Shahararren ɗan siyasar nan da ake jin muryarsa kan harkokin siyasa a kafafen yada labarai, kuma jigo a jam’iyyar APC a jihar Kano, Alhaji Abdulmajid Ɗanbilki Kwamanda, ya ce; ya yi dana-sanin tallan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a zaben shekara ta 2023.
A cikin wata tattaunawa da ya yi da jaridar Daily Trust ta wayar tarho, Kwamanda ya ce duba abin da ya ke faruwa a kasarnan kuma kowa ya ke gani, shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu l, ya gaza wajen cika alkawuran da ya yi wa ‘yan Nijeriya da suka fito suka zabe shi.
- Watanni 2 Da Sauke Baffa Bichi, An Nada Umar Farouk Mukamin Sakataren Gwamnatin Kano
- ‘Yan Nijeriya A Hannun Tinubu Cikin Shekara Guda
Ya ce; a rayuwarsa bai taɓa yin wani abu da ya sa shi yin dana-sani ba irin tallan shugaba Tinubu ba.
Kwamanda Ya ƙara da cewa, yana takaicin abin da yake faruwa a Nijeriya na gazawar gwamnati, amma dole ne sai ya fadi gaskiya duk da shi ɗan jam’iyyar APC ne.
A cewarsa, ƴan Nijeriya suna cikin yunwa, kuma sun fusata da halin da ake ciki, ga rashin tsaro sannan ba kowa ne ya ke iya cin abinci sau biyu ba a rana.
A karshe ya ce yana neman afuwa ga al’umma saboda tallata gwamnatin Tinubu da ya yi akan za ta yi abin kirki amma sai aka samu akasin haka.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp