• English
  • Business News
Wednesday, October 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 hours ago
Mace

A jiya Litinin shugaban kasar Sin ya kaddamar da taron koli na mata na duniya a birnin Beijing, inda ya gabatar da jawabi tare da shawarwari 4 na kasar Sin kan inganta ci gaban harkokin mata a duniya. Jawabin na shugaba Xi ya ja hankalin mahalarta da ma jama’ar duniya inda suke ganin ya aza wani sabon tubalin hadin gwiwa tsakanin kasa da kasa a bangaren raya harkokin mata.

Wannan taro a ganina, ya zo a daidai lokacin da ake bukatarsa. Bayan shekaru 30 da cimma yarjejeniyar Beijing da ta zama jigo wajen raya harkokin mata, an samu sabbin sauye-sauye a duniya wadanda ke bukatar sabbin dabaru. Kuma haduwar da aka yi a yanzu, zai kara ba mata a duniya kwarin gwiwa da bayyana musu cewa, suna da makoma mai haske. Baya ga haka, zuwan mahalartan kasar Sin zai nuna musu irin ci gaban da Sin ta samu a fannin domin su dauki darasi.

Kasar Sin ta bayar da gagarumar gudunmawa ga raya harkokin mata a duniya, inda take zurfafa musaya da hadin gwiwa a fannonin da suka shafi mata domin taimakawa mata a kasashe masu tasowa inganta rayuwarsu da cimma burikansu. Misali, ta horar da mata sama da 200,000 daga kasashe da yankuna sama da 180, baya ga shirye-shiryen horar da mata sama da 100 da ta aiwatar a kasashe masu tasowa.

Idan muka dawo cikin gida, za mu fahimci furucin shugaba Xi cewa, “kowacce mace tauraruwa ce a sabon tafarkin zamanantar da kasar Sin” domin kasar tana iyakar kokarinta wajen tabbatar da daidaiton jinsi cikin dukkan manufofinta na kasa da ba mata damar taka rawa daidai da maza. Sin na daya daga cikin kasashen duniya dake da adadin mai yawa na mata ma’aikata, inda suka dauki kaso 40 cikin 100. Mata Sinawa, suna ci gaba da taka rawar gani a dukkan bangarori na rayuwa. Ni ganau ce na yadda mata a yankunan karkara suka tashi tsaye wajen marawa gwamnati baya a yakin da ta yi da talauci da kuma ci gaba da ake yi na ganin hannun agogo bai koma baya ba. Wani babban batu shi ne, yadda ake aiwatarwa da gyara dokoki domin tabbatar da mata sun samu damarmaki iri daya da takwarorinsu maza, daga bangaren ilimi zuwa na mallakar kadarori da gidan aure da zamantakewa da sauransu. Haka zalika a bangaren siyasa, inda ake da mata masu jagorantar hukumomi da kwamitocin siyasa a kasar.

Shawarwarin shugaba Xi Jinping, abu ne da kasa da kasa za su iya aiwatarwa domin an yi a Sin kuma kwalliya ta biya kudin sabulu. Za mu iya cewa, wannan taro ya sake samar wa duniya karin kafa ta hadin gwiwa domin tattaunawa da hada karfi da karfe wajen gaggauta samar da ci gaba mai ma’ana a fagen kare hakkokin mata da goya musu baya wajen taka rawar gani a harkokin da suka shafi bunkasa tattalin arziki da zamantakewa da ma bayar da gudunmawa ga ci gaban duniya. (Fa’iza Mustapha)

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

October 14, 2025
Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani
Daga Birnin Sin

Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

October 14, 2025
Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 
Daga Birnin Sin

Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

October 14, 2025
Next Post
Kotu

Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

October 14, 2025
Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

October 14, 2025
Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

October 14, 2025
Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

October 14, 2025
Kotu

Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta

October 14, 2025
Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

October 14, 2025
Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya

Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya

October 14, 2025
Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo

Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo

October 14, 2025
Asuu

An Janye Wajibcin Samun Kiredit A Darasin Lissafi Ga Ɗaliban Fannin Zamantakewa Don Shiga Manyan Makarantu 

October 14, 2025
Al’ummun Kasashe Daban-Daban Sun Yabawa Shawarwarin Sin Dake Taimakawa Wajen Dunkulewa Don Hanzarta Ci Gaban Mata

Al’ummun Kasashe Daban-Daban Sun Yabawa Shawarwarin Sin Dake Taimakawa Wajen Dunkulewa Don Hanzarta Ci Gaban Mata

October 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.