• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotun Koli Ta Sanya Ranar 3 Ga Maris Don Yanke Hukunci Kan Tsarin Canjin Kudi

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Kotun Koli

Kotun Koli ta dage karar da wasu gwamnonin jihohi suka shigar kan kalubalantar Gwamnatin Tarayya na aiwatar da sabon tsarin canjin takardun kudi.

Kotun Kolin ta dage Shari’ar zuwa ranar 3 ga watan Maris din 2023.

  • Mahara Sun Tarwatsa Gidan Rediyon Dan Majalisar Da Ke Goyon Bayan Atiku A Ribas
  • Dan Majalisa Ya Sauya Sheka Daga APC Zuwa PDP A Jigawa

Idan za a iya tunawa dai babban bankin Nijeriya (CBN) ya tsawaita wa’adin aiwatar da tsarin canjin takardun kudade na 200, 500 da naira 1,000 daga 31 ga watan Janairun zuwa 10 ga watan Fabrairun 2023 biyo bayan korafe-korafen da wasu ‘yan Nijeriya suka yi ta yi.

Amma Kolin bayan karar da wasu Gwamnoni suka shigar da Gwamnatin tarayya da gwamnan CBN tare da bankunan kasuwanci, kotun ta umarci dukkanin bangarorin da su dakatar daga aiwatar da shirin har zuwa lokacin da za a saurari batun a ranar 22 ga watan Fabrairun.

Kodayake, daga baya shugaban kasa Muhammadu Buhari a yayin jawabin da ya yi wa al’ummar Nijeriya a ranar Alhamis, ya umarci babban bankin Nijeriya CBN da ya sake fitar da tsoffin takardun kudade na naira 200 zallla na tsawon kwanaki 60 don ya sake shiga cikin al’umma tare da sabon takardar kudi na 200 da 500 da 1000.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

Sannan Buhari ya ce tsoffin takardun kudade na 500 da 1000 sun tashi a aiki a kasar nan.

Sai dai bayan matakin na shugaban kasa wasu sun dukufa wajen sukar matakin musamman Gwamnonin jam’iyyar APC.

Wasu da suka fito balo-balo suka kalubanci shirin na canjin Kudi sun hada da gwamnoni, Nasir El-Rufai (Kaduna), Abubakar Badaru (Jigawa), Rotimi Akeredolu (Ondo), Umar Ganduje gwamna a jihar (Kano); Kakakin Majalisar Dokokin tarayya, Femi Gbajabiamila; karamin ministan kwadago, Festus Keyamo; da wasu jiga-jigai a jam’iyyar APC.

Manyan Lauyoyin Najeriya kamar Femi Falana da Mike Ozekhome ma sun caccaki matakin shugaban kasar, su na masu cewa bai kamata matakin na Buhari ya iya soke na kotun kolin kasar ba.

Kazalika, wasu karin Gwamnonin Kaduna da Zamfara da Kogi sun sake shigar da wata karar domin kalubalantar Abubakar Malami, ministan shari’a da gwamnan babban bankin Nijeriya, Godwin Emefiele bisa kin mutunta umarnin kotun koli kan tsoffin takardun kudade.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86
Da ɗumi-ɗuminsa

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

November 5, 2025
ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta
Da ɗumi-ɗuminsa

ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

October 22, 2025
Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas
Da ɗumi-ɗuminsa

Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas

October 22, 2025
Next Post
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Jam'iyyu Sun Tura Wa INEC Sunayen Masu Sa Ido 1,575,301 A Rumfunan Zabe 176,588

LABARAI MASU NASABA

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

November 5, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

Majalisar Dattawa Ta Amince da Naira Tiriliyan 1.1 Don Biyan Bashin ‘Yan Kwangila – Akpabio

November 5, 2025
An Nemi Kasashen ECOWAS Su Samar Da Kariya Ga Yankunan Hakar Ma’adanai

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

November 5, 2025
Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Sanata Barau Ya Tsaya Takarar Shugaban Majalisar Dattawa

Ba Na Jin Tsoron Trump – Martanin Sanata Barau Ga Akpabio

November 5, 2025
CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

November 5, 2025
Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.