ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cibiyar Kimiyyar Noma Na Sin CATAS Ta Cancanci Yabo

by CGTN Hausa
3 years ago
CATAS

Kasar Congo Brazzaville wadda ke yankin tsakiyar Afirka, na da albarkatun noma baya ga danyen mai, kuma ’yan kasar na alfahari, da cin gajiya daga sana’ar noma, to amma aikin noma a wannan zamani na bukatar kwarewa, sanin makamar aiki, da amfani da fasahohin zamani domin samun cikakkiyar gajiya.

Bisa hakan ne ma cibiyar kimiya ta bunkasa noma a yankuna masu zafi ta kasar Sin ko CATAS, ta kuduri aniyar horas da manoma da jami’ai a Congo, dabarun amfani da na’urorin zamani na inganta wannan sana’a. A baya bayan nan, jami’an wannan cibiya ta CATAS sun gudanar da irin wannan horo a birnin Haikou, fadar mulkin lardin Hainan na kasar Sin. Kazalika wasu jami’an cibiyar ta CATAS sun gabatarwa daliban Congo dabarun kimiyya na bunkasa noma a wasu gonakin dake kusa da birnin Brazzaville, fadar mulkin kasar ta Congo.

  • Kasar Sin Mai Burin Ganin Ci Gaban Kowa
  • Sin Ta Harba Sabon Tauraron Dan Adam Na Hangen Nesa

A cikin shekaru biyar, kwararru daga CATAS dake aiki a Brazzaville, suka gudanar da horaswa har sau 29, inda suka gabatarwa manoman kasar, da jami’an sashen noma dabaru daban daban na wanzar da ci gaban sana’ar noma a kasar.

ADVERTISEMENT

Ko shakka babu, kwararru a wannan muhimmin fanni na noma daga kasar Sin, sun shuka wata muhimmiyar alaka ta inganta noma, musamman a yankunan wannan kasa mai dumi dake tsakiyar Afirka, wanda hakan ya sanya dan ba ga inganta hadin gwiwar Sin da nahiyar Afirka.

Karkashin kwazon wadannan kwararru na cibiyar CATAS, an tura sama da rukunin masana 20 zuwa Congo, domin su gudanar da tallafin horaswa na inganta fasahar noma, suna kuma ci gaba da aiki a cibiyar gwaji ta “ATDC” tun daga shekarar 2007 kawo yanzu.

LABARAI MASU NASABA

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

Ana iya ganin tasirin wannan muhimmin aiki a Congo, inda manoman wurin ke gwada sabbin iri na yanayin zafi, da noman kaji, da sauran sassan bunkasa noma.

Tabbas, a sana’ar noma, samun kwarewa, ta amfani da kimiyya da fasahohin zamani, jigo ne na cimma nasarar da ake fata. A wannan gaba da Congo Brazzaville ke more fasahohin kwararru daga kasar Sin, muna iya cewa hakan abun a yaba ne, kuma yana kara nuna aniyar kasar Sin ta yada fasahohinta na ci gaba, ga sauran kasashe masu tasowa dake nahiyar Afirka.

CATAS
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

MASU ALAKA

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal
Daga Birnin Sin

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

July 24, 2026
Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba
Daga Birnin Sin

Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

July 24, 2026
An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI
Daga Birnin Sin

An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

July 24, 2026
Next Post
Adadin Jarin Da Kasar Sin Ta Zuba A Kasashen Waje A Shekarar 2022 Na Kan Gaba A Duniya

Adadin Jarin Da Kasar Sin Ta Zuba A Kasashen Waje A Shekarar 2022 Na Kan Gaba A Duniya

LABARAI MASU NASABA

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

July 24, 2026
Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

July 24, 2026
Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

July 24, 2026
An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

July 24, 2026
NNPP Za Ta Kwace Mulki A Jihar Imo – Kwankwaso

Jam’iyyar NDC Ta Shirya Tsaf Domin Kafa Gwamnati A 2027 —Kwankwaso

July 24, 2026
Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

July 24, 2026
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

July 24, 2026
Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

July 24, 2026
Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

July 24, 2026
Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

July 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.