• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Yanke Wa Wasu Masu Fyade 4 Hukuncin Daurin Rai-Da-Rai A Jigawa

by Sulaiman
3 years ago
in Labarai
0
Kotu Ta Yanke Wa Wasu Masu Fyade 4 Hukuncin Daurin Rai-Da-Rai A Jigawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata babbar kotu dake zamanta a birnin Kudu a jihar Jigawa ta yanke wa wasu mutum hudu da ta samu da laifin aikata fyade, hukuncin daurin rai-da-rai.

Sanarwar da Ma’aikatar Shari’a ta jihar ta fitar ranar Laraba, mai dauke da sa hannun jami’ar hulda ta ma’aikatar, Zainab Baba Santali, ta ce mutanen sun aikata babban laifi, duba da sashi na 283 na kundin dokar jihar na 2012 da aka sabunta.

  • Uba Ya Yi Wa ‘Yarsa Fyade A Osun, Amma Ya Roki Ta Yafe Masa

Mutanen da hukuncin ya afka musu, sun hada da Umar Danladi da Abdussalam Sale da Auwalu Yunusa da kuma Mu’azu Abdurrahman. BBC Hausa

Da yake yanke hukuncin, Mai Shari’a Musa Ubale, ya ce an samu Umar Danladi da laifin yi wa wata yarinya mai shekara takwas fyade lokacin da take komawa gida daga makaranta.
Sannan an samu Abdussalam Sale da laifin yi wa wata Yarinya mai shekaru 12 fyade. Ya hadu da yarinyar ne a kauyen Kishin Gishin Gawa, inda ya yaudare ta ta hanyar aiken ta ta saya masa wani abu, bayan dawowarta ya kamata da karfi ya yi mata fyade.
Sai dai, ya musanta aikata laifin bayan kama shi da aka yi.
Shi kuma Auwalu Yunusa da ya fito daga garin Kafin Fulani, an zarge shi da yi wa wata yarinya mai shekara shida fyade bayan da ya yi mata barazanar cewa zai kashe ta muddin ta fada wa wani.
Kwanaki bayan faruwar lamarin, yarinyar ta kasa tafiya, inda nan ne ta kira sunan Yunusa a matsayin wanda ya yi mata fyade.

Mutum na hudu da aka yanke wa hukunci, Mu’azu Abdulrahman daga Sabuwar Gwaram, an same shi da laifin tare wata yarinya mai shekara takwas lokacin da take komawa gida daga makaranta, inda ya kai ta zuwa wata gona sannan ya yi mata fyade.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Sai dai, bayan gabatar da shi a gaban kotu, ya musanta aikata laifin, inda a nasa bangaren, lauya mai yanke hukunci, ya kira shaidu uku domin gabatar da su suka bayar da shaida.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Jakadan Sin: Ya Kamata A Martaba Zabin Kasashen Duniya Game Da Kare Hakkin Bil Adama

Next Post

‘Yansanda Sun Cafke Dan Takarar Sanata Na PDP Kan Amfani Da Takardun Bogi A Bayelsa

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

7 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

8 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

9 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

13 hours ago
Fyade
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

14 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

15 hours ago
Next Post
‘Yansanda Sun Cafke Dan Takarar Sanata Na PDP Kan Amfani Da Takardun Bogi A Bayelsa

'Yansanda Sun Cafke Dan Takarar Sanata Na PDP Kan Amfani Da Takardun Bogi A Bayelsa

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.