• English
  • Business News
Saturday, August 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotun Birtaniya Ta Daure Wasu ‘Yan Nijeriya 4

by Rabi'u Ali Indabawa
8 months ago
in Kasashen Ketare
0
Kotun Birtaniya Ta Daure Wasu ‘Yan Nijeriya 4
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An yanke wa wasu dalibai 4 ‘yan Nijeriya hukuncin dauri a kasar Birtaniya bisa samun su da hannu a wani rikici da ya hada da wukake na wasan baseball a Leicester.

Lamarin, wanda ya faru a kan titin New Park a farkon sa’o’i na Nuwamba 4, 2021, ya bar wanda aka azabtar da raunuka da yawa.

  • Yunƙurin Kafa Ƙasar Yarbawa: Igboho Ya Miƙa Koke Ga Firaministan Birtaniya
  • Yunƙurin Kafa Ƙasar Yarbawa: Igboho Ya Miƙa Koke Ga Firaministan Birtaniya

Bayan cikakken bincike da ‘yan sandan birnin Leicester suka yi, hukumomi sun gano masu laifin ta hanyar faifan na’urar CCTB, bin diddigin waya, da taimakon jama’a.

A watan Oktoba ne aka kammala shari’ar na tsawon makonni shida, kuma an yanke hukuncin ne a ranar 14 ga watan Nuwamba. Wani rahoto da aka buga a shafin intanet na ‘yan sanda ya yi cikakken bayani kan sakamakon. Destiny Ojo mai shekara 21, na Plumstead, London an yanke masa hukumcin shekaru bakwai saboda tashin hankali, kokari na cutar da jama’a da ganganci.

Habib Lawal mai shekaru 21, na Bedley, London an yanke masa hukumcin shekaru biyar saboda haifar da tashin hankali. Ridwanulahi Raheem mai shekaru 21, na Lambeth, Landan an yanke masa hukumcin shekaru uku saboda kokarin haifar da tashin hankali da kuma mallakar wata wuka.

Labarai Masu Nasaba

Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza

Iran Ta Zargi Birtaniya, Faransa, Da Jamus Da Gazawa Kan Yarjejeniyar Nukiliyar 2015

An yanke wa Joshua Dabies-Ero mai shekaru 21, dan garin Bedley, Landan hukuncin daurin shekaru biyu saboda haifar da tashin hankali. Wanda ake tuhuma na biyar, Justin Asamoah  mai shekaru 22, na Merton, ya amsa laifinsa na mallakar wata wuka kuma an shirya yanke masa hukunci ranar 22 ga watan Nuwamba.

Mai magana da yawun ‘yan sandan Leicester ya yaba wa jama’a bisa taimakon da suka bayar yayin gudanar da bincike tare da jaddada bukatar magance tashe-tashen hankula don tabbatar da tsaron al’umma.

Dan sanda mai binciken Sean Downey, da yake tsokaci kan lamarin, ya ce, “Wannan lamarin ya nuna babban hadarin tashin hankali. An yi sa’a cewa raunukan da aka samu ba su yi muni ko kisa ba. Wannan zai iya zama bincike daban-daban.”

Ya kara da cewa, “Muna godiya ga duk wanda ya goyi bayan binciken. A matsayinmu na karfi, fifikonmu shi ne kare lafiyar jama’a. Ba za a amince da ta’addanci a cikin al’ummominmu ba, kuma za mu ci gaba da daukar kwararan matakai kan masu laifi.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Birtaniya
ShareTweetSendShare
Previous Post

CBN Ya Bayyana Shirin Kakaba Wa Bankuna Takunkumi

Next Post

An Kori Tsohon Manajan Banki Bisa Zargin Damfarar Naira Miliyan 122

Related

Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza
Kasashen Ketare

Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza

2 days ago
Iran Ta Zargi Birtaniya, Faransa, Da Jamus Da Gazawa Kan Yarjejeniyar Nukiliyar 2015
Kasashen Ketare

Iran Ta Zargi Birtaniya, Faransa, Da Jamus Da Gazawa Kan Yarjejeniyar Nukiliyar 2015

2 weeks ago
Bayan Shekaru 20 Yana Bacci, Yariman Saudiyya Ya Rasu
Kasashen Ketare

Bayan Shekaru 20 Yana Bacci, Yariman Saudiyya Ya Rasu

2 weeks ago
Trump Ya Bai Wa Rasha Kwanaki 50 Ta Kawo Ƙarshen Yaƙinta Da Ukraine
Kasashen Ketare

Trump Ya Bai Wa Rasha Kwanaki 50 Ta Kawo Ƙarshen Yaƙinta Da Ukraine

3 weeks ago
Sarkin Maroko Ya Aike Da Ta’aziyya Ga Nijeriya Bisa Rasuwar Buhari
Kasashen Ketare

Sarkin Maroko Ya Aike Da Ta’aziyya Ga Nijeriya Bisa Rasuwar Buhari

3 weeks ago
Aikin Bututun Gas Na Nijeriya – Morocco Na Ƙara Samun Ci Gaba
Kasashen Ketare

Aikin Bututun Gas Na Nijeriya – Morocco Na Ƙara Samun Ci Gaba

3 weeks ago
Next Post
An Kori Tsohon Manajan Banki Bisa Zargin Damfarar Naira Miliyan 122

An Kori Tsohon Manajan Banki Bisa Zargin Damfarar Naira Miliyan 122

LABARAI MASU NASABA

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

August 1, 2025
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

August 1, 2025
2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

August 1, 2025
Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

August 1, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

August 1, 2025
Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

August 1, 2025
Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

August 1, 2025
Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

August 1, 2025
Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

August 1, 2025
An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

August 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.