• English
  • Business News
Friday, May 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotun Birtaniya Ta Daure Wasu ‘Yan Nijeriya 4

by Rabi'u Ali Indabawa
6 months ago
in Kasashen Ketare
0
Kotun Birtaniya Ta Daure Wasu ‘Yan Nijeriya 4
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An yanke wa wasu dalibai 4 ‘yan Nijeriya hukuncin dauri a kasar Birtaniya bisa samun su da hannu a wani rikici da ya hada da wukake na wasan baseball a Leicester.

Lamarin, wanda ya faru a kan titin New Park a farkon sa’o’i na Nuwamba 4, 2021, ya bar wanda aka azabtar da raunuka da yawa.

  • Yunƙurin Kafa Ƙasar Yarbawa: Igboho Ya Miƙa Koke Ga Firaministan Birtaniya
  • Yunƙurin Kafa Ƙasar Yarbawa: Igboho Ya Miƙa Koke Ga Firaministan Birtaniya

Bayan cikakken bincike da ‘yan sandan birnin Leicester suka yi, hukumomi sun gano masu laifin ta hanyar faifan na’urar CCTB, bin diddigin waya, da taimakon jama’a.

A watan Oktoba ne aka kammala shari’ar na tsawon makonni shida, kuma an yanke hukuncin ne a ranar 14 ga watan Nuwamba. Wani rahoto da aka buga a shafin intanet na ‘yan sanda ya yi cikakken bayani kan sakamakon. Destiny Ojo mai shekara 21, na Plumstead, London an yanke masa hukumcin shekaru bakwai saboda tashin hankali, kokari na cutar da jama’a da ganganci.

Habib Lawal mai shekaru 21, na Bedley, London an yanke masa hukumcin shekaru biyar saboda haifar da tashin hankali. Ridwanulahi Raheem mai shekaru 21, na Lambeth, Landan an yanke masa hukumcin shekaru uku saboda kokarin haifar da tashin hankali da kuma mallakar wata wuka.

Labarai Masu Nasaba

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

An yanke wa Joshua Dabies-Ero mai shekaru 21, dan garin Bedley, Landan hukuncin daurin shekaru biyu saboda haifar da tashin hankali. Wanda ake tuhuma na biyar, Justin Asamoah  mai shekaru 22, na Merton, ya amsa laifinsa na mallakar wata wuka kuma an shirya yanke masa hukunci ranar 22 ga watan Nuwamba.

Mai magana da yawun ‘yan sandan Leicester ya yaba wa jama’a bisa taimakon da suka bayar yayin gudanar da bincike tare da jaddada bukatar magance tashe-tashen hankula don tabbatar da tsaron al’umma.

Dan sanda mai binciken Sean Downey, da yake tsokaci kan lamarin, ya ce, “Wannan lamarin ya nuna babban hadarin tashin hankali. An yi sa’a cewa raunukan da aka samu ba su yi muni ko kisa ba. Wannan zai iya zama bincike daban-daban.”

Ya kara da cewa, “Muna godiya ga duk wanda ya goyi bayan binciken. A matsayinmu na karfi, fifikonmu shi ne kare lafiyar jama’a. Ba za a amince da ta’addanci a cikin al’ummominmu ba, kuma za mu ci gaba da daukar kwararan matakai kan masu laifi.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Birtaniya
ShareTweetSendShare
Previous Post

CBN Ya Bayyana Shirin Kakaba Wa Bankuna Takunkumi

Next Post

An Kori Tsohon Manajan Banki Bisa Zargin Damfarar Naira Miliyan 122

Related

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha
Kasashen Ketare

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

2 days ago
China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci
Kasashen Ketare

China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

3 days ago
Isra’ila Ta Yi Barazanar Kai Hare-Hare Kan Iran Kamar Hamas Da Hezbollah
Kasashen Ketare

Isra’ila Ta Yi Barazanar Kai Hare-Hare Kan Iran Kamar Hamas Da Hezbollah

1 week ago
Nijar Ta Soke Yarjejeniyar Tattara Bayanai Da Rasha Da Turkiyya, Ta Fara Neman Sabbin Abokan Hulɗa
Kasashen Ketare

Nijar Ta Soke Yarjejeniyar Tattara Bayanai Da Rasha Da Turkiyya, Ta Fara Neman Sabbin Abokan Hulɗa

1 week ago
Saudiyya Ta Tanadi Hukunci Mai Tsanani Ga Masu Yin Aikin Hajji Babu Takardun Izini
Kasashen Ketare

Saudiyya Ta Tanadi Hukunci Mai Tsanani Ga Masu Yin Aikin Hajji Babu Takardun Izini

1 week ago
Mataimakin Shugaban Ƙasa Zai Wakilci Nijeriya A Rantsar Da Shugaban Gabon
Kasashen Ketare

Mataimakin Shugaban Ƙasa Zai Wakilci Nijeriya A Rantsar Da Shugaban Gabon

2 weeks ago
Next Post
An Kori Tsohon Manajan Banki Bisa Zargin Damfarar Naira Miliyan 122

An Kori Tsohon Manajan Banki Bisa Zargin Damfarar Naira Miliyan 122

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Na Bukatar Dala Biliyan 10 Kowace Shekara Domin Samun Ingantacciyar Wutar Lantarki — Minista

Nijeriya Na Bukatar Dala Biliyan 10 Kowace Shekara Domin Samun Ingantacciyar Wutar Lantarki — Minista

May 16, 2025
Masu Garkuwa Sun Nemi Miliyan ₦30 Don Sako Shugaban APC A Ondo

Masu Garkuwa Sun Nemi Miliyan ₦30 Don Sako Shugaban APC A Ondo

May 16, 2025
Dalilin Tsame Daya Cikin Uku Na Ma’aikatan Ƙasar Nan A Tsarin Sauye-sauyen Biyan Haraji – Czar

Dalilin Tsame Daya Cikin Uku Na Ma’aikatan Ƙasar Nan A Tsarin Sauye-sauyen Biyan Haraji – Czar

May 16, 2025
Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci

Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci

May 16, 2025
Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

May 16, 2025
Abin  Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (1)

Abin  Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (1)

May 16, 2025
Rashin Tsaro Da Raba Wa Manoma Kayan Aiki Kan Lokaci Na Baraza Ga Wadata Kasa Da Abinci

Rashin Tsaro Da Raba Wa Manoma Kayan Aiki Kan Lokaci Na Baraza Ga Wadata Kasa Da Abinci

May 16, 2025
Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

May 15, 2025
Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

May 15, 2025
Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.