• English
  • Business News
Monday, July 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsoho Mai Shekara 70 Ya Shiga Hannu Kan Safarar Wiwi

by Umar Faruk Birnin Kebbi
1 year ago
in Kotu Da Ɗansanda, Labarai, Tsaro
0
Tsoho Mai Shekara 70 Ya Shiga Hannu Kan Safarar Wiwi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jami’an Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Kasa NDLEA, sun kama wani tsoho mai shekara 70 dauke da tabar wiwi mai nauyin kilogiram 57.2 a Jihar Nasarawa tare da kwace hodar Iblis da kudinta ya kai sama da Naira biliyan 2.1. 

An kama wannan wannan nau’in tabar wiwi na roba a tashar ruwa ta Fatakwal, da kuma filin jirgin saman Murtala Muhammed da ke Legas.

Kazalika jami’an dai sun kama wasu mutum biyu da ake zargi da safarar tabar wiwi mai nauyin kilogiram 426 a Jihar Ekiti.

  • NDLEA Ta Cafke Masu Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas
  • Hajjin Bana: NDLEA Ta Kama Maniyyata Dauke da Hodar Iblis A Legas

An bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun Daraktan Yada Labarai na Hukumar NDLEA, Femi Babafemi.

Kazali Hukumar ta kaddamar wasu kame a Babban Birnin Tarayya Abuja da Katsina da kuma Jihar Nasarawa.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

Sanarwar ta ci gaba da cewa, “Jami’an ‘yansandan sun kama wasu manya-manyan kayayyakin tabar wiwi da kudinsu ya haura Naira 2.1 a kan tituna a tashar jiragen ruwa na Fatakwal, Onne da filin jirgin Murtala Muhammed da ke Ikeja.

“A filin jirgin saman Legas, jami’an tare da hadin gwiwar wasu jami’an tsaro a ranar Juma’a, 31 ga watan Mayu, 2024, sun kama wani babban kaya a cikin akwatuna guda takwas, dauke da fakiti 320 da nauyin kilogiram 164.50 na kayayyaki masu nauyi daga Kanada a kan jirgin sama samfurin KLM na Kasar Amsterdam, Netherlands.

“Kayyakin da aka kiyasta kudinsu ya kai Naira miliyan 960 wanda wani fasinja, Ughenu Nnaife Francis ya shigo da shi. Jami’an hukumar NDLEA, kwastam da sauran su ne suka gano shi a dakin karbar fasinjoji na E-ishort na filin jirgin sama a yayin wani aikin karbar fasinjoji na hadin gwiwa da jami’an tsaro suka gudanar a yayin da jami’an suka gudanar da bincike a kai, lokacin da wanda ake zargin ke yunkurin fitar da akwatunan daga zauren.”

A cewar sanarwar, wanda ake zargin da aka kama a filin jirgin sama na Legas ya yi ikirarin cewa an dauke shi aikin safarar kwayoyin ne daga Kasar Kanada zuwa Nijeriya a kan kudi Naira miliyan 6.

Ya ce shi dan Kasar Jamus ne amma ya je Toronto ne domin karbar magungunan, sannan an kama shi da wani kaso mai yawa na Loud, wani nau’in tabar wiwi wanda kudinsa ya kai Naira miliyan 960.

A halin da ake ciki kuma, jami’an NDLEA da ke harabar tashar jiragen ruwa ta Fatakwal sun kama wata kwantena da ta taso daga Kasar Indiya dauke da katan 1,750 na hodar Iblis mai nauyin kilogiram 26,250 kuma darajarsa ta kai Naira biliyan 1.225. Kwantenar mai lamba TEMU 6807401, an nufi Enugu da ita ne, kuma an gano ta lokacin wani aiki na hadin gwiwa da hukumar NDLEA, da kwastam, da sauran hukumomin tsaro suka gudanar.

‘Yansandan sun kuma kama wata mata ‘yar shekara 25 mai suna Blessing Thomas a Abuja a ranar 31 ga watan Mayu bayan da aka samu kilo 1 na sinadarin methamphetamine a hannunta, tana tafiya ne a cikin motar bas daga Legas zuwa Yola, Jihar Adamawa, an kama ta a kan hanyar Kwali zuwa Gwagwalada.

Sanarwar ta kara da cewa, “Haka zalika jami’an tsaro a Jihar Nasarawa sun kama wani tsoho mai suna Muhammadu Ibrahim dan shekaru 70 da haihuwa da tabar wiwi mai nauyin kilogiram 57.2 a garin LafiYa babban birnin jihar.

“An kama mutum biyu Suleiman Kazeem mai shekaru 35 da Sunday Gbenga mai shekaru 20 a lokacin da jami’an NDLEA suka kai farmaki dajin Ara, Ara-Ekiti a Jihar Ekiti inda suka kwato kilogiram 426 na tabar wiwi da tuni aka shirya su a cikin manyan buhuna, da sama da kilogiram 4,000 na sinadari iri daya da ya kai noman sama da kadada 1.66.

“A Jihar Katsina kuwa, an kama wani dan Nijar mai suna Suleman Audu, mai shekaru 29, 76 na tabar wiwi mai nauyin kilogiram 42, a bayan da jami’an NDLEA suka kama shi a hanyar Zaria zuwa Malumfashi.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu Ta Yanke Wa Matar Alkali Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya A Kebbi

Next Post

NSCDC Ta Yaye Dakaru Na Musamman A Zamfara

Related

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato
Da ɗumi-ɗuminsa

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

4 hours ago
Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a
Labarai

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

5 hours ago
Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson
Labarai

Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

6 hours ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Manyan Labarai

Ranar Talata Mai Zuwa Zan Koma Zauren Majalisar Dattawa – Sanata Natasha

9 hours ago
Za A Fara Sufurin Ma’aikata Da Ɗaliban Kaduna Kyauta A Bas
Labarai

Za A Fara Sufurin Ma’aikata Da Ɗaliban Kaduna Kyauta A Bas

12 hours ago
Mutane 8 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsari A Hanyar Lagos
Labarai

Mutane 8 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsari A Hanyar Lagos

13 hours ago
Next Post
NSCDC Ta Yaye Dakaru Na Musamman A Zamfara

NSCDC Ta Yaye Dakaru Na Musamman A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

July 6, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

July 6, 2025
Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

July 6, 2025
Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

July 6, 2025
Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

July 6, 2025
Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

July 6, 2025
Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

July 6, 2025
Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

July 6, 2025
Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

July 6, 2025
Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

July 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.