• English
  • Business News
Monday, August 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Umarci A Sake Cafko Mata Dakta Idris Dutsen Tanshi

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Dutsen Tanshi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babbar Kotun Shari’a da ke Bauchi a ranar Laraba ta warware belin fitaccen malamin addinin Musulunci kuma babban limamin masallacin Juma’a na Dutsen Tanshi da ke Bauchi, Dakta Idris Abdul’aziz tare da umartar a sake kamoshi bisa rashin halartar zaman kotun domin ci gaba da shari’ar tuhumar da ake masa.

Kotun a karkashin mai shari’a Malam Hussaini A. Turaki, ta ki amincewa da bukatar da Lauyan mai kariya ya shigar a gabanta da ke nusar da kotun cewa, sun daukaka kara kan wannan lamarin a kotun daukaka kara da ke Jos don haka ya nemi kada kotun ta cigaba da batu kan shari’ar.

  • Ali Nuhu Da Murja Kunya Na Cikin Mutane 150 Ma Fi Tasiri A Intanet A 2023
  • Harin ‘Yan Bindiga: Jama’a Sun Yi Zanga-zanga A Kaduna, Sun Nemi Taimakon Sarkin Zazzau

Nan take, lauyan gwamnatin jihar ya soki bukatar tare da cewa ba a bi matakan da suka dace na gabatar da wani batun daukaka kara ba.

Sai dai bayan sauraron muhawarar kowani bangare, Mai shari’a ya cimma matsayar cewa, dole ne wanda ake zargi ya bayyana a gaban kotun domin ci gaba da sauraron karar da ake masa.

Idan za a tuna dai, ana zargin babban malamin ne da furta wasu kalamai da ka iya barazana ga zaman lafiya da kwanciyar hankali hadi da tunzura jama’a a jihar. Kodayake, a watannin baya malamin har gidan yari ya je amma daga bisani aka samu belinsa.

Labarai Masu Nasaba

Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam

A ranar Labarar bayan dawowa ci gaba da sauraron karar, lauyan masu shigar da kara, UB Umar na ma’aikatar shari’a ta jihar Bauchi, ya ce, ba kotu ne ko masu shigar da kara za su gabatar da bukata a madadin wanda ake zargi ba, inda ya ce su din sun gaza yin hakan.

Ya ce, “Mun aike masa da sammaci daban-daban, a bayyane balo-balo ya fito ya ce shi ba zai zo kotu ba, muka sake canza sammacin aka manna a addireshinsa domin ba shi damar zuwa kotu.

“Sannan, akwai bukata wacce lauyansa ya shigar, amma ba a gabatar da ita ba.”

Acewar lauyan, kotu ba ta amfani da jita-jita illa abun da aka zo gabanta aka gabatar, don haka, masu kariya ba su bi matakan da suka dace na cewa sun daukaka kara kan shari’ar ba.

“Don haka kotu ta yi umarnin dole ya zo gabanta ya mata bayanin menene dalilinsa na kin halartar zaman da aka yi ta yi a baya, idan yana da hujja mai karfi na yin hakan shi kenan, nan gaba za mu san abun yi.”

Barista UB Umar ya kara da cewa, “Tun da an mika masa sammaci bai zo ba, mataki na gaba shi ne bai wa jami’an tsaron izinin kamoshi gami da gabatar da shi a zaman da kotun za ta yi mako mai zuwa a ranar 24 ga watan nan.”

Shi kuma a bangarensa, lauyan kariya, Ahmad M Umar, ya ce umarnin kamo malamin ba daidai ba ne domin sun sanar da kotun cewa, wannan shari’ar na gaban kotun daukaka kara, don haka, akwai bukatar kotun shari’ar ta mutunta kotun daukaka kara da ke Jos kafin kowane mataki.

Ya ce, “Mun tunatar da koun cewa soke belin wanda ake zargi ba daidai ba ne, sun yi ne bisa kuskure, saboda batun na gaban kotun daukaka kara.

“Mun tunatar da kotun cewa wannan kes din daga wannan kotun zuwa babban kotu sannan zuwa kotun daukaka kara da ke Jos. Mun gabatar da batun ga wannan kotun da sauran bangarorin da lamarin ya shafa tare da notices har guda hudu. Amma sakamakon shari’un zabukan gwamnoni, kotun daukaka karan ba ta samu damar zaunawa kan lamarin ba.

“Yanzu, kotun daukaka ta sake bayar da rana kuma mun shaida wa wannan kotun muka nemi kada ta yi komai domin mutunta matakin kotun daukaka kara, amma duk da suka haka ta soke belin da umarnin a kamo wanda muke karewa.”

Ya ce, matsayarsu shi ne akwai kes din da ke gaban kotun daukaka kara, kuma kotun daukaka kara na gaba da babban kotu balle kotun shari’a. Ya bada tabbacin cewa za su bi matakan da shari’a ta gindaya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Dutsen TanshiJihar Bauchi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hukumar Kashe Gobara Ta Jihar Bauchi Ta Ceto Rayuka Fiye Da 310 A 2023

Next Post

NIS Shiyyar Arewa Maso Gabas Ta Kaddamar Da “Operation Tsaron Iyaka”

Related

Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

9 hours ago
Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam
Labarai

Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam

9 hours ago
Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara
Tsaro

Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara

12 hours ago
Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas
Manyan Labarai

Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas

13 hours ago
Yadda Jinkirin Tabbatar Da ‘Yancin Cin Gashin Kai Ke Cutar Da Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi
Labarai

Yadda Jinkirin Tabbatar Da ‘Yancin Cin Gashin Kai Ke Cutar Da Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi

14 hours ago
Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu
Manyan Labarai

Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu

15 hours ago
Next Post
NIS

NIS Shiyyar Arewa Maso Gabas Ta Kaddamar Da “Operation Tsaron Iyaka”

LABARAI MASU NASABA

Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

August 10, 2025
Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

August 10, 2025
Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam

Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam

August 10, 2025
INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

August 10, 2025
Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

August 10, 2025
Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara

Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara

August 10, 2025
Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas

Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas

August 10, 2025
Yadda Jinkirin Tabbatar Da ‘Yancin Cin Gashin Kai Ke Cutar Da Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi

Yadda Jinkirin Tabbatar Da ‘Yancin Cin Gashin Kai Ke Cutar Da Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi

August 10, 2025
Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu

Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu

August 10, 2025
NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas 

NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas 

August 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.