• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Umarci A Sake Cafko Mata Dakta Idris Dutsen Tanshi

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Dutsen Tanshi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babbar Kotun Shari’a da ke Bauchi a ranar Laraba ta warware belin fitaccen malamin addinin Musulunci kuma babban limamin masallacin Juma’a na Dutsen Tanshi da ke Bauchi, Dakta Idris Abdul’aziz tare da umartar a sake kamoshi bisa rashin halartar zaman kotun domin ci gaba da shari’ar tuhumar da ake masa.

Kotun a karkashin mai shari’a Malam Hussaini A. Turaki, ta ki amincewa da bukatar da Lauyan mai kariya ya shigar a gabanta da ke nusar da kotun cewa, sun daukaka kara kan wannan lamarin a kotun daukaka kara da ke Jos don haka ya nemi kada kotun ta cigaba da batu kan shari’ar.

  • Ali Nuhu Da Murja Kunya Na Cikin Mutane 150 Ma Fi Tasiri A Intanet A 2023
  • Harin ‘Yan Bindiga: Jama’a Sun Yi Zanga-zanga A Kaduna, Sun Nemi Taimakon Sarkin Zazzau

Nan take, lauyan gwamnatin jihar ya soki bukatar tare da cewa ba a bi matakan da suka dace na gabatar da wani batun daukaka kara ba.

Sai dai bayan sauraron muhawarar kowani bangare, Mai shari’a ya cimma matsayar cewa, dole ne wanda ake zargi ya bayyana a gaban kotun domin ci gaba da sauraron karar da ake masa.

Idan za a tuna dai, ana zargin babban malamin ne da furta wasu kalamai da ka iya barazana ga zaman lafiya da kwanciyar hankali hadi da tunzura jama’a a jihar. Kodayake, a watannin baya malamin har gidan yari ya je amma daga bisani aka samu belinsa.

Labarai Masu Nasaba

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

A ranar Labarar bayan dawowa ci gaba da sauraron karar, lauyan masu shigar da kara, UB Umar na ma’aikatar shari’a ta jihar Bauchi, ya ce, ba kotu ne ko masu shigar da kara za su gabatar da bukata a madadin wanda ake zargi ba, inda ya ce su din sun gaza yin hakan.

Ya ce, “Mun aike masa da sammaci daban-daban, a bayyane balo-balo ya fito ya ce shi ba zai zo kotu ba, muka sake canza sammacin aka manna a addireshinsa domin ba shi damar zuwa kotu.

“Sannan, akwai bukata wacce lauyansa ya shigar, amma ba a gabatar da ita ba.”

Acewar lauyan, kotu ba ta amfani da jita-jita illa abun da aka zo gabanta aka gabatar, don haka, masu kariya ba su bi matakan da suka dace na cewa sun daukaka kara kan shari’ar ba.

“Don haka kotu ta yi umarnin dole ya zo gabanta ya mata bayanin menene dalilinsa na kin halartar zaman da aka yi ta yi a baya, idan yana da hujja mai karfi na yin hakan shi kenan, nan gaba za mu san abun yi.”

Barista UB Umar ya kara da cewa, “Tun da an mika masa sammaci bai zo ba, mataki na gaba shi ne bai wa jami’an tsaron izinin kamoshi gami da gabatar da shi a zaman da kotun za ta yi mako mai zuwa a ranar 24 ga watan nan.”

Shi kuma a bangarensa, lauyan kariya, Ahmad M Umar, ya ce umarnin kamo malamin ba daidai ba ne domin sun sanar da kotun cewa, wannan shari’ar na gaban kotun daukaka kara, don haka, akwai bukatar kotun shari’ar ta mutunta kotun daukaka kara da ke Jos kafin kowane mataki.

Ya ce, “Mun tunatar da koun cewa soke belin wanda ake zargi ba daidai ba ne, sun yi ne bisa kuskure, saboda batun na gaban kotun daukaka kara.

“Mun tunatar da kotun cewa wannan kes din daga wannan kotun zuwa babban kotu sannan zuwa kotun daukaka kara da ke Jos. Mun gabatar da batun ga wannan kotun da sauran bangarorin da lamarin ya shafa tare da notices har guda hudu. Amma sakamakon shari’un zabukan gwamnoni, kotun daukaka karan ba ta samu damar zaunawa kan lamarin ba.

“Yanzu, kotun daukaka ta sake bayar da rana kuma mun shaida wa wannan kotun muka nemi kada ta yi komai domin mutunta matakin kotun daukaka kara, amma duk da suka haka ta soke belin da umarnin a kamo wanda muke karewa.”

Ya ce, matsayarsu shi ne akwai kes din da ke gaban kotun daukaka kara, kuma kotun daukaka kara na gaba da babban kotu balle kotun shari’a. Ya bada tabbacin cewa za su bi matakan da shari’a ta gindaya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Dutsen TanshiJihar Bauchi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hukumar Kashe Gobara Ta Jihar Bauchi Ta Ceto Rayuka Fiye Da 310 A 2023

Next Post

NIS Shiyyar Arewa Maso Gabas Ta Kaddamar Da “Operation Tsaron Iyaka”

Related

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano
Labarai

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

9 hours ago
‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 
Labarai

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

10 hours ago
Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi
Labarai

Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

11 hours ago
Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore
Ra'ayi Riga

Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore

13 hours ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

15 hours ago
Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus
Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus

15 hours ago
Next Post
NIS

NIS Shiyyar Arewa Maso Gabas Ta Kaddamar Da “Operation Tsaron Iyaka”

LABARAI MASU NASABA

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 6, 2025
Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 5, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

June 5, 2025
Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

June 5, 2025
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

June 5, 2025
‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

June 5, 2025
Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

June 5, 2025
Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

June 5, 2025
Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

June 5, 2025
Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.