ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsoho Mai Shekara 70 Ya Shiga Hannu Kan Safarar Wiwi

by Umar Faruk Birnin Kebbi
2 years ago
Tsoho

Jami’an Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Kasa NDLEA, sun kama wani tsoho mai shekara 70 dauke da tabar wiwi mai nauyin kilogiram 57.2 a Jihar Nasarawa tare da kwace hodar Iblis da kudinta ya kai sama da Naira biliyan 2.1. 

An kama wannan wannan nau’in tabar wiwi na roba a tashar ruwa ta Fatakwal, da kuma filin jirgin saman Murtala Muhammed da ke Legas.

Kazalika jami’an dai sun kama wasu mutum biyu da ake zargi da safarar tabar wiwi mai nauyin kilogiram 426 a Jihar Ekiti.

ADVERTISEMENT
  • NDLEA Ta Cafke Masu Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas
  • Hajjin Bana: NDLEA Ta Kama Maniyyata Dauke da Hodar Iblis A Legas

An bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun Daraktan Yada Labarai na Hukumar NDLEA, Femi Babafemi.

Kazali Hukumar ta kaddamar wasu kame a Babban Birnin Tarayya Abuja da Katsina da kuma Jihar Nasarawa.

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Sanarwar ta ci gaba da cewa, “Jami’an ‘yansandan sun kama wasu manya-manyan kayayyakin tabar wiwi da kudinsu ya haura Naira 2.1 a kan tituna a tashar jiragen ruwa na Fatakwal, Onne da filin jirgin Murtala Muhammed da ke Ikeja.

“A filin jirgin saman Legas, jami’an tare da hadin gwiwar wasu jami’an tsaro a ranar Juma’a, 31 ga watan Mayu, 2024, sun kama wani babban kaya a cikin akwatuna guda takwas, dauke da fakiti 320 da nauyin kilogiram 164.50 na kayayyaki masu nauyi daga Kanada a kan jirgin sama samfurin KLM na Kasar Amsterdam, Netherlands.

“Kayyakin da aka kiyasta kudinsu ya kai Naira miliyan 960 wanda wani fasinja, Ughenu Nnaife Francis ya shigo da shi. Jami’an hukumar NDLEA, kwastam da sauran su ne suka gano shi a dakin karbar fasinjoji na E-ishort na filin jirgin sama a yayin wani aikin karbar fasinjoji na hadin gwiwa da jami’an tsaro suka gudanar a yayin da jami’an suka gudanar da bincike a kai, lokacin da wanda ake zargin ke yunkurin fitar da akwatunan daga zauren.”

A cewar sanarwar, wanda ake zargin da aka kama a filin jirgin sama na Legas ya yi ikirarin cewa an dauke shi aikin safarar kwayoyin ne daga Kasar Kanada zuwa Nijeriya a kan kudi Naira miliyan 6.

Ya ce shi dan Kasar Jamus ne amma ya je Toronto ne domin karbar magungunan, sannan an kama shi da wani kaso mai yawa na Loud, wani nau’in tabar wiwi wanda kudinsa ya kai Naira miliyan 960.

A halin da ake ciki kuma, jami’an NDLEA da ke harabar tashar jiragen ruwa ta Fatakwal sun kama wata kwantena da ta taso daga Kasar Indiya dauke da katan 1,750 na hodar Iblis mai nauyin kilogiram 26,250 kuma darajarsa ta kai Naira biliyan 1.225. Kwantenar mai lamba TEMU 6807401, an nufi Enugu da ita ne, kuma an gano ta lokacin wani aiki na hadin gwiwa da hukumar NDLEA, da kwastam, da sauran hukumomin tsaro suka gudanar.

‘Yansandan sun kuma kama wata mata ‘yar shekara 25 mai suna Blessing Thomas a Abuja a ranar 31 ga watan Mayu bayan da aka samu kilo 1 na sinadarin methamphetamine a hannunta, tana tafiya ne a cikin motar bas daga Legas zuwa Yola, Jihar Adamawa, an kama ta a kan hanyar Kwali zuwa Gwagwalada.

Sanarwar ta kara da cewa, “Haka zalika jami’an tsaro a Jihar Nasarawa sun kama wani tsoho mai suna Muhammadu Ibrahim dan shekaru 70 da haihuwa da tabar wiwi mai nauyin kilogiram 57.2 a garin LafiYa babban birnin jihar.

“An kama mutum biyu Suleiman Kazeem mai shekaru 35 da Sunday Gbenga mai shekaru 20 a lokacin da jami’an NDLEA suka kai farmaki dajin Ara, Ara-Ekiti a Jihar Ekiti inda suka kwato kilogiram 426 na tabar wiwi da tuni aka shirya su a cikin manyan buhuna, da sama da kilogiram 4,000 na sinadari iri daya da ya kai noman sama da kadada 1.66.

“A Jihar Katsina kuwa, an kama wani dan Nijar mai suna Suleman Audu, mai shekaru 29, 76 na tabar wiwi mai nauyin kilogiram 42, a bayan da jami’an NDLEA suka kama shi a hanyar Zaria zuwa Malumfashi.”

Tsoho
Umar Faruk Birnin Kebbi
+ postsBio
  • Umar Faruk Birnin Kebbi
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-birnin-kebbi-3/
    Dole Ne Ƙungiyoyin Ƴan Banga Su Haɗa Kai – Kauran Yauri
  • Umar Faruk Birnin Kebbi
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-birnin-kebbi-3/
    NAPTIP Ta Kuɓutar Da Yara 19 Da Aka Sace A Kebbi 
  • Umar Faruk Birnin Kebbi
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-birnin-kebbi-3/
    Hukumar SEMA Ta Jihar Kebbi Ta Tallafa Wa Mutanen Da Ambaliyar Ruwan Sama Ta Shafa A Argungu
  • Umar Faruk Birnin Kebbi
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-birnin-kebbi-3/
    Kotu Ta Yanke Wa Matar Alkali Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya A Kebbi

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Next Post
NSCDC Ta Yaye Dakaru Na Musamman A Zamfara

NSCDC Ta Yaye Dakaru Na Musamman A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.