar Da Ganduje A Kano

Mai shari’a Buhari, a hukuncin da ta yanke a ranar 22 ga Afrilu, 2024, tare da kwafin na hukuncin da aka bai wa manema labarai ranar Lahadi a Abuja, ya karfafa kararraki guda uku da makusantan mamatan uku suka shigar.

“Za a ba wa kowane iyayen mamaci Kudi Naira miliyan 100,000,000.00 a matsayin diyya da kuma jimillar diyyar za ta zama tare da ribar kashi 10 a duk shekara har sai an cika adadin.

“Wadanda aka yi kara za su nemi afuwar masu kara a bainar jama’a kowace rana saboda keta haddinsu da suka yi,” in ji ta.

Labarai Masu Nasaba

An Yanke Wa Mai Gadi Da Mai Dafa Abinci Hukuncin Kisa Kan Kashe Tsohon Kwamishina A Katsina

‘Yansanda Sun Damke Mutum Shida Kan Kisan Da Aka Yi A Kasuwar Abuja

Za a iya tunawa cewa mutane uku ne da suka hada da; Magaji Yusuf, Muhammad Lawal da Aliyu Badamasi sun shigar da kara mai lamba: FHC/KH/KD/138/2022, FHC/KH/KD/140/2022 da FHC/KH/KD/146/2022 a gaban kotun.
Sun yi zargin cewa a ranar 8 ga Agusta, 2022, jami’an ‘yan sandan Nijeriya sun harbe Jafar Magaji, Aliyu Lawal da Muhsin Badamasi, a lokacin da suke gudanar da ibadarsu ta Muzaharar Ashura a Garin Zariya.

Sun kai karar Sufeto-Janar na ’yansanda (IGP), Mataimakin Sufeto-Janar na ’yansanda na shiyya ta 7, Kwamishinan ’Yansandan Jihar Kaduna, AC Surajo Fana (Kwamandan yankin Zariya), Ibrahim Zubairu (Jami’in ’Yansanda, Kasuwar Mata, Sabon Garin). Zaria Dibision), da Kasim Muhammad (DPO, Zaria City Dibision) a matsayin wadanda ake kara na 1 zuwa na 6.

Masu neman a gabatar da karar a ranar 26 ga Satumba, 2022 da kuma gabatarwa a ranar 26 ga Satumba, 2022, ta tawagar lauyoyinsu da suka hada da H.G Magashi, M.D Abubakar da Dokta Yusha’u Shaikh, da sauran mutum bakwai.

Sun nemi a bayyana cewa harbin da aka yi wa Jafar Magaji, Aliyu Lawal da Muhsin Badamasi a ranar da ake gudanar da muzaharar a matsayin abin da ya saba wa doka, kuma ya saba wa kundin tsarin mulkin kasa da kuma tauye hakkinsu na rayuwa kamar yadda sashe na 33 na kundin tsarin mulkin 1999 da sashe na 1999 ya tabbatar, da kuma Yarjejeniya 4 Ta Afirka Kan Hakkokin Dan’Adam da Jama’a Cap A9 LFN, 2004.

Don haka sun roki kotu da ta umarci wadanda ake kara tare da su biya su Naira miliyan 200 kowannensu saboda tauye hakkin ‘yan uwansu da suka rasu.

Haka kuma sun nemi oda, inda suka umurci wadanda ake kara da su rubuta takardar neman gafara ta hanyar bugawa a cikin jaridun kasar guda biyu da ke yawo a Arewacin Nijeriya.

Amma wadanda ake kara, a cikin kararsu ta farko mai kwanan wata da kuma gabatar da su a ranar 8 ga Nuwamba, 2022, sun nemi a ba da umarnin soke kararrakin ukun saboda rashin hukumci.

Bayan haka, sun kuma gabatar da takardar shaidar adawa da kara.

Sai dai mai shari’a Buhari ya amince da gabatar da lauyoyin wanda ya shigar da karar, kuma ya dauki hukumci kan lamarin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Rikicin 'Yan Shi'aRikicin Shugabanci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaban Serbia: Kullum shugaba Xi Jinping Ya Cika Alkawarinsa

Next Post

An Gabatar Da Rahoto Dangane Da Hadin Gwiwar Da Kasar Sin Da Kasashen Turai Suke Yi A Fannin Kare Muhalli

Related

An Yanke Wa Mai Gadi Da Mai Dafa Abinci Hukuncin Kisa Kan Kashe Tsohon Kwamishina A Katsina
Kotu Da Ɗansanda

An Yanke Wa Mai Gadi Da Mai Dafa Abinci Hukuncin Kisa Kan Kashe Tsohon Kwamishina A Katsina

2 days ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Damke Mutum Shida Kan Kisan Da Aka Yi A Kasuwar Abuja

3 weeks ago
Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa
Kotu Da Ɗansanda

Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa

3 weeks ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

4 weeks ago
‘Yan Sanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Jefe Wani Direba Har Lahira A Ondo
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

2 months ago
Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe
Kotu Da Ɗansanda

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

2 months ago
Next Post
An Gabatar Da Rahoto Dangane Da Hadin Gwiwar Da Kasar Sin Da Kasashen Turai Suke Yi A Fannin Kare Muhalli

An Gabatar Da Rahoto Dangane Da Hadin Gwiwar Da Kasar Sin Da Kasashen Turai Suke Yi A Fannin Kare Muhalli

LABARAI MASU NASABA

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

August 1, 2025
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

August 1, 2025
2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

August 1, 2025
Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

August 1, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

August 1, 2025
Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

August 1, 2025
Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

August 1, 2025
Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

August 1, 2025
Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

August 1, 2025
An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

August 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.