Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta sanya ranar 7 ga watan Satumba domin sauraron karar da ke neman a haramta wa Bola Tinubu dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar APC takara a zaben 2023.
Masu shigar da kara, jiga-jigan jam’iyyar APC guda hudu, sun nemi kotu ta yanke hukuncin cewa Tinubu bai cancanci tsayawa takarar shugaban kasa a zaben 2023 ba a matsayin dan takarar jam’iyyar saboda zargin ya mika takardun bogi na makarantun da ya yi ga hukumar zabe ta kasa (INEC).
- Sin Ta Kare Matakan Martani Da Ta Dauka Kan Yankin Taiwan Saboda Ziyarar Pelosi
- Kungiyar ASUU Ta Bukaci Soke Jarrabawar Jami’ar Jihar Kaduna
An dai zargi Tinubu da gabatar da takardun bogi lamarin da ya janyo cece-kuce da tarin muhawara mai zafi.
Hakazalika, an zarge shi da aikata laifuka da suka shafi harkokin safarar miyagun kwayoyi da kuma badakalar gidaje a kasar Amurka.
Sai daj dan takarar shugaban kasar na jam’iyyar APC, ya dukkan zarge-zargen da ake masa.
Tinubu zai kara zaben shugaban kasa na 2023 da Atiku na jam’iyyar PDP, Peter Obi daga jam’iyyar LP sai kuma Rabiu Musa Kwankwaso daga jam’iyyar NNPP.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp