• English
  • Business News
Tuesday, July 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsoho Mai Shekara 70 Ya Shiga Hannu Kan Safarar Wiwi

by Umar Faruk Birnin Kebbi
1 year ago
in Kotu Da Ɗansanda, Labarai, Tsaro
0
Tsoho Mai Shekara 70 Ya Shiga Hannu Kan Safarar Wiwi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jami’an Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Kasa NDLEA, sun kama wani tsoho mai shekara 70 dauke da tabar wiwi mai nauyin kilogiram 57.2 a Jihar Nasarawa tare da kwace hodar Iblis da kudinta ya kai sama da Naira biliyan 2.1. 

An kama wannan wannan nau’in tabar wiwi na roba a tashar ruwa ta Fatakwal, da kuma filin jirgin saman Murtala Muhammed da ke Legas.

Kazalika jami’an dai sun kama wasu mutum biyu da ake zargi da safarar tabar wiwi mai nauyin kilogiram 426 a Jihar Ekiti.

  • NDLEA Ta Cafke Masu Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas
  • Hajjin Bana: NDLEA Ta Kama Maniyyata Dauke da Hodar Iblis A Legas

An bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun Daraktan Yada Labarai na Hukumar NDLEA, Femi Babafemi.

Kazali Hukumar ta kaddamar wasu kame a Babban Birnin Tarayya Abuja da Katsina da kuma Jihar Nasarawa.

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Ba Ta Da Sha’awar Yin Gwajin Makamin Nukiliya — Shettima

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

Sanarwar ta ci gaba da cewa, “Jami’an ‘yansandan sun kama wasu manya-manyan kayayyakin tabar wiwi da kudinsu ya haura Naira 2.1 a kan tituna a tashar jiragen ruwa na Fatakwal, Onne da filin jirgin Murtala Muhammed da ke Ikeja.

“A filin jirgin saman Legas, jami’an tare da hadin gwiwar wasu jami’an tsaro a ranar Juma’a, 31 ga watan Mayu, 2024, sun kama wani babban kaya a cikin akwatuna guda takwas, dauke da fakiti 320 da nauyin kilogiram 164.50 na kayayyaki masu nauyi daga Kanada a kan jirgin sama samfurin KLM na Kasar Amsterdam, Netherlands.

“Kayyakin da aka kiyasta kudinsu ya kai Naira miliyan 960 wanda wani fasinja, Ughenu Nnaife Francis ya shigo da shi. Jami’an hukumar NDLEA, kwastam da sauran su ne suka gano shi a dakin karbar fasinjoji na E-ishort na filin jirgin sama a yayin wani aikin karbar fasinjoji na hadin gwiwa da jami’an tsaro suka gudanar a yayin da jami’an suka gudanar da bincike a kai, lokacin da wanda ake zargin ke yunkurin fitar da akwatunan daga zauren.”

A cewar sanarwar, wanda ake zargin da aka kama a filin jirgin sama na Legas ya yi ikirarin cewa an dauke shi aikin safarar kwayoyin ne daga Kasar Kanada zuwa Nijeriya a kan kudi Naira miliyan 6.

Ya ce shi dan Kasar Jamus ne amma ya je Toronto ne domin karbar magungunan, sannan an kama shi da wani kaso mai yawa na Loud, wani nau’in tabar wiwi wanda kudinsa ya kai Naira miliyan 960.

A halin da ake ciki kuma, jami’an NDLEA da ke harabar tashar jiragen ruwa ta Fatakwal sun kama wata kwantena da ta taso daga Kasar Indiya dauke da katan 1,750 na hodar Iblis mai nauyin kilogiram 26,250 kuma darajarsa ta kai Naira biliyan 1.225. Kwantenar mai lamba TEMU 6807401, an nufi Enugu da ita ne, kuma an gano ta lokacin wani aiki na hadin gwiwa da hukumar NDLEA, da kwastam, da sauran hukumomin tsaro suka gudanar.

‘Yansandan sun kuma kama wata mata ‘yar shekara 25 mai suna Blessing Thomas a Abuja a ranar 31 ga watan Mayu bayan da aka samu kilo 1 na sinadarin methamphetamine a hannunta, tana tafiya ne a cikin motar bas daga Legas zuwa Yola, Jihar Adamawa, an kama ta a kan hanyar Kwali zuwa Gwagwalada.

Sanarwar ta kara da cewa, “Haka zalika jami’an tsaro a Jihar Nasarawa sun kama wani tsoho mai suna Muhammadu Ibrahim dan shekaru 70 da haihuwa da tabar wiwi mai nauyin kilogiram 57.2 a garin LafiYa babban birnin jihar.

“An kama mutum biyu Suleiman Kazeem mai shekaru 35 da Sunday Gbenga mai shekaru 20 a lokacin da jami’an NDLEA suka kai farmaki dajin Ara, Ara-Ekiti a Jihar Ekiti inda suka kwato kilogiram 426 na tabar wiwi da tuni aka shirya su a cikin manyan buhuna, da sama da kilogiram 4,000 na sinadari iri daya da ya kai noman sama da kadada 1.66.

“A Jihar Katsina kuwa, an kama wani dan Nijar mai suna Suleman Audu, mai shekaru 29, 76 na tabar wiwi mai nauyin kilogiram 42, a bayan da jami’an NDLEA suka kama shi a hanyar Zaria zuwa Malumfashi.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu Ta Yanke Wa Matar Alkali Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya A Kebbi

Next Post

NSCDC Ta Yaye Dakaru Na Musamman A Zamfara

Related

Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Manyan Labarai

Nijeriya Ba Ta Da Sha’awar Yin Gwajin Makamin Nukiliya — Shettima

26 minutes ago
Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC
Labarai

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

9 hours ago
NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19
Da ɗumi-ɗuminsa

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

10 hours ago
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista
Da ɗumi-ɗuminsa

Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

11 hours ago
Gwamna Peter Mbah Ya Ƙaddamar Da Jiragen Kasuwanci 3 Na ‘Enugu Air’ Mallakin Jihar
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Peter Mbah Ya Ƙaddamar Da Jiragen Kasuwanci 3 Na ‘Enugu Air’ Mallakin Jihar

12 hours ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Da ɗumi-ɗuminsa

Lauyoyin Majalisar Dattawa Sun Ƙaryata Natasha Kan Cewa Kotu Ta Ce Ta Koma Bakin Aiki

15 hours ago
Next Post
NSCDC Ta Yaye Dakaru Na Musamman A Zamfara

NSCDC Ta Yaye Dakaru Na Musamman A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Nijeriya Ba Ta Da Sha’awar Yin Gwajin Makamin Nukiliya — Shettima

July 8, 2025
Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

July 7, 2025
Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

July 7, 2025
Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

July 7, 2025
Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

July 7, 2025
NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

July 7, 2025
Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

July 7, 2025
Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan

Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan

July 7, 2025
Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%

Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%

July 7, 2025
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

July 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.