ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotun Koli Ta Sanya Ranar 3 Ga Maris Don Yanke Hukunci Kan Tsarin Canjin Kudi

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Kotun Koli

Kotun Koli ta dage karar da wasu gwamnonin jihohi suka shigar kan kalubalantar Gwamnatin Tarayya na aiwatar da sabon tsarin canjin takardun kudi.

Kotun Kolin ta dage Shari’ar zuwa ranar 3 ga watan Maris din 2023.

  • Mahara Sun Tarwatsa Gidan Rediyon Dan Majalisar Da Ke Goyon Bayan Atiku A Ribas
  • Dan Majalisa Ya Sauya Sheka Daga APC Zuwa PDP A Jigawa

Idan za a iya tunawa dai babban bankin Nijeriya (CBN) ya tsawaita wa’adin aiwatar da tsarin canjin takardun kudade na 200, 500 da naira 1,000 daga 31 ga watan Janairun zuwa 10 ga watan Fabrairun 2023 biyo bayan korafe-korafen da wasu ‘yan Nijeriya suka yi ta yi.

ADVERTISEMENT

Amma Kolin bayan karar da wasu Gwamnoni suka shigar da Gwamnatin tarayya da gwamnan CBN tare da bankunan kasuwanci, kotun ta umarci dukkanin bangarorin da su dakatar daga aiwatar da shirin har zuwa lokacin da za a saurari batun a ranar 22 ga watan Fabrairun.

Kodayake, daga baya shugaban kasa Muhammadu Buhari a yayin jawabin da ya yi wa al’ummar Nijeriya a ranar Alhamis, ya umarci babban bankin Nijeriya CBN da ya sake fitar da tsoffin takardun kudade na naira 200 zallla na tsawon kwanaki 60 don ya sake shiga cikin al’umma tare da sabon takardar kudi na 200 da 500 da 1000.

LABARAI MASU NASABA

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

Sannan Buhari ya ce tsoffin takardun kudade na 500 da 1000 sun tashi a aiki a kasar nan.

Sai dai bayan matakin na shugaban kasa wasu sun dukufa wajen sukar matakin musamman Gwamnonin jam’iyyar APC.

Wasu da suka fito balo-balo suka kalubanci shirin na canjin Kudi sun hada da gwamnoni, Nasir El-Rufai (Kaduna), Abubakar Badaru (Jigawa), Rotimi Akeredolu (Ondo), Umar Ganduje gwamna a jihar (Kano); Kakakin Majalisar Dokokin tarayya, Femi Gbajabiamila; karamin ministan kwadago, Festus Keyamo; da wasu jiga-jigai a jam’iyyar APC.

Manyan Lauyoyin Najeriya kamar Femi Falana da Mike Ozekhome ma sun caccaki matakin shugaban kasar, su na masu cewa bai kamata matakin na Buhari ya iya soke na kotun kolin kasar ba.

Kazalika, wasu karin Gwamnonin Kaduna da Zamfara da Kogi sun sake shigar da wata karar domin kalubalantar Abubakar Malami, ministan shari’a da gwamnan babban bankin Nijeriya, Godwin Emefiele bisa kin mutunta umarnin kotun koli kan tsoffin takardun kudade.

Kotun Koli
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu

MASU ALAKA

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa
Da ɗumi-ɗuminsa

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

July 10, 2026
An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa
Manyan Labarai

An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

July 10, 2026
An Kama Tsohon Minista Uche Nnaji Kan Zargin Amfani Da Takardun Bogi
Da ɗumi-ɗuminsa

An Kama Tsohon Minista Uche Nnaji Kan Zargin Amfani Da Takardun Bogi

July 1, 2026
Next Post
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Jam'iyyu Sun Tura Wa INEC Sunayen Masu Sa Ido 1,575,301 A Rumfunan Zabe 176,588

LABARAI MASU NASABA

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

July 17, 2026
Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

July 17, 2026
Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

July 17, 2026
Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

July 17, 2026
Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

July 17, 2026
Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

July 17, 2026
Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

July 17, 2026
Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

July 17, 2026
Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

July 17, 2026
Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.