• English
  • Business News
Friday, August 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Tabbatar Da Kwace Masallacin Juma’a Na Marigayi Sheikh Ja’afar Na Kano

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
in Labarai
0
An Daure Bakanike Wata 3 Saboda Satar Batirin Mota
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babbar Kotun Jihar Kano mai lamba 5 a ranar Litinin ta tabbatar da kwace Masallacin Marigayi Sheikh Ja’afar Mahmud Adam tare da garkame shi.

Kacewar ya biyo bayan daukar dogon lokaci ana tafka shari’a inda daga bisani ta kwace Masallacin da ke unguwar Sabuwar Gandu.

  • Ministan Wajen Mali: Sin Ta Shiga Kyakkyawan Tafarkin Raya Hakkin Dan Adam
  • Hajjin Bana: NCAA Ta Ziyarci Filin Jirgin Gombe, Ta Ce Filin Zai Yi Jigilar Alhazai

An kwace Masallacin ne kacokan daga hannun kungiyar Izala, kotu ta mika shi ga kungiyar ci gaban unguwar ta Sabuwar Gandu.

Kamar yadda lamarin ya kasance, da safiyar ranar Litinin, Alkalin babbar kotun mai lamba 5 da ke zamanta a sakatariyar Audu Bako, Mai Shari’a Malam Usman Na’Abba ya je Masallacin na Sheikh Ja’afar Mahmud Adam, da ke unguwar ta Sabuwar Gandu da kansa, domin jaddada hukuncin da kotun ta yi watanni uku da suka gabata na tabbatar da mallakin Masallacin da makaranta da kuma gidan liman ga kungiyar ci gaban unguwar ta Sabuwar Gandu da kewaye.

A wata takarda mai dauke hatimin kotun har ma da na mai shari’a mai dauke kwanan watan 18 ga Mayun wannan shekara da muke ciki, Alkalin kotun ya shaida cewa, duba da shekaru da aka shafe ana gudanar da shari’ar tsakanin unguwar ci gaban unguwar da kuma kungiyar Izala, a don hakan ne ma shaidu daga kowane bangare sun tabbatar da cewa fili da kuma gine-ginen mallakin kungiyar ci gaban unguwar ta Sabuwar Gandu ne, wanda kuma a wancan lokaci kungiyar Izala ta gaza gamsar da kotu da hujjoji masu kwari dangane da da’awar da take yi na mallakin wannan Masallaci har dai da makarantar, don haka ne ma alkali Malam Umar Na’abba ya yi umarnin cewa daga waccan rana ta biyu ga Fabrairun wannan shekara da muke ciki, kotu ta tabbatar wa qungiyar unguwar ta Sabuwar Gandu mallakinsa sabanin kungiyar Izala da take da’awa tun a baya.

Labarai Masu Nasaba

Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa

Matsalar Shugabanci A Jihohi Ke Haifar Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki Ga Yara

Rahotanni sun yi nuni da cewa an like kofofin masallacin da takardun umar kotu da take umarnin cewa babbar kotun ta mika mallaki da kuma iko na wannan masallaci ga qungiyar ci gaba unguwar. An gano motar Izala a harabar Masallacin na kwashe kayan masallacin da kuma shirye-shirye kwashe kayan gidan limamin domin bin umarni kotu.

An shafe shekara bakwai ana shari’ar tsakanin kungiyar Izala, da gwamnatin Kano da kuma babban sakataren ma’aikatar kasa da tsare-tsare da kungiyar ta ci gaban unguwar, amma yanzu komai ya zo karshe.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KotuMasallaciSabuwar GanduSheikh Jafar Mahmud Adam
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ministan Wajen Mali: Sin Ta Shiga Kyakkyawan Tafarkin Raya Hakkin Dan Adam

Next Post

Dalilinmu Na Karbar Sunan Ahmed Lawan Maimakon Na Machina – INEC

Related

Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa
Manyan Labarai

Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa

51 minutes ago
Matsalar Shugabanci A Jihohi Ke Haifar Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki Ga Yara
Manyan Labarai

