ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 6, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Tabbatar Da Kwace Masallacin Juma’a Na Marigayi Sheikh Ja’afar Na Kano

by Rabi'u Ali Indabawa
4 years ago
Sheikh Jafar Mahmud Adam

Babbar Kotun Jihar Kano mai lamba 5 a ranar Litinin ta tabbatar da kwace Masallacin Marigayi Sheikh Ja’afar Mahmud Adam tare da garkame shi.

Kacewar ya biyo bayan daukar dogon lokaci ana tafka shari’a inda daga bisani ta kwace Masallacin da ke unguwar Sabuwar Gandu.

  • Ministan Wajen Mali: Sin Ta Shiga Kyakkyawan Tafarkin Raya Hakkin Dan Adam
  • Hajjin Bana: NCAA Ta Ziyarci Filin Jirgin Gombe, Ta Ce Filin Zai Yi Jigilar Alhazai

An kwace Masallacin ne kacokan daga hannun kungiyar Izala, kotu ta mika shi ga kungiyar ci gaban unguwar ta Sabuwar Gandu.

ADVERTISEMENT

Kamar yadda lamarin ya kasance, da safiyar ranar Litinin, Alkalin babbar kotun mai lamba 5 da ke zamanta a sakatariyar Audu Bako, Mai Shari’a Malam Usman Na’Abba ya je Masallacin na Sheikh Ja’afar Mahmud Adam, da ke unguwar ta Sabuwar Gandu da kansa, domin jaddada hukuncin da kotun ta yi watanni uku da suka gabata na tabbatar da mallakin Masallacin da makaranta da kuma gidan liman ga kungiyar ci gaban unguwar ta Sabuwar Gandu da kewaye.

A wata takarda mai dauke hatimin kotun har ma da na mai shari’a mai dauke kwanan watan 18 ga Mayun wannan shekara da muke ciki, Alkalin kotun ya shaida cewa, duba da shekaru da aka shafe ana gudanar da shari’ar tsakanin unguwar ci gaban unguwar da kuma kungiyar Izala, a don hakan ne ma shaidu daga kowane bangare sun tabbatar da cewa fili da kuma gine-ginen mallakin kungiyar ci gaban unguwar ta Sabuwar Gandu ne, wanda kuma a wancan lokaci kungiyar Izala ta gaza gamsar da kotu da hujjoji masu kwari dangane da da’awar da take yi na mallakin wannan Masallaci har dai da makarantar, don haka ne ma alkali Malam Umar Na’abba ya yi umarnin cewa daga waccan rana ta biyu ga Fabrairun wannan shekara da muke ciki, kotu ta tabbatar wa qungiyar unguwar ta Sabuwar Gandu mallakinsa sabanin kungiyar Izala da take da’awa tun a baya.

LABARAI MASU NASABA

Jonathan Ya Musanta Zargin Tayin Naira Biliyan 500 Domin Raba Kuri’un Kudu Maso Kudu

Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

Rahotanni sun yi nuni da cewa an like kofofin masallacin da takardun umar kotu da take umarnin cewa babbar kotun ta mika mallaki da kuma iko na wannan masallaci ga qungiyar ci gaba unguwar. An gano motar Izala a harabar Masallacin na kwashe kayan masallacin da kuma shirye-shirye kwashe kayan gidan limamin domin bin umarni kotu.

An shafe shekara bakwai ana shari’ar tsakanin kungiyar Izala, da gwamnatin Kano da kuma babban sakataren ma’aikatar kasa da tsare-tsare da kungiyar ta ci gaban unguwar, amma yanzu komai ya zo karshe.

Sheikh Jafar Mahmud Adam
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Sarkin Zazzau Ya Umarci A Soke Wasu Al’adu Da Ke Kawo Wa Aure Cikas

MASU ALAKA

Jonathan Ya Musanta Zargin Tayin Naira Biliyan 500 Domin Raba Kuri’un Kudu Maso Kudu
Labarai

Jonathan Ya Musanta Zargin Tayin Naira Biliyan 500 Domin Raba Kuri’un Kudu Maso Kudu

July 6, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje
Labarai

Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

July 5, 2026
Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam
Labarai

Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

July 5, 2026
Next Post
Dalilinmu Na Karbar Sunan Ahmed Lawan Maimakon Na Machina – INEC

Dalilinmu Na Karbar Sunan Ahmed Lawan Maimakon Na Machina - INEC

LABARAI MASU NASABA

Jonathan Ya Musanta Zargin Tayin Naira Biliyan 500 Domin Raba Kuri’un Kudu Maso Kudu

Jonathan Ya Musanta Zargin Tayin Naira Biliyan 500 Domin Raba Kuri’un Kudu Maso Kudu

July 6, 2026
FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

July 5, 2026
Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

July 5, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

July 5, 2026
An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

July 5, 2026
Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

July 5, 2026
Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

July 5, 2026
Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

July 5, 2026
Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

July 5, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

July 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.