• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Kori Shugabannin PDP Da Ke Goyon Bayan Kwankwaso A Kano

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Manyan Labarai, Siyasa
0
Kotu Ta Kori Shugabannin PDP Da Ke Goyon Bayan Kwankwaso A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kotun daukaka kara da ke zamanta a Abuja a ranar Litinin ta jingine hukuncin da babban kotun tarayya ta yi na amincewa da Shehu Sagagi a matsayin shugaban jam’iyyar PDP a Jihar Kano.

Sagagi, wanda ke samun goyon bayan tsohon gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, wanda tuni ya fice daga jam’iyyar tare da zama dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar NNPP a halin yanzu.

  • Sojoji Sun Kashe Dan Ta’adda, Sun Kama Wasu 3 A Kaduna
  • Yadda Bidiyon Tsiraicina Ya Karade Shafukan Sada Zumunta – Safara’u

Wasu mambobin jam’iyyar dai sun jima suna zargin Sagagi da magoya bayansa da yin aikin goyon bayan mai gidansu a siyasa, Kwankwaso tare da yin saddu domin muradinsa ya cika.

A ranar 29 ga watan Maris ne kwamitin uwar jam’iyyar PDP na kasa, ya rushe shugabancin jam’iyyar a Jihar Kano tare da nada wasu kwamitin riko na mutane shida da zai maye gurbin wadanda aka rushe.

A ranar 25 ga watan Mayu, alkalin babbar kotun tarayya a Kano, Taiwo Taiwo, ya ba da umarnin hana uwar jam’iyyar PDP daga cire Sagagi a matsayin shugaba har sai wa’adin mulkinsa ya kare a watan Disambar 2024.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Hukuncin kotun ya ce uwar jam’iyyar ba ta da ikon rushe shugabannin da suka zama shugabanni ta hanyar zabe.

Sai dai kuma kotun daukaka kara a ranar Litinin, ta rushe wannan hukuncin na babbar kotun tarayya, inda ta ce lamari ne na cikin gida don haka uwar jam’iyyar tana da cikakken ikon rushe shugabannin jam’iyyar a Jihar Kano.

Kotun daukaka karar ta zartar da hukuncin cewa uwar jam’iyyar ta kasa na da ikon rushe kwamitin shugabanni jam’iyyar na Jihar Kano.

Hukuncin da alkalan kotun daukaka karar su uku suka yanke, wanda ke karkashin jagorancin Peter Ige, ta ce matakin da uwar jam’iyyar ta dauka na rushe shugabannin jiha da na kananan hukumomin Jihar Kano tare da nada kwamitin riko bai dace a kalubalanci hakan a kotu ba domin ya saba wa dokar jam’iyyar PDP.

Kotun ta ce rushe da nada kwamitin riko da uwar jam’iyyar ta yi, ya gudana ne bisa amfani da sashen dokar 31 (2) (e) na jam’iyyar.

Hukuncin na kotun na zuwa ne daidai lokacin da tsohon gwamnan Jihar Kano Ibrahim Shekarau, ya sake komawa cikin jam’iyyar ta PDP, wanda ake kyautata zaton shi ne ma zai jagoranci jam’iyyar wajen tsare-tsaren zaben 2023 a jihar.

Kazalika, ana ganin wannan hukuncin zai kawo karshen rikicin cikin gida da ke faruwa a PDP a Kano kan waye dan takarar gwamna na jam’iyyar a tsakanin Muhammad Abacha, dan tsohon shugaban kasa, Sani Abacha da Sadiq Wali.

Shi dai Muhammad Abacha an zabe shi ne a karkashin jagorancin Sagagi yayin da shi kuma Sadiq Wali dan tsohon ministan harkokin kasashen waje, Aminu Wali uwar jam’iyyar ta zaba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HukuncikanoKituKwankwasoPDPRikicin Cikin GidaSagagiShekarauSiyasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hukumar Gidan Yarin Kuje Ta Tabbatar Da Mutuwar Fursuna A Gidan Yarin Kuje

Next Post

Zan Fallasa ‘Yan Takarar Shugaban Kasar Da Burinsu Kawai Su Saci Kudi Ne — Wike

Related

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

6 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

20 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

22 hours ago
Rasuwar ÆŠantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar ÆŠantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

1 day ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

1 day ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Manyan Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

1 day ago
Next Post
Zan Fallasa ‘Yan Takarar Shugaban Kasar Da Burinsu Kawai Su Saci Kudi Ne — Wike

Zan Fallasa ‘Yan Takarar Shugaban Kasar Da Burinsu Kawai Su Saci Kudi Ne — Wike

LABARAI MASU NASABA

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

June 29, 2025
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

June 29, 2025
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

June 29, 2025
Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

June 29, 2025
Babu Irin ArziÆ™in Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Babu Irin ArziÆ™in Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

June 29, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

June 29, 2025
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.