Matsalar Shugabanci A Jihohi Ke Haifar Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki Ga Yara

2 hours ago
Ba Sulhu Ko Sassauci Ga Ƴan Bindiga A Zamfara – Gwamna Lawal Dare
Labarai

Ba Sulhu Ko Sassauci Ga Ƴan Bindiga A Zamfara – Gwamna Lawal Dare

9 hours ago
NLC Ta Baiwa Gwamnati Kwanaki 7 Don Magance Badaƙalar Satar Kuɗin Ma’aikata
Labarai

NLC Ta Baiwa Gwamnati Kwanaki 7 Don Magance Badaƙalar Satar Kuɗin Ma’aikata

10 hours ago
Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Kaduna Ta Yi Watsi Da Kalaman El-rufa’i Akan Zargin Maguɗin Zaɓe
Labarai

Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Kaduna Ta Yi Watsi Da Kalaman El-rufa’i Akan Zargin Maguɗin Zaɓe

11 hours ago
Gwamnati Na Ƙoƙarin Tsoratar Da Ni Don In Shiga APC – Sanata Tambuwal
Labarai

Gwamnati Na Ƙoƙarin Tsoratar Da Ni Don In Shiga APC – Sanata Tambuwal

12 hours ago
Next Post
Dalilinmu Na Karbar Sunan Ahmed Lawan Maimakon Na Machina – INEC

Dalilinmu Na Karbar Sunan Ahmed Lawan Maimakon Na Machina - INEC

LABARAI MASU NASABA

Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa

Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa

August 15, 2025
Matsalar Shugabanci A Jihohi Ke Haifar Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki Ga Yara

Matsalar Shugabanci A Jihohi Ke Haifar Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki Ga Yara

August 15, 2025
Ba Sulhu Ko Sassauci Ga Ƴan Bindiga A Zamfara – Gwamna Lawal Dare

Ba Sulhu Ko Sassauci Ga Ƴan Bindiga A Zamfara – Gwamna Lawal Dare

August 14, 2025
NLC Ta Baiwa Gwamnati Kwanaki 7 Don Magance Badaƙalar Satar Kuɗin Ma’aikata

NLC Ta Baiwa Gwamnati Kwanaki 7 Don Magance Badaƙalar Satar Kuɗin Ma’aikata

August 14, 2025
Sashen Aikewa Da Kunshin Sakwanni Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni 7 Na Farkon Bana

Sashen Aikewa Da Kunshin Sakwanni Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni 7 Na Farkon Bana

August 14, 2025
Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Kaduna Ta Yi Watsi Da Kalaman El-rufa’i Akan Zargin Maguɗin Zaɓe

Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Kaduna Ta Yi Watsi Da Kalaman El-rufa’i Akan Zargin Maguɗin Zaɓe

August 14, 2025
Salon Zamanantarwa Na Sin Kyakkyawan Misali Ne Ga Kasashen Afirka

Salon Zamanantarwa Na Sin Kyakkyawan Misali Ne Ga Kasashen Afirka

August 14, 2025
Gwamnati Na Ƙoƙarin Tsoratar Da Ni Don In Shiga APC – Sanata Tambuwal

Gwamnati Na Ƙoƙarin Tsoratar Da Ni Don In Shiga APC – Sanata Tambuwal

August 14, 2025
Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Masana’antar Lantarki Ya Ci Gaba Da Samun Karfin Juriya A Kasar Sin

Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Masana’antar Lantarki Ya Ci Gaba Da Samun Karfin Juriya A Kasar Sin

August 14, 2025
Gidauniya Ta Rabar Da Buhun Takin Zamani 6,000 Ga Manoma A Bauchi 

Gidauniya Ta Rabar Da Buhun Takin Zamani 6,000 Ga Manoma A Bauchi 

August 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.