ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Tabbatar Da Kwace Masallacin Juma’a Na Marigayi Sheikh Ja’afar Na Kano

by Rabi'u Ali Indabawa
4 years ago
Sheikh Jafar Mahmud Adam

Babbar Kotun Jihar Kano mai lamba 5 a ranar Litinin ta tabbatar da kwace Masallacin Marigayi Sheikh Ja’afar Mahmud Adam tare da garkame shi.

Kacewar ya biyo bayan daukar dogon lokaci ana tafka shari’a inda daga bisani ta kwace Masallacin da ke unguwar Sabuwar Gandu.

  • Ministan Wajen Mali: Sin Ta Shiga Kyakkyawan Tafarkin Raya Hakkin Dan Adam
  • Hajjin Bana: NCAA Ta Ziyarci Filin Jirgin Gombe, Ta Ce Filin Zai Yi Jigilar Alhazai

An kwace Masallacin ne kacokan daga hannun kungiyar Izala, kotu ta mika shi ga kungiyar ci gaban unguwar ta Sabuwar Gandu.

ADVERTISEMENT

Kamar yadda lamarin ya kasance, da safiyar ranar Litinin, Alkalin babbar kotun mai lamba 5 da ke zamanta a sakatariyar Audu Bako, Mai Shari’a Malam Usman Na’Abba ya je Masallacin na Sheikh Ja’afar Mahmud Adam, da ke unguwar ta Sabuwar Gandu da kansa, domin jaddada hukuncin da kotun ta yi watanni uku da suka gabata na tabbatar da mallakin Masallacin da makaranta da kuma gidan liman ga kungiyar ci gaban unguwar ta Sabuwar Gandu da kewaye.

A wata takarda mai dauke hatimin kotun har ma da na mai shari’a mai dauke kwanan watan 18 ga Mayun wannan shekara da muke ciki, Alkalin kotun ya shaida cewa, duba da shekaru da aka shafe ana gudanar da shari’ar tsakanin unguwar ci gaban unguwar da kuma kungiyar Izala, a don hakan ne ma shaidu daga kowane bangare sun tabbatar da cewa fili da kuma gine-ginen mallakin kungiyar ci gaban unguwar ta Sabuwar Gandu ne, wanda kuma a wancan lokaci kungiyar Izala ta gaza gamsar da kotu da hujjoji masu kwari dangane da da’awar da take yi na mallakin wannan Masallaci har dai da makarantar, don haka ne ma alkali Malam Umar Na’abba ya yi umarnin cewa daga waccan rana ta biyu ga Fabrairun wannan shekara da muke ciki, kotu ta tabbatar wa qungiyar unguwar ta Sabuwar Gandu mallakinsa sabanin kungiyar Izala da take da’awa tun a baya.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Rahotanni sun yi nuni da cewa an like kofofin masallacin da takardun umar kotu da take umarnin cewa babbar kotun ta mika mallaki da kuma iko na wannan masallaci ga qungiyar ci gaba unguwar. An gano motar Izala a harabar Masallacin na kwashe kayan masallacin da kuma shirye-shirye kwashe kayan gidan limamin domin bin umarni kotu.

An shafe shekara bakwai ana shari’ar tsakanin kungiyar Izala, da gwamnatin Kano da kuma babban sakataren ma’aikatar kasa da tsare-tsare da kungiyar ta ci gaban unguwar, amma yanzu komai ya zo karshe.

Sheikh Jafar Mahmud Adam
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Dalilinmu Na Karbar Sunan Ahmed Lawan Maimakon Na Machina – INEC

Dalilinmu Na Karbar Sunan Ahmed Lawan Maimakon Na Machina - INEC

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.