• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Yanke Wa Matar Alkali Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya A Kebbi

by Umar Faruk Birnin Kebbi
1 year ago
in Labarai
0
Kotu Ta Yanke Wa Matar Alkali Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya A Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babbar kotun Jihar Kebbi ta daya ta yanke hukuncin kisa ta hanyar rataya ga wata tsohuwar matar wani alkalin Majastare Mai Shari’a Muhammad Attahiru Ibrahim Zagga, Farida Abubakar, bisa laifin kashe shi yayin da aka gurfanar da ita a gaban kotun.

Marigayin dai ya mutu ne a sakamakon kashe shi da aka yi a gidansa da ke rukunin gidagen Muhammadu Adamu Aliero, inda aka yanke masa wuya da kuma hannun hagu.

  • Gwamnatin Kebbi Ta Ayyana Asabar Ɗin Karshe Wata A Matsayin Ranar Tsaftar Muhalli
  • Mataimakin Gwamnan Kebbi Ya Nisanta Kansa Da Kalaman PDP

Da yake yanke hukuncin, babban Jojin jihar, Mai Shari’a Abubakar Umar wanda ya yanke hukunci a kan karar, ya ce kotun ta gamsu cewa wacce ake tuhuma da aikata laifin ce ta aiwatar kamar yadda shaidun da masu gabatar da kara suka gabatar suka nuna.

“An ga wacce ake kara a karshe tare da marigayin a gidansa da ke Birnin Kebbi, jim kadan bayan haka, an sami gawarsa. Haka kuma Shaidar ta dace ta alakanta wadda ake tuhuma da aikata laifin”.

Hakazalika, kotu ta ce ” Ta gamsu da cewa hujjojin da shaidu 12 suka gabatar a gaban kotu sun bayyana cewa ita ce ta kashe marigayin”.

Labarai Masu Nasaba

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har ilayau, “An ga marigayin tare da wacce ake kara su kadai, shaidun da aka gabatar sun kasance masu karfi, ba tare da wata jayayya ba, an sami Hijabinta da jini, haka kuma laifin da aka aikata a daidai lokacin da marigayin ya kusa kara auren wata amarya kamar yadda shaidu suka tabbatar wa kotun”.

Bugu da kari Kotun ta kara da cewa ta gamsu da dukkan hujjojin da aka gabatar a gabanta. Ta tabbatar da cewa wadda ake tuhumar ta shirya kai harin ne da wuka mai kaifi, ko shakka babu yankan wukar ya yi sanadin mutuwarsa.

“Kotu ta yanke miki hukuncin kisa ta hanyar rataya kamar yadda sashe na 191 a ciki (b) na kundin dokokin Jihar Kebbi ta tanada, za a rataye ki ta wuya har sai kun mutu”.

“Kotu ta kuma yanke miki hukuncin daurin shekaru 7 a gidan yari bisa samun ki da laifin cutar da marigayin kamar yadda sashe na 224 (1) na dokokin Jihar Kebbi ya tanada ko ki biya Naira dubu dari ko duka biyun”.

Mai Shari’a Abubakar Umar ya bayyana cewa, bayan sauraron dukkan bangarorin biyu, a irin wannan yanayi, an kashe marigayin ne a lokacin da yake aiki, (Majastare Attahiru Muhammad Ibrahim Zagga) kuma doka ta tabbatar da babu shakka, irin wannan laifin hukuncin ya zama tilas.

Kotun ta bayyana cewa Farida Abubakar ta aikata laifin ne a ranar 25/8/2022 yayin da aka shigar da manyan tuhume-tuhumen a gaban kotu a ranar 26/7/2023 tare da yanke hukunci a ranar 3/6/2024.

Lauyan da ke tsaya wa wacce ake kara, Mudashiru Sale ya ce “wadda aka yanke wa hukuncin da nake karewa za ta daukaka kara kan hukuncin da aka yanke mata a gaban kotun daukaka kara da ke a Jihar Sakwakkato.”

Lauyoyin da ke gabatar da kara sun gabatar da shaidu 12 tare da gabatar da kayan da za su tabbatar cewa an aikata laifin har guda 8 da suka hada da Hijabi mai dauke da jini, inda kotun ta karbe su a Matsayar shaida yayin da wacce ake kara ta gabatar da shaidu 2 da aka shigar da su a gaban Kotun.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: CourtHukuncinKebbiPolice
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Kano Ta Biyawa Ɗalibai 119,903 Kudin Jarrabawar NECO Da NBAIS

Next Post

Tsoho Mai Shekara 70 Ya Shiga Hannu Kan Safarar Wiwi

Related

Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

2 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

2 hours ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)
Labarai

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

3 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

4 hours ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

6 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

7 hours ago
Next Post
Tsoho Mai Shekara 70 Ya Shiga Hannu Kan Safarar Wiwi

Tsoho Mai Shekara 70 Ya Shiga Hannu Kan Safarar Wiwi

LABARAI MASU NASABA

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

June 28, 2025
Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.