• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Yanke Wa Matar Alkali Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya A Kebbi

by Umar Faruk Birnin Kebbi
1 year ago
Kebbi

Babbar kotun Jihar Kebbi ta daya ta yanke hukuncin kisa ta hanyar rataya ga wata tsohuwar matar wani alkalin Majastare Mai Shari’a Muhammad Attahiru Ibrahim Zagga, Farida Abubakar, bisa laifin kashe shi yayin da aka gurfanar da ita a gaban kotun.

Marigayin dai ya mutu ne a sakamakon kashe shi da aka yi a gidansa da ke rukunin gidagen Muhammadu Adamu Aliero, inda aka yanke masa wuya da kuma hannun hagu.

  • Gwamnatin Kebbi Ta Ayyana Asabar Ɗin Karshe Wata A Matsayin Ranar Tsaftar Muhalli
  • Mataimakin Gwamnan Kebbi Ya Nisanta Kansa Da Kalaman PDP

Da yake yanke hukuncin, babban Jojin jihar, Mai Shari’a Abubakar Umar wanda ya yanke hukunci a kan karar, ya ce kotun ta gamsu cewa wacce ake tuhuma da aikata laifin ce ta aiwatar kamar yadda shaidun da masu gabatar da kara suka gabatar suka nuna.

“An ga wacce ake kara a karshe tare da marigayin a gidansa da ke Birnin Kebbi, jim kadan bayan haka, an sami gawarsa. Haka kuma Shaidar ta dace ta alakanta wadda ake tuhuma da aikata laifin”.

Hakazalika, kotu ta ce ” Ta gamsu da cewa hujjojin da shaidu 12 suka gabatar a gaban kotu sun bayyana cewa ita ce ta kashe marigayin”.

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

Har ilayau, “An ga marigayin tare da wacce ake kara su kadai, shaidun da aka gabatar sun kasance masu karfi, ba tare da wata jayayya ba, an sami Hijabinta da jini, haka kuma laifin da aka aikata a daidai lokacin da marigayin ya kusa kara auren wata amarya kamar yadda shaidu suka tabbatar wa kotun”.

Bugu da kari Kotun ta kara da cewa ta gamsu da dukkan hujjojin da aka gabatar a gabanta. Ta tabbatar da cewa wadda ake tuhumar ta shirya kai harin ne da wuka mai kaifi, ko shakka babu yankan wukar ya yi sanadin mutuwarsa.

“Kotu ta yanke miki hukuncin kisa ta hanyar rataya kamar yadda sashe na 191 a ciki (b) na kundin dokokin Jihar Kebbi ta tanada, za a rataye ki ta wuya har sai kun mutu”.

“Kotu ta kuma yanke miki hukuncin daurin shekaru 7 a gidan yari bisa samun ki da laifin cutar da marigayin kamar yadda sashe na 224 (1) na dokokin Jihar Kebbi ya tanada ko ki biya Naira dubu dari ko duka biyun”.

Mai Shari’a Abubakar Umar ya bayyana cewa, bayan sauraron dukkan bangarorin biyu, a irin wannan yanayi, an kashe marigayin ne a lokacin da yake aiki, (Majastare Attahiru Muhammad Ibrahim Zagga) kuma doka ta tabbatar da babu shakka, irin wannan laifin hukuncin ya zama tilas.

Kotun ta bayyana cewa Farida Abubakar ta aikata laifin ne a ranar 25/8/2022 yayin da aka shigar da manyan tuhume-tuhumen a gaban kotu a ranar 26/7/2023 tare da yanke hukunci a ranar 3/6/2024.

Lauyan da ke tsaya wa wacce ake kara, Mudashiru Sale ya ce “wadda aka yanke wa hukuncin da nake karewa za ta daukaka kara kan hukuncin da aka yanke mata a gaban kotun daukaka kara da ke a Jihar Sakwakkato.”

Lauyoyin da ke gabatar da kara sun gabatar da shaidu 12 tare da gabatar da kayan da za su tabbatar cewa an aikata laifin har guda 8 da suka hada da Hijabi mai dauke da jini, inda kotun ta karbe su a Matsayar shaida yayin da wacce ake kara ta gabatar da shaidu 2 da aka shigar da su a gaban Kotun.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

TCN
Labarai

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI
Labarai

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Labarai

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
Next Post
Tsoho Mai Shekara 70 Ya Shiga Hannu Kan Safarar Wiwi

Tsoho Mai Shekara 70 Ya Shiga Hannu Kan Safarar Wiwi

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

October 9, 2025
TCN

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

October 9, 2025
Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

October 9, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

October 9, 2025
SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.