ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Kori Shugabannin PDP Da Ke Goyon Bayan Kwankwaso A Kano

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Kotu

Kotun daukaka kara da ke zamanta a Abuja a ranar Litinin ta jingine hukuncin da babban kotun tarayya ta yi na amincewa da Shehu Sagagi a matsayin shugaban jam’iyyar PDP a Jihar Kano.

Sagagi, wanda ke samun goyon bayan tsohon gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, wanda tuni ya fice daga jam’iyyar tare da zama dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar NNPP a halin yanzu.

  • Sojoji Sun Kashe Dan Ta’adda, Sun Kama Wasu 3 A Kaduna
  • Yadda Bidiyon Tsiraicina Ya Karade Shafukan Sada Zumunta – Safara’u

Wasu mambobin jam’iyyar dai sun jima suna zargin Sagagi da magoya bayansa da yin aikin goyon bayan mai gidansu a siyasa, Kwankwaso tare da yin saddu domin muradinsa ya cika.

ADVERTISEMENT

A ranar 29 ga watan Maris ne kwamitin uwar jam’iyyar PDP na kasa, ya rushe shugabancin jam’iyyar a Jihar Kano tare da nada wasu kwamitin riko na mutane shida da zai maye gurbin wadanda aka rushe.

A ranar 25 ga watan Mayu, alkalin babbar kotun tarayya a Kano, Taiwo Taiwo, ya ba da umarnin hana uwar jam’iyyar PDP daga cire Sagagi a matsayin shugaba har sai wa’adin mulkinsa ya kare a watan Disambar 2024.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

Hukuncin kotun ya ce uwar jam’iyyar ba ta da ikon rushe shugabannin da suka zama shugabanni ta hanyar zabe.

Sai dai kuma kotun daukaka kara a ranar Litinin, ta rushe wannan hukuncin na babbar kotun tarayya, inda ta ce lamari ne na cikin gida don haka uwar jam’iyyar tana da cikakken ikon rushe shugabannin jam’iyyar a Jihar Kano.

Kotun daukaka karar ta zartar da hukuncin cewa uwar jam’iyyar ta kasa na da ikon rushe kwamitin shugabanni jam’iyyar na Jihar Kano.

Hukuncin da alkalan kotun daukaka karar su uku suka yanke, wanda ke karkashin jagorancin Peter Ige, ta ce matakin da uwar jam’iyyar ta dauka na rushe shugabannin jiha da na kananan hukumomin Jihar Kano tare da nada kwamitin riko bai dace a kalubalanci hakan a kotu ba domin ya saba wa dokar jam’iyyar PDP.

Kotun ta ce rushe da nada kwamitin riko da uwar jam’iyyar ta yi, ya gudana ne bisa amfani da sashen dokar 31 (2) (e) na jam’iyyar.

Hukuncin na kotun na zuwa ne daidai lokacin da tsohon gwamnan Jihar Kano Ibrahim Shekarau, ya sake komawa cikin jam’iyyar ta PDP, wanda ake kyautata zaton shi ne ma zai jagoranci jam’iyyar wajen tsare-tsaren zaben 2023 a jihar.

Kazalika, ana ganin wannan hukuncin zai kawo karshen rikicin cikin gida da ke faruwa a PDP a Kano kan waye dan takarar gwamna na jam’iyyar a tsakanin Muhammad Abacha, dan tsohon shugaban kasa, Sani Abacha da Sadiq Wali.

Shi dai Muhammad Abacha an zabe shi ne a karkashin jagorancin Sagagi yayin da shi kuma Sadiq Wali dan tsohon ministan harkokin kasashen waje, Aminu Wali uwar jam’iyyar ta zaba.

Kotu
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Zan Fallasa ‘Yan Takarar Shugaban Kasar Da Burinsu Kawai Su Saci Kudi Ne — Wike

Zan Fallasa ‘Yan Takarar Shugaban Kasar Da Burinsu Kawai Su Saci Kudi Ne — Wike

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.