• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Tura Alhassan Ado Dogwa Gidan Gyaran Hali

by Muhammad
2 years ago
in Labarai
0
Kotu Ta Tura Alhassan Ado Dogwa Gidan Gyaran Hali
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata kotun majisteri mai zamanta a Unguwar Normans land da ke Kano, ta tura Hon. Alhassan Ado Doguwa, gidan gyaran hali sakamakon zarginsa da harbe wasu mutane da kone su ranar Lahadin data gabata.

Ana zargin Alhassan Ado Dogwa, wanda shi ne shugaban masu rinjaye na majalisar wakilan Nijeriya da laifin harbi tare da kone mutane a karamar hukumarsa ta Tudun Wada da ke jihar Kano.

  • An Kama Alhassan Doguwa Kan Zargin Kisan Kai A Kano
  • An Kona Motoci Da Jikkata Wasu Yayin Artabu Tsakanin Magoya Bayan NNPP Da APC A Tudun Wada

Alkalin kotun mai lamba 54 ya ce, za a ci gaba da shari’ar Doguwan ranar 7 ga wannan watan da muke ciki.

A yamma cin yau Laraba aka gurfanar da shugaban masu rinjaye na Majalisar Wakilan Nijeriya, Hon. Alhassan Ado Doguwa, bisa laifuka da suka hada da haɗin baki wajen aikata kisan kai.

Sauran laifukan da ake zarginsa da su sun haɗa da raunata mutane da dama tare da zargin hannu a kunna wuta a ofishin jam’iyyar hamayya ta NNPP.

Labarai Masu Nasaba

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Ana zargin Doguwar da laifin tayar da gobarar a ofishin a ranar Lahadi 26 ga watan Fabarairu, 2023 wanda hakan ya yi sanadin ƙona wasu mutane da ke cikin ofishin.

Laifukan da ake zargin sa da su sun haɗa da kashe wasu mutum uku tare da raunata wasu mutum takwas a ƙaramar hukumar Doguwa a ranar 26 ga wannan watan nan a lokacin da ake karɓa da bayyana sakamakon zaɓen ɗan majalisar.

An yi ta yaɗa hotuna da bidiyon wasu mutane da ake zargi an harba da bindiga a shafukan sada zumunta, daga nan kuma rundunar ‘yan sandan ta gayyaci ɗan majalisar domin gudanar da bincike kan batun.

Sanarwar ta ce bayan da ɗan majalisar ya ƙi amsa gayyatar ne, rundunar ‘yan sandan jihar ta kama shi a filin jirgin saman Malam Aminu Kano da ke jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Alhassan Ado DoguwaDoguwakanoKisan kaiKotu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zuciyata Da Kofofina A Bude Suke Ga Kowa Don Ci Gaban Nijeriya – Tinubu

Next Post

Me Ya Faru Ga Panda Da Amurka Ta Ara Daga Kasar Sin?

Related

Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

9 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

9 hours ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)
Labarai

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

10 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

10 hours ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

13 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

14 hours ago
Next Post
Me Ya Faru Ga Panda Da Amurka Ta Ara Daga Kasar Sin?

Me Ya Faru Ga Panda Da Amurka Ta Ara Daga Kasar Sin?

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.