ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Kori Shugabannin PDP Da Ke Goyon Bayan Kwankwaso A Kano

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Kotu

Kotun daukaka kara da ke zamanta a Abuja a ranar Litinin ta jingine hukuncin da babban kotun tarayya ta yi na amincewa da Shehu Sagagi a matsayin shugaban jam’iyyar PDP a Jihar Kano.

Sagagi, wanda ke samun goyon bayan tsohon gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, wanda tuni ya fice daga jam’iyyar tare da zama dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar NNPP a halin yanzu.

  • Sojoji Sun Kashe Dan Ta’adda, Sun Kama Wasu 3 A Kaduna
  • Yadda Bidiyon Tsiraicina Ya Karade Shafukan Sada Zumunta – Safara’u

Wasu mambobin jam’iyyar dai sun jima suna zargin Sagagi da magoya bayansa da yin aikin goyon bayan mai gidansu a siyasa, Kwankwaso tare da yin saddu domin muradinsa ya cika.

ADVERTISEMENT

A ranar 29 ga watan Maris ne kwamitin uwar jam’iyyar PDP na kasa, ya rushe shugabancin jam’iyyar a Jihar Kano tare da nada wasu kwamitin riko na mutane shida da zai maye gurbin wadanda aka rushe.

A ranar 25 ga watan Mayu, alkalin babbar kotun tarayya a Kano, Taiwo Taiwo, ya ba da umarnin hana uwar jam’iyyar PDP daga cire Sagagi a matsayin shugaba har sai wa’adin mulkinsa ya kare a watan Disambar 2024.

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Hukuncin kotun ya ce uwar jam’iyyar ba ta da ikon rushe shugabannin da suka zama shugabanni ta hanyar zabe.

Sai dai kuma kotun daukaka kara a ranar Litinin, ta rushe wannan hukuncin na babbar kotun tarayya, inda ta ce lamari ne na cikin gida don haka uwar jam’iyyar tana da cikakken ikon rushe shugabannin jam’iyyar a Jihar Kano.

Kotun daukaka karar ta zartar da hukuncin cewa uwar jam’iyyar ta kasa na da ikon rushe kwamitin shugabanni jam’iyyar na Jihar Kano.

Hukuncin da alkalan kotun daukaka karar su uku suka yanke, wanda ke karkashin jagorancin Peter Ige, ta ce matakin da uwar jam’iyyar ta dauka na rushe shugabannin jiha da na kananan hukumomin Jihar Kano tare da nada kwamitin riko bai dace a kalubalanci hakan a kotu ba domin ya saba wa dokar jam’iyyar PDP.

Kotun ta ce rushe da nada kwamitin riko da uwar jam’iyyar ta yi, ya gudana ne bisa amfani da sashen dokar 31 (2) (e) na jam’iyyar.

Hukuncin na kotun na zuwa ne daidai lokacin da tsohon gwamnan Jihar Kano Ibrahim Shekarau, ya sake komawa cikin jam’iyyar ta PDP, wanda ake kyautata zaton shi ne ma zai jagoranci jam’iyyar wajen tsare-tsaren zaben 2023 a jihar.

Kazalika, ana ganin wannan hukuncin zai kawo karshen rikicin cikin gida da ke faruwa a PDP a Kano kan waye dan takarar gwamna na jam’iyyar a tsakanin Muhammad Abacha, dan tsohon shugaban kasa, Sani Abacha da Sadiq Wali.

Shi dai Muhammad Abacha an zabe shi ne a karkashin jagorancin Sagagi yayin da shi kuma Sadiq Wali dan tsohon ministan harkokin kasashen waje, Aminu Wali uwar jam’iyyar ta zaba.

Kotu
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Next Post
Zan Fallasa ‘Yan Takarar Shugaban Kasar Da Burinsu Kawai Su Saci Kudi Ne — Wike

Zan Fallasa ‘Yan Takarar Shugaban Kasar Da Burinsu Kawai Su Saci Kudi Ne — Wike

LABARAI MASU NASABA

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.