ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Tabbatar Da Kwace Masallacin Juma’a Na Marigayi Sheikh Ja’afar Na Kano

by Rabi'u Ali Indabawa
4 years ago
Sheikh Jafar Mahmud Adam

Babbar Kotun Jihar Kano mai lamba 5 a ranar Litinin ta tabbatar da kwace Masallacin Marigayi Sheikh Ja’afar Mahmud Adam tare da garkame shi.

Kacewar ya biyo bayan daukar dogon lokaci ana tafka shari’a inda daga bisani ta kwace Masallacin da ke unguwar Sabuwar Gandu.

  • Ministan Wajen Mali: Sin Ta Shiga Kyakkyawan Tafarkin Raya Hakkin Dan Adam
  • Hajjin Bana: NCAA Ta Ziyarci Filin Jirgin Gombe, Ta Ce Filin Zai Yi Jigilar Alhazai

An kwace Masallacin ne kacokan daga hannun kungiyar Izala, kotu ta mika shi ga kungiyar ci gaban unguwar ta Sabuwar Gandu.

ADVERTISEMENT

Kamar yadda lamarin ya kasance, da safiyar ranar Litinin, Alkalin babbar kotun mai lamba 5 da ke zamanta a sakatariyar Audu Bako, Mai Shari’a Malam Usman Na’Abba ya je Masallacin na Sheikh Ja’afar Mahmud Adam, da ke unguwar ta Sabuwar Gandu da kansa, domin jaddada hukuncin da kotun ta yi watanni uku da suka gabata na tabbatar da mallakin Masallacin da makaranta da kuma gidan liman ga kungiyar ci gaban unguwar ta Sabuwar Gandu da kewaye.

A wata takarda mai dauke hatimin kotun har ma da na mai shari’a mai dauke kwanan watan 18 ga Mayun wannan shekara da muke ciki, Alkalin kotun ya shaida cewa, duba da shekaru da aka shafe ana gudanar da shari’ar tsakanin unguwar ci gaban unguwar da kuma kungiyar Izala, a don hakan ne ma shaidu daga kowane bangare sun tabbatar da cewa fili da kuma gine-ginen mallakin kungiyar ci gaban unguwar ta Sabuwar Gandu ne, wanda kuma a wancan lokaci kungiyar Izala ta gaza gamsar da kotu da hujjoji masu kwari dangane da da’awar da take yi na mallakin wannan Masallaci har dai da makarantar, don haka ne ma alkali Malam Umar Na’abba ya yi umarnin cewa daga waccan rana ta biyu ga Fabrairun wannan shekara da muke ciki, kotu ta tabbatar wa qungiyar unguwar ta Sabuwar Gandu mallakinsa sabanin kungiyar Izala da take da’awa tun a baya.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Rahotanni sun yi nuni da cewa an like kofofin masallacin da takardun umar kotu da take umarnin cewa babbar kotun ta mika mallaki da kuma iko na wannan masallaci ga qungiyar ci gaba unguwar. An gano motar Izala a harabar Masallacin na kwashe kayan masallacin da kuma shirye-shirye kwashe kayan gidan limamin domin bin umarni kotu.

An shafe shekara bakwai ana shari’ar tsakanin kungiyar Izala, da gwamnatin Kano da kuma babban sakataren ma’aikatar kasa da tsare-tsare da kungiyar ta ci gaban unguwar, amma yanzu komai ya zo karshe.

Sheikh Jafar Mahmud Adam
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
Dalilinmu Na Karbar Sunan Ahmed Lawan Maimakon Na Machina – INEC

Dalilinmu Na Karbar Sunan Ahmed Lawan Maimakon Na Machina - INEC

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.