• English
  • Business News
Friday, May 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Yi Watsi Da Bukatar APC Na Dakatar Da Zaɓen Kananan Hukumomi A Kano

by Sadiq
8 months ago
in Labarai
0
Kotu Ta Yi Watsi Da Bukatar APC Na Dakatar Da Zaɓen Kananan Hukumomi A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babbar Kotun Tarayya da ke Jihar Kano ta yi watsi da bukatar jam’iyyar APC, na hana Hukumar Zaɓen Mai Zaman Kanta ta Jihar Kano (KANSIEC), na gudanar da zaben kananan hukumomi a jihar.

APC tare da Hon. Aminu Aliyu Tiga ne suka shigar da korafi a gaban kotun, suna neman umarni don hana KANSIEC ci gaba da shirye-shiryen zaben.

  • An Kwantar Da Tsohon Shugaban Sudan Omar al-Bashir A Asibiti
  • Majalisa Ta Tabbatar Da Nadin Kudirat A Matsayin Alkalin Alkalan Nijeriya

Haka kuma, sun nemi kotu ta tabbatar da matsayin da kowa ke ciki har sai an saurari shari’ar.

Amma, a hukuncin da mai shari’a Simon Amobeda ya yanke, kotun ta ki karbar bukatarsu, inda ta umarci a sanar da wadanda ake kara don su bayyana dalilin da ya sa bai kamata a yi zaben ba.

Wadanda ake kara sun hada da KANSIEC, shugabanta Farfesa Sani Lawal Malumfashi, Majalisar Dokokin Jihar Kano, Babban Lauyan Jihar, ‘yansanda, Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), Hukumar Tsaro ta DSS, Hukumar Tsaro ta (NSCDC), da wasu.

Labarai Masu Nasaba

Duk Da Janye Tallafin Rarar Mai, Matsin Rayuwa Na Addabar ‘Yan Nijeriya

Shekara Biyun Mulki Tinubu: Nasarori Da Matsaloli Da Inda Aka Dosa

Mai shari’a Amobeda ya yi watsi da bukatun APC, tare da bayar da umarnin a gaggauta sauraren shari’ar.

Za a ci gaba da sauraron shari’ar a ranar 4 ga watan Oktoba, 2024.

Haka kuma, alkalin ya gargadi dukkanin bangarorin da su guji yin wani abu da zai iya shafar sakamakon shari’ar.

Tun da farko, KANSIEC ta samu umarnin kotu da ya hana APC da sauran jam’iyyu 18 tsoma baki a harkar zaben, wanda aka tsara zai gudanaa a ranar 26 ga watan Oktoba, 2024.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCkanoKotuShari'aWatsi Da KaraZaben Kananan Hukumomi
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kwantar Da Tsohon Shugaban Sudan Omar al-Bashir A Asibiti

Next Post

Sin Ta Kira Taron Nazarin Yanayi Da Aikin Raya Tattalin Arzikin Kasar 

Related

Duk Da Janye Tallafin Rarar Mai, Matsin Rayuwa Na Addabar ‘Yan Nijeriya
Manyan Labarai

Duk Da Janye Tallafin Rarar Mai, Matsin Rayuwa Na Addabar ‘Yan Nijeriya

23 minutes ago
Shekara Biyun Mulki Tinubu: Nasarori Da Matsaloli Da Inda Aka Dosa
Manyan Labarai

Shekara Biyun Mulki Tinubu: Nasarori Da Matsaloli Da Inda Aka Dosa

1 hour ago
Yadda Rikici Ya Yi Sanadin Kashe DPO A Kano
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 41 Da Ake Zargi Da Kisan DPO A Kano

14 hours ago
Ana Fargabar Mutane Da Dama Sun Rasu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Neja
Labarai

Ana Fargabar Mutane Da Dama Sun Rasu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Neja

15 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake A Nasarawa
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake A Nasarawa

16 hours ago
Atiku Ya Caccaki Gwamnatin Tinubu, Ya Yi Gargaɗi Kan Cin Sabon Bashi
Manyan Labarai

Atiku Ya Caccaki Gwamnatin Tinubu, Ya Yi Gargaɗi Kan Cin Sabon Bashi

19 hours ago
Next Post
Sin Ta Kira Taron Nazarin Yanayi Da Aikin Raya Tattalin Arzikin Kasar 

Sin Ta Kira Taron Nazarin Yanayi Da Aikin Raya Tattalin Arzikin Kasar 

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Janye Tallafin Rarar Mai, Matsin Rayuwa Na Addabar ‘Yan Nijeriya

Duk Da Janye Tallafin Rarar Mai, Matsin Rayuwa Na Addabar ‘Yan Nijeriya

May 30, 2025
Shekara Biyun Mulki Tinubu: Nasarori Da Matsaloli Da Inda Aka Dosa

Shekara Biyun Mulki Tinubu: Nasarori Da Matsaloli Da Inda Aka Dosa

May 30, 2025
Cutar Hawan Jini Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuke

Cutar Hawan Jini Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuke

May 30, 2025
Gasar Wasanni Ta Kasa Wata Hanya Ce Ta Hada Kan Matasan Nijeriya– Obasanjo

Gasar Wasanni Ta Kasa Wata Hanya Ce Ta Hada Kan Matasan Nijeriya– Obasanjo

May 29, 2025
An Gudanar Da Dandalin Kawancen Birane Na Kasa Da Kasa Na Shanghai 

An Gudanar Da Dandalin Kawancen Birane Na Kasa Da Kasa Na Shanghai 

May 29, 2025
Darajar Sashen Masana’antun AI Na Sin Ta Kai Kusan Yuan Biliyan 600

Darajar Sashen Masana’antun AI Na Sin Ta Kai Kusan Yuan Biliyan 600

May 29, 2025
Yadda Rikici Ya Yi Sanadin Kashe DPO A Kano

‘Yansanda Sun Kama Mutane 41 Da Ake Zargi Da Kisan DPO A Kano

May 29, 2025
Sanarwar Bayan Taron Kolin Sin Da ASEAN Da GCC Ta Yi Nuni Ga Burin Kara Dunkulewa Waje Guda

Sanarwar Bayan Taron Kolin Sin Da ASEAN Da GCC Ta Yi Nuni Ga Burin Kara Dunkulewa Waje Guda

May 29, 2025
Sin Ta Cimma Nasasar Harbar Na’urar Nazarin Tauraro a Sararin Sama Mai Lakabin “Tianwen-2”

Sin Ta Cimma Nasasar Harbar Na’urar Nazarin Tauraro a Sararin Sama Mai Lakabin “Tianwen-2”

May 29, 2025
Ana Fargabar Mutane Da Dama Sun Rasu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Neja

Ana Fargabar Mutane Da Dama Sun Rasu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Neja

May 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.