• English
  • Business News
Friday, October 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Kori Shugabannin PDP Da Ke Goyon Bayan Kwankwaso A Kano

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Kotu

Kotun daukaka kara da ke zamanta a Abuja a ranar Litinin ta jingine hukuncin da babban kotun tarayya ta yi na amincewa da Shehu Sagagi a matsayin shugaban jam’iyyar PDP a Jihar Kano.

Sagagi, wanda ke samun goyon bayan tsohon gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, wanda tuni ya fice daga jam’iyyar tare da zama dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar NNPP a halin yanzu.

  • Sojoji Sun Kashe Dan Ta’adda, Sun Kama Wasu 3 A Kaduna
  • Yadda Bidiyon Tsiraicina Ya Karade Shafukan Sada Zumunta – Safara’u

Wasu mambobin jam’iyyar dai sun jima suna zargin Sagagi da magoya bayansa da yin aikin goyon bayan mai gidansu a siyasa, Kwankwaso tare da yin saddu domin muradinsa ya cika.

A ranar 29 ga watan Maris ne kwamitin uwar jam’iyyar PDP na kasa, ya rushe shugabancin jam’iyyar a Jihar Kano tare da nada wasu kwamitin riko na mutane shida da zai maye gurbin wadanda aka rushe.

A ranar 25 ga watan Mayu, alkalin babbar kotun tarayya a Kano, Taiwo Taiwo, ya ba da umarnin hana uwar jam’iyyar PDP daga cire Sagagi a matsayin shugaba har sai wa’adin mulkinsa ya kare a watan Disambar 2024.

LABARAI MASU NASABA

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

Hukuncin kotun ya ce uwar jam’iyyar ba ta da ikon rushe shugabannin da suka zama shugabanni ta hanyar zabe.

Sai dai kuma kotun daukaka kara a ranar Litinin, ta rushe wannan hukuncin na babbar kotun tarayya, inda ta ce lamari ne na cikin gida don haka uwar jam’iyyar tana da cikakken ikon rushe shugabannin jam’iyyar a Jihar Kano.

Kotun daukaka karar ta zartar da hukuncin cewa uwar jam’iyyar ta kasa na da ikon rushe kwamitin shugabanni jam’iyyar na Jihar Kano.

Hukuncin da alkalan kotun daukaka karar su uku suka yanke, wanda ke karkashin jagorancin Peter Ige, ta ce matakin da uwar jam’iyyar ta dauka na rushe shugabannin jiha da na kananan hukumomin Jihar Kano tare da nada kwamitin riko bai dace a kalubalanci hakan a kotu ba domin ya saba wa dokar jam’iyyar PDP.

Kotun ta ce rushe da nada kwamitin riko da uwar jam’iyyar ta yi, ya gudana ne bisa amfani da sashen dokar 31 (2) (e) na jam’iyyar.

Hukuncin na kotun na zuwa ne daidai lokacin da tsohon gwamnan Jihar Kano Ibrahim Shekarau, ya sake komawa cikin jam’iyyar ta PDP, wanda ake kyautata zaton shi ne ma zai jagoranci jam’iyyar wajen tsare-tsaren zaben 2023 a jihar.

Kazalika, ana ganin wannan hukuncin zai kawo karshen rikicin cikin gida da ke faruwa a PDP a Kano kan waye dan takarar gwamna na jam’iyyar a tsakanin Muhammad Abacha, dan tsohon shugaban kasa, Sani Abacha da Sadiq Wali.

Shi dai Muhammad Abacha an zabe shi ne a karkashin jagorancin Sagagi yayin da shi kuma Sadiq Wali dan tsohon ministan harkokin kasashen waje, Aminu Wali uwar jam’iyyar ta zaba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 
Manyan Labarai

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

October 30, 2025
Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC
Manyan Labarai

Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

October 30, 2025
Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai

October 30, 2025
Next Post
Zan Fallasa ‘Yan Takarar Shugaban Kasar Da Burinsu Kawai Su Saci Kudi Ne — Wike

Zan Fallasa ‘Yan Takarar Shugaban Kasar Da Burinsu Kawai Su Saci Kudi Ne — Wike

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo

October 30, 2025
An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara

An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara

October 30, 2025
Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 

Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 

October 30, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutum Ɗaya, Sun Kama Mace Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Dajin Kwara 

October 30, 2025
Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC

Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC

October 30, 2025
Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray

Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray

October 30, 2025
Kasar Sin Ce Ke Da Sama Da Rabin Muhimman Makaloli Na Duniya

Kasar Sin Ce Ke Da Sama Da Rabin Muhimman Makaloli Na Duniya

October 30, 2025
Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai

Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai

October 30, 2025
Bunkasar Fannin Kirkire-Kirkiren Fasahohi Na Sin Alheri Ne Ga Dukkanin Duniya Ba Barazana Ba

Bunkasar Fannin Kirkire-Kirkiren Fasahohi Na Sin Alheri Ne Ga Dukkanin Duniya Ba Barazana Ba

October 30, 2025
Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

October 30, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.