• English
  • Business News
Sunday, November 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotun Daukaka Kara Ta Samu Korafe-korafen Zabubbukan 2023 Guda 1,209

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Kotun

Shugabar kotun daukaka kara, Mai Shari’a Monica Dongben-Mensem, ta bayyana cewa kotun ta zartar da jimillar hukunce-hukunce 7,295 da kuma ci gaba da sauraron kararraki 3,665 a kakar shari’a ta 2022/2023.

Da take jawabi yayin bikin fara sabuwar shekarar shari’a a Abuja, Mai Shari’a Dongben-Mensen, ta tunatare da cewa an samar da kwamitoci 98 domin sauraron koke-koken zabe a fadin kasar nan, saboda a gudanar da jimillar korafe-korafen zabe guda 1,209 da aka shigar a gabanta.

  • Cibiyar Kimiyyar Noma Na Sin CATAS Ta Cancanci Yabo
  • Babu Wata Yarjejeniya Tsakaninmu Da Gwamnatin Tarayya Kan Dakatar Da Yajin Aiki – NLC

Ta ce daga cikin korafe-korafen, biyar an shigar da su ne a kotun sauraron kararrakin zaben shugaban kasa kuma an kammala su, yayin da wasu 147 da aka shigar a kotun sauraron kararrakin zaben sanatan, sannan an gabatar da kararraki 417 na zaben majalisar wakilai.

Shugabar kotun daukaka kara ta ce, jimillar korafe-korafe 557 da ke da alaka da majalisar dokokin jihohi, da kuma zabukan gwamnoni 83 ne aka yi watsi da su. Ya ce jihohi 28 ne suka halarci zaben gwamnoni kuma an shigar da kara a jihohi 24.

A cewarta, a halin yanzu sashin Abuja na cike da tarin takardu, sannan kuma suna fama da rashin isassun wuraren ajiya da ofisoshi.

LABARAI MASU NASABA

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

Shugabar ta yi kira ga ministan Babban Birnin Tarayya Abuja da ya samar da wani katafaren fili don gina sashin kotun da ke Abuja.

A nasa jawabin, Ministan Shari’a, Prince Lateef Fagbemi ya ce gwamnatin Shugaba Bola Tinubu za ta magance matsalar karancin alkalai a kotun daukaka kara da kuma kotun koli.

Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike ya hori bangaren shari’a da su ci gaba da rike amanar jama’a saboda ‘yan Nijeriya na da kwarin gwiwa kan hukuncin kotuna.

Wike ya yi wannan kiran ne a taron shekara shari’a ta 2023/2024 na kotun daukaka kara, wanda aka gudanar a shalkwatan babban kotun daukaka da ke Abuja.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya
Tambarin Dimokuradiyya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
Next Post
Gwamna yusuf

Gwamnan Kano Ya Sake Nada Sabbin Hadimai 116

LABARAI MASU NASABA

Triumph

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025
CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.